הבשורה על-פי מתי 6 – HHH & HCB

Habrit Hakhadasha/Haderekh

הבשורה על-פי מתי 6:1-34

1”היזהרו שלא תעשו את מעשיכם הטובים לפני כולם, כדי שכולם יראו ויכבדו אתכם, כי ככה אין לכם שכר מאביכם שבשמים. 2אם אתה נותן נדבה, אל תספר על כך לכולם, כפי שעושים הצבועים. הם אף תוקעים בשופר בבית־הכנסת לכבוד זה, כדי שכולם יעריצו את צדקנותם. אני אומר לכם: הם יקבלו את מה שמגיע להם. 3אם אתה נותן נדבה, עשה זאת בסתר – אל תספר לידך השמאלית מה שעושה ידך הימנית. 4ואז אביכם שבשמים, הרואה במסתרים, יגמול לכם.

5”כשאתם מתפללים, אל תנהגו כמו הצבועים, המתפללים בפינות רחוב ובבית־הכנסת כדי שכולם יראו אותם. אני אומר לכם: שכרם אתם. 6כשאתם מתפללים, היכנסו לחדר לבד, נעלו את הדלת והתפללו בסתר אל אביכם. ואז אביכם שבשמים, הרואה את הנעשה במסתרים, ייתן לכם שכר בגלוי.

7‏-8”אל תחזרו שוב ושוב על אותה תפילה, כפי שנוהגים עובדי האלילים. הם חושבים שיקבלו תשובה רק אם יחזרו על תפילתם פעמים רבות. זכרו: אביכם יודע מה שאתם צריכים לפני שאתם מבקשים זאת ממנו! 9לכן התפללו כך:

’אבינו שבשמים, יתקדש שמך.

10תבוא מלכותך,

שרצונך ייעשה בארץ כמו בשמים.

11ספק לנו מדי יום את המזון הדרוש לנו.

12אנא סלח לנו על חטאינו, כשם שאנו סולחים לאלה שחטאו נגדנו.

13עזור לנו לעמוד נגד פיתויים וניסיונות,

והצל אותנו מכל רע

(כי שלך המלכות, הכוח והתפארת לעולמי עולמים. אמן‘).

14”אביכם שבשמים יסלח לכם אם תסלחו גם אתם לאלה שחוטאים נגדכם. 15אם לא תהיו מוכנים לסלוח להם, לא יסלח ה׳ גם לכם על חטאיכם.

16”כאשר אתם צמים, אל תפגינו זאת לפני כולם, כפי שעושים הצבועים. הם מנסים להראות עצובים ושהם בצום. הם יקבלו את מה שמגיע להם. 17אך אתם, כאשר אתם צמים, סדרו וטפחו את מראכם, 18כדי שאיש לא יחשוב שאתם רעבים – מלבד אביכם שבשמים הרואה במסתרים, והוא ייתן לכם את השכר המגיע לכם.

19”אל תצברו לכם רכוש בארץ, במקום שהוא עלול להחליד, להירקב או להיגנב. 20צברו את רכושכם בשמים, כי שם הוא בטוח מפני גנבה ולא יאבד את ערכו לעולם. 21במקום שבו נמצא אוצרכם שם נמצא גם לבכם ומחשבותיכם.

22”עין האדם היא אור גופו. אם עינך טהורה, תמיד יזרח אור השמש בתוך נפשך. 23אבל אם עינכם רעה, אזי תחשך כולך. מה רבה חשכה זאת! 24אינך יכול לעבוד שני אדונים; אתה תשנא את האחד ותאהב את האחר, או להיפך – תהיה נאמן לאחד ותזלזל באחר. אינך יכול לעבוד את האלוהים ואת הכסף!

25”משום כך אני אומר לכם שלא תדאגו לדברים חומרניים ויום־יומיים כמו מה לאכול ולשתות ומה ללבוש. הלא החיים חשובים מאוכל, והנפש חשובה מהלבוש. 26תחשבו על הציפורים למשל: אין הן דואגות למה שתאכלנה – הציפורים אינן זורעות, אינן קוצרות ואינן אוגרות מזון – כי אביכם שבשמים מאכיל אותן ודואג להן. והלא יקרים אתם לאלוהים הרבה יותר מהציפורים. 27חוץ מזה, מה תועיל דאגתכם? האם היא יכולה להוסיף עוד יום לחייכם, או עוד סנטימטר לקומתכם?

28”ומדוע אתם דואגים ללבוש? הביטו בפרחי הבר! אין הם דואגים למה שילבשו! 29ואילו שלמה המלך בכל תפארתו לא היה לבוש יותר יפה מהם! 30ואם אלוהים מלביש את פרחי השדה הצומחים היום ונובלים מחר, האם אינכם חושבים שילביש גם אתכם, חסרי אמונה שכמותכם?

31”לכן אל תדאגו לאוכל או ללבוש. 32בני־אדם שאינם מאמינים באלוהים דואגים יום־יום למה שיאכלו וישתו, אולם אביכם שבשמים יודע בדיוק מה אתם צריכים. 33בקשו לפני הכול את מלכותו של אלוהים וחיו ביושר, והוא ייתן לכם את כל מה שאתם צריכים.

34”אם כן אל תדאגו למחר; אלוהים ידאג למחר שלכם, ודיה לצרה בשעתה.“

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 6:1-34

Bayarwa ga mabukata

1“Ku yi hankali kada ku nuna ‘ayyukanku na adalci’ a gaban mutane, don su gani. In kuka yi haka, ba za ku sami lada daga wurin Ubanku da yake cikin sama ba.

2“Saboda haka sa’ad da kake ba wa masu bukata taimako, kada ka yi shelarsa, yadda munafukai suke yi a majami’u da kuma kan tituna, don mutane su yabe su. Gaskiya nake gaya muku, sun riga sun sami ladarsu cikakke. 3Amma sa’ad da kake ba wa masu bukata taimako, kada ka yarda hannun hagunka yă ma san abin da hannun damarka yake yi, 4don bayarwarka ta zama a ɓoye. Ubanka kuwa mai ganin abin da ake yi a ɓoye, zai sāka maka.

Addu’a

(Luka 11.2-4)

5“Sa’ad da kuma kuke addu’a, kada ku zama kamar munafukai, gama sun cika son yin addu’a a tsaye a cikin majami’u da kuma a bakin titi, don mutane su gan su. Gaskiya nake gaya muku, sun riga sun sami ladarsu cikakke. 6Amma sa’ad da kake addu’a, sai ka shiga ɗakinka, ka rufe ƙofa, ka yi addu’a ga Ubanka wanda ba a gani. Ubanka kuwa mai ganin abin da ake yi a ɓoye, zai sāka maka. 7Sa’ad da kuma kuke addu’a, kada ku yi ta maimaita magana, kamar marasa sanin Allah, domin suna tsammani za a ji su saboda yawan maganarsu. 8Kada ku zama kamar su, gama Ubanku ya san abin da kuke bukata kafin ma ku roƙe shi.

9“To, ga yadda ya kamata ku yi addu’a.

“ ‘Ubanmu wanda yake cikin sama,

a tsarkake sunanka,

10mulkinka yă zo

a aikata nufinka a duniya

kamar yadda ake yi a sama.

11Ka ba mu yau abincin yininmu.

12Ka gafarta mana laifofinmu,

kamar yadda mu ma muke gafarta wa masu yin mana laifi.

13Kada ka bari a kai mu cikin jarraba,

amma ka cece mu daga mugun nan.6.13 Ko kuwa daga mugu; waɗansu rubuce-rubucen hannun da ba su jima ba ɗaya, gama mulki da iko da ɗaukaka naka ne har abada. Amin.

14Gama in kuna yafe wa mutane sa’ad da suka yi muku laifi, Ubanku da yake cikin sama ma zai gafarta muku. 15Amma in ba kwa yafe wa mutane laifofinsu, Ubanku ma ba zai gafarta muku zunubanku ba.

Azumi

16“Sa’ad da kuma kuna azumi, kada ku ɓata fuska, yadda munafukai suke yi. Sukan ɓata fuskokinsu domin su nuna wa mutane cewa suna azumi. Gaskiya nake gaya muku, sun riga sun sami ladarsu cikakke. 17Amma sa’ad da kana azumi, ka shafa wa kanka mai, ka wanke fuskarka, 18domin kada mutane su ga alama cewa kana azumi, sai dai Ubanka kaɗai wanda ba a gani; Ubanka kuwa mai ganin abin da ake yi a ɓoye, zai sāka maka.

Ajiya a sama

(Luka 12.33,34)

19“Kada ku yi wa kanku ajiyar dukiya a duniya, inda asu da tsatsa suke ɓatawa, inda kuma ɓarayi sukan fasa, su yi sata. 20Amma ku yi wa kanku ajiyar dukiya a sama, inda ba tsatsa da asu da za su ɓata su, inda kuma ba ɓarayin da za su fasa, su yi sata. 21Gama inda dukiyarka take, a nan ne fa zuciyarka za tă kasance.

(Luka 11.34-36)

22“Ido shi ne fitilar jiki. In idanunka suna da kyau, dukan jikinka zai cika da haske. 23Amma in idanunka suna da lahani, dukan jikinka ma zai cika da duhu. To, in hasken da yake a cikinka duhu ne, duhun ya wuce misali ke nan!

(Luka 16.13)

24“Ba mai iya bauta wa iyayengiji biyu. Ko dai yă ƙi ɗaya, yă ƙaunaci ɗaya, ko kuwa yă yi aminci ga ɗaya, sa’an nan yă rena ɗayan. Ba dama ku bauta wa Allah, ku kuma bauta wa kuɗi gaba ɗaya.”

Kada ku damu

(Luka 12.22-31)

25“Saboda haka, ina gaya muku, kada ku damu game da rayuwarku, game da abin da za ku ci, ko abin da za ku sha; ko kuma game da jikinku, game da abin da za ku sa. Ashe, rai bai fi abinci ba, jiki kuma bai fi tufafi ba? 26Ku dubi tsuntsayen sararin sama mana; ba sa shuki ko girbi ko ajiya a rumbuna, duk da haka, Ubanku na sama yana ciyar da su. Ashe, ba ku fi su daraja nesa ba? 27Wane ne a cikinku ta wurin damuwa zai iya ƙara wa rayuwarsa ko sa’a ɗaya6.27 Ko kuwa a kamu guda ga tsayinsa?

28“Me ya sa kuke damuwa a kan riguna? Ku dubi yadda furannin jeji suke girma mana. Ba sa aiki ko saƙa. 29Duk da haka ina gaya muku ko Solomon cikin dukan darajarsa bai sa kayan adon da ya kai na ko ɗaya a cikinsu ba. 30In haka Allah yake yi wa ciyawar jeji sutura, wadda yau tana nan, gobe kuwa a jefa a cikin wuta, ba zai ma fi yi muku sutura ba, ya ku masu ƙarancin bangaskiya? 31Don haka, kada ku damu, kuna cewa, ‘Me za mu ci?’ Ko, ‘Me za mu sha?’ Ko kuma, ‘Me za mu sa?’ 32Gama marasa sanin Allah suna fama neman dukan waɗannan abubuwa, Ubanku na sama kuwa ya san kuna bukatarsu. 33Da farko dai, ku nemi mulkin Allah da kuma adalcinsa, za a kuwa ba ku dukan waɗannan abubuwa. 34Saboda haka kada ku damu game da gobe, gama gobe zai damu da kansa. Damuwar yau ma ta isa wahala.