מעשי השליחים 18 – HHH & HCB

Habrit Hakhadasha/Haderekh

מעשי השליחים 18:1-28

1לאחר מכן עזב פולוס את אתונה ובא לקורינתוס. 2שם הוא התוודע אל יהודי יליד פונטוס, בשם עקילס, אשר הגיע לא־מזמן מאיטליה יחד עם אשתו פריסקילה. עקילס ופריסקילה נמלטו למעשה מאיטליה, משום שהקיסר קלודיוס ציווה לגרש את כל היהודים מרומא. 3מאחר שהזוג עסק במקצועו של פולוס – אריגת יריעות אוהלים – החליט פולוס לגור בביתם ולעבוד יחד איתם.

4כל שבת ביקר פולוס בבית־הכנסת וניסה לשכנע בדבריו גם את היהודים וגם את היוונים. 5לאחר שהגיעו סילא וטימותיוס ממקדוניה, הקדיש פולוס את כל זמנו להטפה ולהוכחת משיחותו של ישוע ליהודים. 6אולם כשהתנגדו היהודים לפולוס וגידפו את ישוע, ניער פולוס את האבק מבגדיו ואמר: ”דמכם בראשכם! עשיתי את המוטל עלי, ומצפוני נקי. מעתה ואילך אלך לגויים!“

7הוא יצא מבית־הכנסת ועבר לגור בביתו של טיטוס יוסטוס, איש ירא־אלוהים שגר בקרבת מקום. 8אולם קריספוס – ראש בית־הכנסת – וכל בני ביתו האמינו באדון. גם קורינתיים רבים שהקשיבו לפולוס האמינו לדבריו ונטבלו במים.

9לילה אחד דיבר האדון ישוע אל פולוס בחזיון ואמר: ”אל תפחד! המשך לבשר ואל תחדל, 10כי אני איתך! איש לא יפגע בך לרעה, כי אנשים רבים בעיר הזאת שייכים לי.“

11וכך נשאר פולוס באותה עיר כשנה וחצי ולימד את דבר אלוהים. 12אולם כשנתמנה גליון למושל אכיה, ארגנו היהודים הפגנת מחאה נגד פולוס, והעמידוהו לדין לפני המושל. 13”האיש הזה מסית את בני־האדם לעבוד את אלוהים בדרך המנוגדת לחוק הרומאי!“ האשימו אותו. 14אולם עוד לפני שהספיק פולוס לפתוח את פיו ולהגן על עצמו, פנה גליון אל מאשימיו ואמר: ”הקשיבו, יהודים: אילו הבאתם לפני מקרה פשע, הייתי חייב להקשיב לכם, 15אולם כיוון שזוהי שאלה של הגדרות מילוליות, של שמות, מושגים ומונחים בנושא הדת שלכם, טפלו בכך אתם בעצמכם. אינני מעוניין לדון בעניין!“ 16והוא גירש אותם מאולם המשפט.

17הם הלכו ותפסו את סוסתניס, שנבחר לא־מזמן לראש בית־הכנסת, הכו אותו ועשו בו שפטים לפני כסא המשפט, אך לגליון לא היה אכפת.

18פולוס נשאר בקורינתוס עוד זמן־מה, ולאחר מכן נפרד לשלום מן המאמינים והפליג לסוריה יחד עם פריסקילה ועקילס. בקנכרי גילח פולוס את שער ראשו, משום שנדר נדר מסוים. 19כשהגענו לנמל אפסוס, הוא הלך לבית־הכנסת כדי לשוחח עם היהודים. 20הם ביקשו ממנו להישאר אצלם עוד ימים אחדים, אך פולוס השיב שאין לו זמן לכך. 21‏-22”אני מוכרח להגיע לירושלים לפני החג“, אמר להם. ”אולם אם ירצה השם, אשוב לבקר אתכם.“

פולוס הפליג לדרכו והגיע לקיסריה. הוא הלך לבקר את הקהילה, ולאחר מכן המשיך לאנטיוכיה. 23לאחר ששהה זמן־מה באנטיוכיה, המשיך בדרכו ועבר באזור גלטיה ובפריגיה. בכל מקום ביקר אצל המאמינים, עודד אותם ועזר להם להתחזק באמונתם.

24באותם ימים הגיע לאפסוס יהודי יליד אלכסנדריה, אפולוס שמו, אשר היה מטיף ומורה מוכשר ובקיא בתנ״ך. 25‏-26הוא היה מלומד בדרך האדון, ולימד היטב על־אודות ישוע, אבל ידע על טבילת יוחנן בלבד. בהתלהבות רבה ובאומץ לב הטיף אפולוס בבית הכנסת: פריסקילה ועקילס שמעו את דרשתו המרשימה והזמינו אותו לביתם והסבירו לו את דרך אלוהים ביתר דיוק.

27אפולוס החליט לנסוע ליוון, והאחים עודדו אותו לעשות כן. הם כתבו מכתב למאמינים ביוון וביקשו מהם לקבלו בחמימות. לאחר שהגיע ליוון השתמש בו אלוהים לחיזוק הקהילה המקומית, 28מפני שהצליח לסתור את טענות היהודים בוויכוחים פומביים, והוכיח לכולם, מתוך הכתוב בתנ״ך, שישוע הוא המשיח.

Hausa Contemporary Bible

Ayyukan Manzanni 18:1-28

A Korint

1Bayan haka, Bulus ya bar Atens ya tafi Korint. 2A can ya sadu da wani mutumin Yahuda mai suna Akwila, ɗan garin Fontus, wanda ya je can ba da daɗewa ba daga Italiya tare da matarsa Firiskila, gama Kalaudiyus ya umarci dukan Yahudawa su bar Roma. Sai Bulus ya tafi yă gan su, 3da yake shi ma mai ɗinkin tenti ne kamar su, sai ya zauna ya yi aiki tare da su. 4Kowace Asabbaci kuwa yakan yi muhawwara a majami’a, yana ƙoƙari yă rinjayi Yahudawa da Hellenawa.

5Sa’ad da Sila da Timoti suka iso daga Makidoniya, sai Bulus ya ba da kansa ga yin wa’azi kaɗai, yana tabbatar wa Yahudawa cewa Yesu shi ne Kiristi. 6Amma sa’ad da Yahudawa suka yi hamayya da Bulus suka kuma shiga zaginsa, sai ya karkaɗe tufafinsa a cikin rashin yarda, ya ce musu, “Alhakinku yana a kanku! Ba ni da wani laifi. Daga yanzu zan tafi wajen Al’ummai.”

7Sai Bulus ya bar majami’ar ya kuma tafi ƙofar da take kusa da gidan Titus Yustus, mai yi wa Allah sujada. 8Kirisbus, shugaban majami’a, da dukan iyalinsa suka gaskata Ubangiji; Korintiyawa masu yawa kuwa da suka ji shi suka gaskata, aka kuwa yi musu baftisma.

9Wata rana da dad dare, Ubangiji ya yi magana da Bulus a cikin wahayi ya ce, “Kada ka ji tsoro; ka ci gaba da yin magana, kada ka yi shiru. 10Gama ina tare da kai, ba kuma wanda zai fāɗa maka ya cuce ka, domin ina da mutane da yawa a wannan birni.” 11Saboda haka Bulus ya zauna a nan har shekara ɗaya da rabi, yana koya musu maganar Allah.

12Yayinda Galliyo yake muƙaddas Akayya, Yahudawa suka haɗa kai suka tasar wa Bulus, suka kuwa kawo shi cikin kotu. 13Suka yi zarge cewa, “Wannan mutum yana rarrashin mutane su yi wa Allah sujada a hanyoyin da suka saɓa wa doka.”

14A daidai sa’ad da Bulus yana shirin yin magana, sai Galliyo ya ce wa Yahudawan, “Da a ce ku Yahudawa kuna gunaguni game da munafunci, ko kuma wani babban laifi, da sai in iya sauraronku. 15Amma da yake ya shafi gardama ce game da kalmomi da sunaye da kuma dokarku, sai ku ji da ita da kanku. Ni ba zan zama mai shari’a kan irin waɗannan abubuwa ba.” 16Saboda haka ya kore su. 17Sai duk suka juya kan Sostenes shugaban majami’a suka yi masa dūka a gaban kotun. Amma Galliyo ko yă kula.

Firiskila, Akwila da Afollos

18Bulus kuwa ya ci gaba da zama a Korint na ’yan kwanaki. Sa’an nan ya bar ’yan’uwa ya shiga jirgin ruwa zuwa Suriya tare da Firiskila da Akwila. Kafin ya tashi, ya aske kansa a Kenkireya saboda alkawarin da ya yi. 19Suka isa Afisa, inda Bulus ya bar Firiskila da Akwila. Shi kansa ya shiga majami’a ya kuma yi muhawwara da Yahudawa. 20Sa’ad da suka roƙe shi ya ƙara ’yan kwanaki da su, bai yarda ba. 21Amma da yake barin wurin, ya yi alkawari cewa, “Zan dawo in Allah ya yarda.” Sa’an nan ya tashi daga Afisa a jirgin ruwa. 22Sa’ad da ya sauka a Kaisariya, sai ya haura ya gai da ikkilisiya sa’an nan ya gangara zuwa Antiyok.

23Bayan ya yi ’yan kwanaki a Antiyok, Bulus ya tashi daga can ya zaga ko’ina a yankin Galatiya da Firjiya, yana ƙarfafa dukan almajirai.

24Ana cikin haka sai wani mutumin Yahuda mai suna Afollos, ɗan ƙasar Alekzandariya, ya zo Afisa. Shi masani ne, yana da cikakken sani na Nassosi. 25An horar da shi a hanyar Ubangiji, ya kuma himma ƙwarai a magana, ya kuma yi koyarwa game da Yesu, daidai, ko da yake baftismar Yohanna ce kaɗai ya sani. 26Sai ya fara magana gabagadi a majami’a. Sa’ad da Firiskila da Akwila suka ji shi, sai suka gayyace shi gidansu suka ƙara bayyana masa hanyar Allah sosai.

27Sa’ad da Afollos ya so ya tafi Akayya, sai ’yan’uwa suka ƙarfafa shi suka kuma rubuta wa almajiran da suke can da su marabce shi. Da isowarsa, ya zama da taimako ƙwarai ga waɗanda ta wurin alheri suka gaskata. 28Gama da ƙwazo ya ƙaryata Yahudawa a muhawwara a fili, yana tabbatar daga Nassosi cewa Yesu shi ne Kiristi.