מעשי השליחים 6 – HHH & HCB

Habrit Hakhadasha/Haderekh

מעשי השליחים 6:1-15

1באותם הימים, כשמספר התלמידים הלך וגדל במהירות, החלו להישמע ביניהם תלונות ומריבות. היהודים שהגיעו מחו״ל ודיברו רק יוונית התלוננו שהאלמנות שלהם מופלות לרעה; בשעת חלוקת המזון היומית אין הן מקבלות אותה הכמות הניתנת לאלמנות מקרב המקומיים דוברי העברית. 2משום כך כנסו שנים־עשר השליחים את כל המאמינים לאסיפה כללית.

”עלינו להקדיש את זמננו לבישור דבר אלוהים, ולא לעסוק בבעיות חולין כמו חלוקת אוכל!“ אמרו השליחים. 3”אחים יקרים, הביטו סביבכם ובחרו שבעה אנשים נבונים, מלאים ברוח הקודש ובעלי שם טוב, והפקידו בידם את העניין הזה. 4וכך נוכל אנחנו להתרכז בתפילה, בהטפה ובהוראה.“

5ההצעה נתקבלה על־ידי כל חברי הקהילה, והם בחרו באנשים הבאים:

סטפנוס (שהיה מלא אמונה ורוח הקודש בצורה בולטת במיוחד), פיליפוס, פרוכורוס, ניקנור, טימון, פרמנס, ניקולס מאנטיוכיה (אשר היה גוי שהתגייר, ולאחר מכן האמין בישוע המשיח). 6שבעה אנשים אלה הוצגו בפני השליחים, וקיבלו את ברכתם בסמיכת ידיים ובתפילה.

7דבר האלוהים נשמע בחוגים הולכים וגדלים, ומספר התלמידים בירושלים גדל מאוד. גם כוהנים רבים האמינו בישוע המשיח.

8סטפנוס, שהיה כאמור מלא אמונה ורוח הקודש, חולל נסים ונפלאות בקרב העם. 9אולם יום אחד קמו מספר אנשים מקבוצת ”החופשיים“ והחלו להתווכח איתו. עד מהרה הצטרפו אליהם יהודים מקוריניה, מאלכסנדריה שבמצרים, מקיליקיה ומאסיה הקטנה, 10אך איש מהם לא יכול היה לגבור על החוכמה ועל הרוח שהיו בו.

11לכן הם שחדו כמה אנשים, כדי שיעידו נגד סטפנוס ויטענו ששמעו אותו מקלל את משה רבנו ואפילו את אלוהים.

12אשמת השקר הזאת עוררה את זעם ההמונים ואת כעסם של המנהיגים על סטפנוס. הם אסרו אותו והעמידוהו לדין לפני הסנהדרין. 13עדי השקר העידו נגד סטפנוס וטענו שאינו מפסיק לדבר נגד בית־המקדש ונגד התורה.

14”במו אוזנינו שמענו אותו אומר שאותו אדם, ישוע מנצרת, יהרוס את בית־המקדש וישנה את החוקים שמסר לנו משה!“ הצהירו עדי השקר. 15באותו רגע הביטו כל חברי הסנהדרין בסטפנוס וראו את פניו, ממש כפני מלאך אלוהים!

Hausa Contemporary Bible

Ayyukan Manzanni 6:1-15

Zaɓen mutane bakwai

1A waɗannan kwanaki, sa’ad da yawan almajirai suke ƙaruwa, sai Yahudawan masu jin Hellenanci a cikinsu suka yi gunaguni a kan Yahudawan da suke Ibraniyawa domin ba a kula da gwaurayensu a wajen raba abinci na yau da kullum. 2Saboda haka Sha Biyun nan suka tara dukan almajirai wuri ɗaya, suka ce, “Bai zai yi kyau mu bar hidimar maganar Allah don mu shiga hidimar abinci ba. 3’Yan’uwa, ku zaɓi mutum bakwai daga cikinku waɗanda aka sani suna cike da Ruhu da kuma hikima. Mu kuwa za mu danƙa musu wannan aiki 4mu kuwa mu mai da halinmu ga yin addu’a da kuma hidimar maganar Allah.”

5Wannan shawarar kuwa ta gamshi dukan ƙungiyar. Sai suka zaɓi Istifanus, mutumin da yake cike da bangaskiya da kuma Ruhu Mai Tsarki; da Filibus, Burokorus, Nikano, Timon, Farmenas, da Nikolas daga Antiyok, wanda ya tuba zuwa Yahudanci. 6Suka gabatar da waɗannan mutane wa manzanni, waɗanda kuwa suka yi addu’a, suka ɗibiya hannuwansu a kansu.

7Saboda haka maganar Allah ta yaɗu. Yawan almajirai a Urushalima kuwa ya yi saurin ƙaruwa, firistoci masu yawa kuma suka zama masu biyayya ga wannan bangaskiya.

An kama Istifanus

8To, Istifanus, mutum cike da alheri da ikon Allah, ya aikata manyan ayyukan da alamu masu banmamaki a cikin mutane. 9Sai hamayya ta taso daga ’yan ƙungiyar Majami’a na ’Yantattu (kamar yadda ake kiransu), Yahudawan Sairin da Alekzandariya da kuma lardunan Silisiya da Asiya. Mutanen nan suka fara muhawwara da Istifanus, 10amma ba su iya cin nasara kan hikimarsa ko kuma a kan Ruhu wanda ta wurinsa ne ya magana ba.

11Sa’an nan a asirce suka zuga waɗansu mutane su ce, “Mun ji Istifanus ya faɗa kalmomin saɓo game da Musa da kuma Allah.”

12Ta haka suka tā da hankalin mutane da dattawa da kuma malaman dokoki. Suka kama Istifanus suka kawo shi a gaban Majalisa. 13Suka kawo masu ba da shaidar ƙarya, waɗanda suka ba da shaida cewa, “Wannan mutum ba ya rabuwa da maganar banza a kan wurin nan mai tsarki da kuma doka. 14Gama mun ji shi yana cewa wannan Yesu Banazare zai rushe wurin nan ya kuma canja al’adun da Musa ya ba mu.”

15Dukan waɗanda suke zaune a Majalisar suka kafa wa Istifanus ido, suka kuma ga fuskarsa ta yi kama da ta mala’ika.