התגלות 20 – HHH & HCB

Habrit Hakhadasha/Haderekh

התגלות 20:1-15

1אחרי כן ראיתי מלאך יורד מן השמים, ובידו מפתח התהום ושרשרת גדולה וכבדה. 2המלאך תפס את התנין – הלא הוא הנחש הקדמוני, המלשין, השטן – וכבלו בשרשרת למשך אלף שנים. 3המלאך השליכו אל התהום, סגר ונעל את פי התהום, כדי שהשטן לא יוכל להתעות יותר את העמים עד שיחלפו אלף השנים. בתום אלף השנים הוא ישוחרר לזמן קצר. 4לאחר מכן ראיתי כיסאות שעליהם ישבו מקבלי סמכות המשפט. ראיתי גם את נשמותיהם של אלה אשר נרצחו על־שום עדותם למען ישוע המשיח ולמען דבר אלוהים, ואת נשמותיהם של אלה אשר לא השתחוו לחיה ולפסלה, ולא נשאו את אות החותם של החיה על מצחם או זרועם. כל אלה קמו לתחייה ומלכו עם המשיח אלף שנים.

5זאת תחיית המתים הראשונה. (יתר המתים קמו לתחייה רק לאחר אלף השנים). 6ברוכים וקדושים אלה שקמים בתחייה הראשונה; המוות השני לא יפגע בהם, כי יהיו כוהנים לאלוהים ולמשיחו וימלכו איתו אלף שנים.

7בתום אלף השנים ישוחרר השטן ממאסרו. 8הוא ילך להתעות את עמי־העולם – את גוג ומגוג שמספר צבאם כחול אשר על שפת הים – ויסיתם להילחם נגד אלוהים.

9הצבא האדיר הזה יעלה ויתפשט על מרחבי הארץ, ויתקיף את מחנה בני־אלוהים ואת (ירושלים) העיר האהובה. ברם אלוהים יוריד עליהם אש מן השמים שתשרוף אותם. 10השטן אשר הסיתם יושלך לאגם אש וגופרית, מקום שאליו הושלכו החיה ונביא השקר, והם יתייסרו יומם ולילה לעולם ועד.

11לאחר מכן ראיתי כיסא גדול ולבן, וראיתי גם את היושב עליו – זה אשר מפניו נמלטו הארץ והשמים, אך לא מצאו מקום להסתתר. 12ראיתי את המתים, את הקטנים והגדולים, עומדים לפני כיסא אלוהים; ראיתי ספרים נפתחים, ביניהם גם ספר החיים, והמתים נשפטו לפי מעשיהם הכתובים בספרים. 13הים נאלץ להשיב את המתים הקבורים בו. גם המוות והשאול נאלצו להשיב את מתיהם, וכל אחד נשפט בהתאם למעשיו. 14המוות והשאול הושלכו לאגם האש, שהוא המוות השני. 15כל אלה שלא נכתב שמם בספר החיים הושלכו גם הם לאגם האש.

Hausa Contemporary Bible

Ruʼuya ta Yohanna 20:1-15

Shekaru dubu

1Na kuma ga wani mala’ika yana saukowa daga sama, yana da mabuɗin Abis yana kuma riƙe da ƙaton sarƙa a hannunsa. 2Ya kama macijin, wannan tsohon maciji, wanda yake shi ne Iblis, ko kuwa Shaiɗan, aka kuma ɗaura shi har shekara dubu. 3Ya jefa shi cikin Abis, ya kuma kulle ya sa hatimi a kansa, don a hana kada yă ƙara ruɗin al’ummai, sai shekarun nan dubu sun cika. Bayan wannan, dole a sake shi na ɗan lokaci.

4Na ga kursiyoyi inda waɗanda aka ba su ikon shari’a suke zama a kai. Sai na ga rayukan waɗanda aka yanke kawunansu saboda shaidarsu don Yesu saboda kuma maganar Allah. Ba su yi wa dabban nan ko siffarta sujada ba, ba su kuma sami alamarta a goshinsu ko a hannuwansu ba. Suka sāke rayuwa daga matattu, suka yi mulki tare da Kiristi shekaru dubu. 5(Sauran matattu ba su sāke rayuwa ba, sai da shekaru dubun nan suka cika.) Wannan fa shi ne tashin matattu na farko. 6Masu albarka da kuma tsarki ne waɗanda suke da rabo a tashin matattu na farko. Mutuwa ta biyu ba ta da iko a kansu, sai dai za su zama firistocin Allah da kuma na Kiristi za su kuma yi mulki tare da shi na shekaru dubu.

Hallakar Shaiɗan

7Sa’ad da shekaru dubun nan suka cika, za a saki Shaiɗan daga kurkukun da yake, 8zai kuma fito don yă ruɗi al’ummai da suke a kursuyoyi huɗu na duniya, Gog da Magog, yă tattara su don yaƙi. Yawansu kuwa ya yi kamar yashi a bakin teku. 9Suka mamaye duk fāɗin duniya suka kuma kewaye sansanin mutanen Allah, birnin da yake ƙauna. Amma wuta ta fito daga sama ta cinye su. 10Aka jefa Iblis da ya ruɗe su cikin tafkin farar wuta, inda aka jefa dabban nan da annabin ƙaryan nan. Za a ba su azaba dare da rana har abada abadin.

An shari’anta matattu

11Sa’an nan na ga babban farin kursiyi da kuma wannan da yake zama a kansa. Duniya da sararin sama kuwa suka ɓace daga gabansa, babu wuri kuwa dominsu. 12Sai na ga matattu, babba da yaro tsaye a gaban kursiyin, aka kuma buɗe littattafai. Aka buɗe wani littafi, wanda yake shi ne littafin rai. Aka yi wa matattu shari’a bisa ga abin da suka aikata yadda yake a rubuce a cikin littattafai. 13Teku ya ba da matattu da suke cikinsa, mutuwa da Hades kuma suka ba da matattu da suke cikinsu, aka kuma yi wa kowane mutum shari’a bisa ga abin da ya aikata. 14Sa’an nan aka jefar da mutuwa da kuma Hades cikin tafkin wuta. Tafkin wutar nan kuwa shi ne mutuwa ta biyu. 15Duk wanda ba a sami sunansa a rubuce a cikin littafin rai ba, an jefar da shi cikin tafkin wutar nan.