מעשי השליחים 5 – HHH & HCB

Habrit Hakhadasha/Haderekh

מעשי השליחים 5:1-42

1אולם היה ביניהם גם אדם אחר בשם חנניה. הוא ואשתו ‎שַׁפִּירָה החליטו למכור את חלקת אדמתם. 2בהסכמת אשתו החביא חנניה חלק מהכסף שקיבל תמורת האדמה, ואת יתרת הסכום הביא אל השליחים, בהצהירו שזה כל הסכום שקיבל תמורת האדמה.

3”חנניה,“ אמר לו פטרוס, ”מדוע הנחת לשטן להשתלט על לבך? כשטענת שזהו הסכום כולו, שיקרת לרוח הקודש! 4הרכוש היה שלך, והיית רשאי למכרו או להחזיק בו. גם לאחר שמכרת אותו היה מותר לך להחליט איזה חלק מהסכום לתת. כיצד יכולת לעשות דבר כזה? לא לנו שיקרת, כי אם לה׳!“

5ברגע ששמע חנניה מילים אלה, צנח ארצה ומת. כל הנוכחים נבהלו מאוד. 6באו בחורים אחדים וכיסו אותו בסדין, הוציאוהו החוצה וקברו אותו.

7כשלוש שעות לאחר מכן באה לשם אשתו של חנניה, בלי שידעה דבר על מה שקרה. 8”אמרי לי,“ פנה אליה פטרוס, ”האם מכרתם את אדמתכם במחיר כזה וכזה?“

”כן,“ ענתה שַׁפִּירָה, ”במחיר הזה מכרנו את האדמה.“

9”כיצד יכולתם, את ובעלך, אפילו להעלות על דעתכם לנסות את רוח ה׳?“ קרא פטרוס. ”מאחורי הדלת הזאת עומדים הבחורים שקברו זה עתה את בעלך, ובעוד רגע הם יישאו גם אותך החוצה!“

10באותו רגע נפלה גם שַׁפִּירָה על הרצפה ומתה. כשנכנסו הצעירים וראו שהיא מתה, נשאו אותה החוצה וקברו אותה לצד בעלה. 11אימה גדולה נפלה על כל הקהל ועל כל מי ששמע מה קרה.

12בינתיים המשיכו השליחים להתאסף בקביעות בבית־המקדש, באגף הנקרא ”אולם שלמה“, וחוללו נסים ונפלאות לעיני כל העם. 13המאמינים האחרים לא העזו להצטרף אל השליחים, אך כולם התייחסו אליהם ביראת כבוד. 14ומספר הגברים והנשים שהאמינו באדון ישוע הלך וגדל מיום ליום. 15החולים הוצאו לרחובות על מיטות ומזרונים, כדי שייפול עליהם צילו של פטרוס בשעה שיעבור שם. 16אנשים רבים מערי הסביבה נהרו לירושלים והביאו איתם חולים ואחוזי־שדים, וכולם נרפאו.

17הכהן הגדול וידידיו מבין הצדוקים הגיבו בזעם ובקנאה. 18הם תפסו את השליחים וכלאו אותם בבית־הסוהר העירוני.

19אולם באותו לילה בא מלאך ה׳, פתח את שערי הכלא, שלח אותם לחופשי ואמר להם: 20”שובו לבית־המקדש והמשיכו לבשר לעם את כל דברי החיים האלה!“

21השליחים הגיעו לפנות־בוקר לבית־המקדש, ומיד החלו ללמד את העם. מאוחר יותר הגיעו למקדש הכהן הגדול ופמלייתו, ולאחר שכינסו את כל חברי הסנהדרין, שלחו לקרוא לשליחים שבכלא כדי להעמידם לדין. 22אולם כשהגיעו אנשי המשמר לכלא, לא מצאו שם את השליחים! הם חזרו אל המועצה ודיווחו: 23”שערי בית־הסוהר היו נעולים, והשומרים עמדו על משמרתם; אך כשפתחנו את השערים לא מצאנו איש בפנים!“ 24ראשי הכוהנים ומפקד משמר־המקדש נבהלו מאוד ותהו כיצד ייגמר העניין. 25כעבור זמן קצר בא מישהו והודיע: ”האנשים שאסרתם עומדים בבית־המקדש ומלמדים את העם!“

26‏-27מפקד משמר המקדש וסגניו הלכו ועצרו את השליחים, (אולם לא השתמשו בכוח הזרוע, כי פחדו שאם יפגעו בשליחים לרעה יסקול אותם ההמון באבנים) והביאו אותם לפני הסנהדרין.

28”האם לא אמרנו לכם שלא לדבר יותר לעולם על הישוע הזה?“ דרש הכהן הגדול. ”במקום לשמוע לקולנו הפצתם את תורתכם בכל ירושלים, ומלבד זאת אתם עוד מנסים להטיל עלינו את האשמה במותו!“

29על כך ענו פטרוס והשליחים: ”עלינו לשמוע קודם כל לקול אלוהים, ורק לאחר מכן לקולם של בני־אדם! 30אלוהי אבותינו החזיר את ישוע לחיים, לאחר שהרגתם אותו בתלייה על הצלב. 31ואז, בגבורה גדולה, העלה אותו האלוהים למעלת שר ומושיע, כדי לתת לבני־ישראל הזדמנות לחזור בתשובה ולקבל סליחה על חטאיהם. 32אנחנו עדים לדברים אלה, וכן גם רוח הקודש שנתן ה׳ לכל מי ששומע בקולו.“

33דברים אלה הרגיזו כל־כך את חברי הסנהדרין, עד שהחליטו להוציא את השליחים להורג. 34אולם פרוש אחד מחברי הסנהדרין, גמליאל שמו, קם על רגליו ודרש להוציא את השליחים מן האולם עד שיסיים לומר את דבריו (הוא היה בקיא בתורה ונכבד מאוד בעיני העם).

35לאחר מכן פנה אל חברי הסנהדרין ואמר:

”אנשי ישראל, עליכם לשקול היטב ובכובד ראש מה שאתם עומדים לעשות לאנשים האלה. 36אל תשכחו שלפני זמן־מה קם אותו ברנש תודס, והעמיד פנים שהוא איש חשוב. כ־400 איש הצטרפו אליו, אולם לאחר שנהרג התפזרו תלמידיו לכל עבר.

37”לאחר תודס, בזמן מפקד התושבים, קם יהודה הגלילי. הוא משך אחריו תלמידים רבים, אך גם הוא מת וכל תלמידיו נעלמו.

38”משום כך אני מציע שתעזבו את האנשים האלה לנפשם. אם התורה הזאת שהם מלמדים בדויה מלבם – היא תישכח במהרה. 39אך אם היא מאלוהים – לא תוכלו לעצור את האנשים האלה; אתם עלולים למצוא את עצמכם נלחמים נגד אלוהים!“

40חברי הסנהדרין קיבלו את עצתו של רבן גמליאל. הם הכניסו את השליחים אל האולם, הלקו אותם בשוטים, ציוו עליהם שלא לדבר יותר לעולם בשם ישוע, ולבסוף שחררו אותם. 41השליחים יצאו מאולם בית הדין בלב שמח, משום שה׳ מצא אותם ראויים לסבול חרפה למען שם ישוע. 42ויום יום, בבית־המקדש ובבתים, המשיכו ללמד שישוע הוא המשיח.

Hausa Contemporary Bible

Ayyukan Manzanni 5:1-42

Ananiyas da Saffiratu

1To wani mutum mai suna Ananiyas tare da matarsa Saffiratu, shi ma ya sayar da wata mallakarsa. 2Da cikakken sanin matarsa ya ajiye sashi daga cikin kuɗin don kansa, ya kuma kawo sauran ya ajiye a sawun manzanni.

3Sai Bitrus ya ce, “Ananiyas, ta yaya Shaiɗan ya cika zuciyarka haka da ka yi wa Ruhu Mai Tsarki ƙarya ka kuma ajiye wa kanka sauran kuɗin da ka karɓa na filin? 4Ba naka ba ne kafin ka sayar da shi? Bayan da ka sayar da shi kuma, kuɗin ba naka ba ne? Me ya sa ka yi tunanin yin irin wannan abu? Ba mutum ne ka yi wa ƙarya ba, Allah ne ka yi masa.”

5Da Ananiyas ya ji wannan, sai ya fāɗi ya mutu. Sai babban tsoro kuwa ya kama duk waɗanda suka ji abin da ya faru. 6Sai samari suka zo gaba, suka naɗe gawarsa, suka fitar da shi suka je suka binne.

7Bayan kusan awa uku, sai matarsa ta shigo, ba da sanin abin da ya faru ba. 8Bitrus ya tambaye ta ya ce, “Gaya mini, kuɗin da yake da Ananiyas kuka sayar da filin ke nan?”

Ta ce, “I, haka ne muka sayar.”

9Bitrus ya ce mata, “Ta yaya kuka yarda ku gwada Ruhun Ubangiji? Duba! Sawun mutanen da suka binne mijinki suna bakin ƙofa, za su kuwa ɗauke ki zuwa waje ke ma.”

10Nan take ta fāɗi a ƙafafunsa ta mutu. Sai samarin suka shigo ciki, suka kuwa same ta matacciya, suka ɗauke ta suka kai ta waje suka binne ta kusa da mijinta. 11Babban tsoro ya kama dukan ikkilisiya da kuma duk wanda ya ji game da abubuwan nan.

Manzanni sun warkar da mutane da yawa

12Manzannin suka yi ayyukan da alamu masu banmamaki masu yawa a cikin mutanen. Dukan masu bi kuwa sukan taru a Shirayin Solomon. 13Ba wanda ya yi karambanin shiga cikinsu, duk da haka mutane suna girmama su ƙwarai. 14Duk da haka, maza da matan da suke gaskata ga Ubangiji sai ƙaruwa suke, suka kuma ƙaru a yawa. 15A sakamakon haka, mutane suka kawo marasa lafiya a tituna suka kwantar da su a kan gadaje da tabarmai domin aƙalla inuwar Bitrus za tă bi kan waɗansunsu yayinda yake wucewa. 16Jama’a ma suka tattaru daga garuruwa kewaye da Urushalima suna kawo marasa lafiyarsu da kuma waɗanda mugayen ruhohi suke damun su, dukansu kuwa suka warke.

An tsananta wa manzanni

17Sai babban firist da dukan abokan aikinsa, waɗanda suke na ƙungiyar Sadukiyawa suka cika da kishi. 18Suka kama manzannin suka sa su a kurkukun da ake sa kowa da kowa. 19Amma da dare wani mala’ikan Ubangiji ya buɗe ƙofofin kurkukun ya fitar da su. 20Ya ce, “Ku je ku tsaya a filin haikali ku sanar wa mutane cikakken saƙon wannan sabon rai.”

21Da gari ya waye, sai suka shiga filin haikali, yadda aka faɗa musu, suka kuwa fara koyar da mutane.

Sa’ad da babban firist da abokan aikinsa suka iso, sai suka kira Majalisa gaba ɗaya dukan dattawan Isra’ila, suka kuma aika kurkuku a zo da manzannin. 22Amma da dogarawan suka iso kurkukun, ba su same su a can ba. Saboda haka suka dawo suka ba da labari, suka ce, 23“Mun iske kurkukun a kulle sosai, da masu gadi suna tsaye a bakin ƙofofin; amma da muka buɗe su, sai muka tarar ba kowa a ciki.” 24Da jin wannan labari, sai shugaban masu gadin haikali da manyan firistocin suka ruɗe, suna tunanin abin da wannan al’amari zai zama.

25Sai wani ya zo ya ce, “Ga shi! Mutanen da kuka sa a kurkuku suna tsaye a filin haikali suna koya wa mutane.” 26Da wannan, shugaban ya tafi tare da dogarawansa suka kawo manzannin. Sun kawo su amma fa ba ƙarfi da yaji ba, don suna tsoro kada mutane su jajjefe su da duwatsu.

27Da suka kawo manzannin, sai suka sa su suka bayyana a gaban Majalisar don babban firist ya tuhume su. 28Ya ce, “Mun kwaɓe ku da gaske kada ku ƙara koyarwa cikin wannan suna, duk da haka kun cika Urushalima da koyarwarku, har ma kuna so ku ɗora mana laifin jinin mutumin nan.”

29Bitrus da sauran manzannin suka amsa suka ce, “Dole ne mu yi wa Allah biyayya a maimakon mutane! 30Allahn kakanninmu ya tā da Yesu daga matattu, wanda kuka kashe ta wurin ratayewa a bisan itace. 31Allah ya ɗaukaka shi zuwa hannun damansa a matsayin Yerima da Mai Ceto don yă kawo tuba da gafarar zunubai ga Isra’ila. 32Mu shaidu ne ga waɗannan abubuwa, haka kuma Ruhu Mai Tsarki, wanda Allah ya ba wa waɗanda suke yin masa biyayya.”

33Da suka ji haka, sai suka yi fushi suka so su kashe su. 34Amma wani Bafarisiyen da ake kira Gamaliyel, wani malamin doka, wanda dukan mutane ke girmamawa, ya miƙe tsaye a Majalisar ya umarta a fitar da mutanen waje na ɗan lokaci. 35Sa’an nan ya yi musu jawabi ya ce, “Mutanen Isra’ila, ku yi kula da kyau da abin da kuke niyyar yi wa mutanen nan. 36Kwanan baya, Teyudas ya ɓullo, yana cewa wai shi wani mutum ne, kuma wajen mutane ɗari huɗu suka bi shi. Aka kuwa kashe shi, dukan masu binsa kuwa suka watse, kome ya wargaje. 37Bayansa, Yahuda mutumin Galili ya ɓullo a kwanakin ƙidaya, ya jagoranci mutane cikin tawaye. Shi ma aka kashe shi, dukan mabiyansa kuma aka watsar da su. 38Saboda haka, a wannan batu na yanzu, ina ba ku shawara. Ku ƙyale mutanen nan! Ku bar su su tafi! Gama in manufarsu ko ayyukansu na mutum ne, ai, zai rushe. 39Amma in daga Allah ne, ba za ku iya hana waɗannan mutane ba, za ku dai sami kanku kuna gāba da Allah ne.”

40Jawabinsa ya rinjaye su. Suka kira manzannin suka sa aka yi musu bulala. Sa’an nan suka kwaɓe su kada su ƙara magana a cikin sunan Yesu, suka kuma bar su suka tafi.

41Manzannin suka bar Majalisar, suna farin ciki domin an ga sun cancanta a kunyata su saboda Sunan nan. 42Kowace rana, a filin haikali da kuma gida-gida, ba su fasa koyarwa da kuma shelar labari mai daɗi cewa Yesu shi ne Kiristi ba.