התגלות 6 – HHH & HCB

Habrit Hakhadasha/Haderekh

התגלות 6:1-17

1ראיתי את השה שובר את החותם הראשון, ואחת מארבע החיות קראה בקול שנשמע כרעם: ”בוא!“ 2הבטתי וראיתי לפני סוס לבן. רוכבו נשא בידו קשת, על ראשו הונח כתר והוא דהר קדימה כמנצח כדי לנצח.

3כששבר השה את החותם השני, שמעתי את החיה השנייה קוראת: ”בוא!“ 4הפעם הופיע סוס אדום. לרוכבו ניתנו חרב גדולה וסמכות להשבית את השלום בארץ, כדי שבני־האדם יהרגו זה את זה.

5כששבר השה את החותם השלישי, שמעתי את החיה השלישית קוראת: ”בוא!“ ואז הופיע סוס שחור וביד רוכבו מאזניים. 6מבין ארבע החיות שמעתי קול: ”כיכר לחם או קילו וחצי שעורה תמורת יום־עבודה, אך אל תזיקו לשמן וליין.“

7כששבר השה את החותם הרביעי, שמעתי את החיה הרביעית קוראת: ”בוא!“ 8הבטתי וראיתי סוס בצבע ירקרק, ושם רוכבו ”מוות“, ובעקבותיו בא ”שאול“. הם קיבלו שלטון על רבע מהעולם: להרוג ולהשמיד ברעב, במלחמות, במחלות ובטרף לחיות־הבר.

9כששבר השה את החותם החמישי, ראיתי מזבח ומתחתיו נשמות האנשים שהוצאו להורג על שום שקיימו והפיצו את דבר ה׳, ומשום עדותם הנאמנה.

10הנשמות זעקו בקול: ”ה׳ הקדוש והאמיתי, מתי תשפוט את אנשי העולם על העוול שעשו לנו? מתי תנקום את דמנו מיושבי הארץ?“ 11לכל אחת מהנשמות ניתנה גלימה לבנה, ונאמר להן לנוח עוד זמן־מה, עד אשר יושלם מספר אחיהם, משרתי המשיח, שסופם להיהרג למען המשיח.

12כששבר השה את החותם השישי, ראיתי רעידת אדמה חזקה; השמש השחירה כפחם, הירח האדים כדם; 13כוכבי השמים נפלו כתאנים שמושלכות ארצה, כשהרוח מניעה בכוח את עץ התאנה. 14השמים נעלמו כאילו היו מגילה שנגללה, וכל ההרים והאיים נותקו ממקומם. 15מלכי העולם, מנהיגיו, העשירים, קציני־צבא בכירים וכל בני־האדם – חשובים יותר וחשובים פחות, עבדים ובני־חורין – הסתתרו במערות ובסלעי ההרים. 16הם התחננו אל ההרים שיפלו עליהם ויסתירו אותם מפני היושב על כיסא־המלכות ומפני זעם השה, 17כי הגיע יום זעמו של ה׳, ומי יוכל להינצל?

Hausa Contemporary Bible

Ruʼuya ta Yohanna 6:1-17

Hatimai

1Na kalli yayinda Ɗan Ragon ya buɗe hatimin farko na hatimai bakwai ɗin nan. Sai na ji ɗaya daga cikin halittu huɗun nan masu rai ya yi magana da murya mai kama da tsawa ya ce, “Zo!” 2Na duba, can kuwa a gabana ga wani farin doki! Mai hawansa yana riƙe da baka, aka kuma ba shi rawani, ya yi sukuwa ya fito kamar mai nasara da ya kutsa don nasara.

3Sa’ad da Ɗan Ragon ya buɗe hatimi na biyun, sai na ji halitta mai rai na biyu ya ce, “Zo!” 4Sai wani doki ya fito, ja wur. Aka ba wa mai hawansa iko yă ɗauke salama daga duniya yă kuma sa mutane su kashe juna. Aka ba shi babban takobi.

5Sa’ad da Ɗan Ragon ya buɗe hatimi na uku, sai na ji halitta mai rai na uku ya ce, “Zo!” Na duba, can a gabana kuwa ga wani baƙin doki! Mai hawansa yana riƙe da abubuwan awo guda biyu a hannunsa. 6Sai na ji wani abu mai ƙara kamar wata murya a tsakiyar halittu huɗun nan masu rai tana cewa, “Kwatan alkama don albashin aikin yini, da kuma kwata uku na sha’ir don albashin yini guda, kada kuwa ka ɓata man da ruwan inabi!”

7Sa’ad da Ɗan Ragon ya buɗe hatimi na huɗu, sai na ji muryar halitta mai rai na huɗu ya ce, “Zo!” 8Na duba, can a gabana kuwa ga ƙodaɗɗen doki! An ba wa mai hawansa suna Mutuwa, Hades kuwa yana biye da shi. Aka ba su iko a kan kashi ɗaya bisa huɗu na duniya don su yi kisa da takobi, yunwa da annoba, har ma da namomin jeji na duniya.

9Sa’ad da ya buɗe hatimi na biyar, sai na ga a ƙarƙashin bagaden rayukan waɗanda aka kashe saboda maganar Allah da kuma shaidar da suka yi. 10Suka yi kira da babbar murya suka ce, “Ya Ubangiji Mai Iko Duka, Mai Tsarki da kuma Mai Gaskiya, sai yaushe za ka shari’anta mazaunan duniya ka kuma ɗauki mana fansar jininmu?” 11Sai aka ba wa kowannensu farin riga, aka kuma faɗa musu su ɗan jira kaɗan sai an cika adadin abokansu masu hidima da kuma ’yan’uwansu waɗanda za a kashe kamar yadda su ma aka kashe su.

12Ina kallo yayinda ya buɗe hatimi na shida. Sai aka yi babban girgizar ƙasa. Rana ta zama baƙa kamar gwado na gashin akuya, wata kuma gaba ɗaya ya zama ja wur kamar jini, 13taurarin sararin sama suka fāffāɗi a ƙasa, kamar yadda ɗanyun ’ya’yan ɓaure suke fāɗuwa daga itacen ɓaure sa’ad da iska mai ƙarfi ta jijjiga shi. 14Sararin sama kuwa ya janye kamar naɗaɗɗen littafi, ya yi ta naɗewa, aka kuma kawar da kowane dutse da kowane tsibiri daga wurinsa.

15Sa’an nan sarakunan duniya, hakimai, jarumawa, masu arziki, masu ƙarfi, da kowane bawa da kuma kowane ’yantacce ya ɓoye a cikin koguna da kuma cikin duwatsun tsaunuka. 16Suka kira duwatsu da tsaunuka suna cewa, “Ku fāɗi a kanmu ku kuma ɓoye mu daga fuskar wannan mai zama a kan kursiyi da kuma daga fushin Ɗan Ragon nan! 17Gama babbar ranar fushinsu ta zo, wa kuwa zai iya tsayawa?”