Эфесянам 1 – NRT & HCB

New Russian Translation

Эфесянам 1:1-23

1От Павла, апостола Иисуса Христа, избранного по воле Бога.

Святым в Эфесе, живущим по вере в Иисуса Христа.

2Благодать и мир вам от Бога, нашего Отца, и от Господа Иисуса Христа.

Духовные благословения

3Благословен Бог и Отец нашего Господа Иисуса Христа. Он во Христе благословил нас всеми духовными благословениями небес. 4Ведь Он избрал нас в Нем еще до создания мира, чтобы нам быть святыми и непорочными перед Ним. Он, по Своей любви, 5по Своему доброму желанию и воле, предопределил нам через Иисуса Христа стать усыновленными Им детьми. 6В этом проявлена вся слава Его благодати, которую Он дал нам во Христе, возлюбленном Им. 7В Нем мы получили искупление Его кровью и прощение грехов по Его безграничной благодати, 8которой Он щедро наделил нас. Со всякой мудростью и знанием 9Он открыл нам тайну Своей воли. Он сделал это по Своему доброму желанию, изначально воплощенному во Христе, 10чтобы в определенное время объединить все на небесах и на земле под властью Христа.

11В Нем мы стали наследниками, как это и было предопределено замыслом Бога, совершающего все в мире согласно Своей воле и Своим целям, 12чтобы мы, первыми возложившие надежду на Христа, послужили к Его восхвалению.

13В Нем и вы, услышав слово истины – Радостную Весть, несущую вам спасение, – и поверив во Христа, были отмечены печатью обещанного Святого Духа, 14Который является залогом нашего будущего наследия и искупления тех, кто принадлежит Ему, для похвалы Его славы.

Молитва Павла

15Поэтому и я, услышав о вашей вере в Господа Иисуса и о вашей любви ко всем святым, 16не перестаю благодарить за вас Бога, вспоминая вас в своих молитвах. 17Я молюсь, чтобы Бог нашего Господа Иисуса Христа, прославленный Отец, дал вам Духа мудрости и откровения1:17 Или: «дал вам духовную мудрость и откровение»., чтобы вы лучше познали Его. 18Я молюсь и о том, чтобы Бог просветил очи вашего сердца, и вы увидели, что представляет собой та надежда, к которой Он вас призвал, сколь велико богатство славы, которую получат в наследство святые, 19и каково безмерное величие Его силы в нас, верующих под действием Его безграничной силы. 20Этой же силой Бог произвел действие и во Христе, когда воскресил Его из мертвых и посадил по правую руку1:20 См. Пс. 109:1. от Себя на небесах, 21выше всяких начальств, властей, сил и господств и выше всякого имени, упоминаемого не только в этом веке, но и в будущем. 22Бог все покорил под ноги Христа1:22 См. Пс. 8:7., поставил Его, Владыку всего, главой Церкви, 23которая является Его телом, полнотой Того, Кто наполняет все во всем.

Hausa Contemporary Bible

Afisawa 1:1-23

1Bulus, wanda Allah ya zaɓa don yă zama manzon Kiristi Yesu,

Zuwa ga tsarkaka da suke a Afisa,1.1 Waɗansu rubuce-rubucen hannu na dā ba su da a Afisa. da kuma suke amintattu1.1 Ko kuwa masu bi waɗanda cikin Kiristi Yesu.

2Alheri da salama daga Allah Ubanmu da Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.

Albarkun ruhaniya a cikin Kiristi

3Yabo ya tabbata ga Allah Uban Ubangijinmu Yesu Kiristi, wanda ya kawo mana kowace albarka ta ruhaniya daga sama. 4Gama ya zaɓe mu a cikin Kiristi tun dā can, kafin ma a halicci duniya don mu zama masu tsarki da kuma marasa aibi a gabansa. 5A cikin ƙauna, ya1.4,5 Ko kuwa gani cikin ƙauna. 5 Ya ƙaddara mu zama ’ya’yansa na riƙo ta wurin Kiristi Yesu, bisa ga nufinsa na alheri. 6Ya yi haka don mu yabi Allah saboda alherin da ya yi mana saboda mu na ƙaunataccen Ɗansa ne. 7A cikinsa muka sami fansa ta wurin jininsa, wato, yafewar zunubanmu. Kiristi ya yi wannan saboda yawan alherin Allah 8wanda ya ba mu babu iyaka tare da dukan hikima da fahimta. 9Allah ya yi abin da ya nufa, ya kuma sanar mana shirin asirin da ya riga ya shirya yă cika ta wurin Kiristi. 10Nufinsa ke nan, idan lokaci ya cika, yă harhaɗa dukan abubuwa a ƙarƙashin ikon Kiristi, wato, dukan abubuwan da suke sama da abubuwan da suke ƙasa.

11A cikinsa ne kuma aka zaɓe mu mu sami gādo daga Allah,1.11 Ko kuwa mun zama abin gādon Allah an kuwa ƙaddara mu ga haka bisa ga nufin wannan da yake zartar da dukan abubuwa yadda ya yi nufi yă yi. 12Manufar Allah ita ce cewa mu da muka fara sa bege a cikin Kiristi, mu yi zaman yabon ɗaukakar Allah. 13An kuma haɗa ku a cikin Kiristi lokacin da kuka ji saƙon nan na gaskiya, wanda yake labari mai daɗi na cetonku. Da kuka ba da gaskiya, sai aka yi muku alamar shaida a cikinsa da Ruhu Mai Tsarki. 14Ruhu Mai Tsarkin nan shi ne tabbacin da Allah ya yi na cewa zai ba mu kome da ya yi alkawari, har ya sa muka sani nan gaba Allah zai ceci waɗanda suke nasa. Wannan kuwa domin yabon ɗaukakarsa ne.

Godiya da addu’a

15Saboda haka, tun lokacin da na ji labarin bangaskiyarku cikin Ubangiji Yesu da kuma ƙaunar da kuke yi wa dukan mutanen Allah, 16ban fasa yin godiya saboda ku ba, ina tuna da ku cikin addu’o’ina. 17Ina ta roƙo cewa Allah na Ubangijinmu Yesu Kiristi, Uba Maɗaukaki, yă ba ku Ruhun hikima da na ganewa, domin ku san shi da kyau. 18Ina kuma addu’a cewa zuciyarku tă waye don ku gane ko mene ne sa zuciyan nan da ya kira ku a kansa, ku kuma san darajar dukiyan nan wadda take ta mutanen Allah, wato, albarkunsa. 19Ina addu’a ku san girman ikon Allah wanda ya wuce misali, wanda yake namu. Ikon da yake aiki a cikinmu, ɗaya ne da ikon nan 20da ya tā da Kiristi daga matattu, ya kuma sa ya zauna a hannun damansa a cikin mulkin samaniya. 21Yanzu yana mulki a kan dukan masu sarauta, da masu iko, da masu ƙarfi, da kuma masu mulki. Yana mulkin kome a wannan duniya, zai kuma yi mulkin duniya mai zuwa. 22Allah ya sa kome a ƙarƙashin ikonsa, ya kuma ba shi iko a kan kome don amfanin ikkilisiya. 23Kuma ikkilisiya ce jikinsa; ta kuma cika da Kiristi, wanda ya cika kome ta kowace hanya.