הבשורה על-פי מתי 2 – HHH & HCB

Habrit Hakhadasha/Haderekh

הבשורה על-פי מתי 2:1-23

1ישוע נולד בעיר בית־לחם שבאזור יהודה, בימי המלך הורדוס. זמן קצר לאחר לידתו, הופיעו בירושלים מספר חוזי־כוכבים שבאו מארץ רחוקה במזרח, ושאלו: 2”היכן התינוק שנועד להיות מלך היהודים? ראינו את כוכבו במזרח ובאנו להשתחוות לו.“

3הורדוס נבהל מאוד משאלתם, וכמוהו נבהלו כל אנשי ירושלים. 4הוא כינס את מנהיגי היהודים ושאל אותם: ”האם אמרו לנו הנביאים היכן ייוולד המשיח?“

5ענו לו: ”כן, בבית לחם. הרי מיכה הנביא אמר:2‏.5 ב 5 מיכה ה 1 6’ואתה, בית־לחם בארץ יהודה, אינך צעיר באלופי יהודה, כי ממך יצא מושל אשר ירעה את־עמי ישראל‘. “

7הורדוס הזמין את חוזי־הכוכבים לפגישה סודית, ושאל אותם מתי בדיוק ראו לראשונה את הכוכב. 8לאחר מכן אמר להם: ”לכו לבית־לחם וחפשו את הילד. כשתמצאו אותו, שובו אלי והודיעו לי זאת, כדי שאוכל גם אני ללכת להשתחוות לו.“

9לאחר הפגישה עם המלך יצאו חוזי־הכוכבים לדרך, ולפתע הכוכב שראו במזרח הופיע לנגד עיניהם. הם הלכו בעקבות הכוכב עד שנעמד בדיוק מעל המקום שבו היה התינוק. 10הם שמחו מאוד.

11כשנכנסו חוזי־הכוכבים אל הבית שבו היה התינוק ומרים אמו, נפלו לפניו, השתחוו לו, ולאחר מכן פתחו את חבילותיהם ונתנו לו מתנות: זהב, לבונה ומור.

12בינתיים הזהיר אותם אלוהים בחלום שלא לחזור אל הורדוס, ומשום כך שבו חוזי־הכוכבים לארצם בדרך אחרת.

13לאחר שעזבו, נגלה מלאך ה׳ ליוסף בחלום ואמר: ”קום, ברח למצרים עם התינוק ועם אמו, והישאר שם עד שאומר לך לחזור, כי הורדוס רוצה להרוג את הילד.“ 14באותו לילה יצא יוסף עם מרים ועם הילד למצרים, 15ונשאר אתם שם עד מותו של הורדוס. כך התקיימה הנבואה:2‏.15 ב 15 הושע יא 1 ”וממצרים קראתי לבני.“

16כשהורדוס הבין שחוזי־הכוכבים התחמקו ממנו, הוא מאוד כעס. הוא שלח חיילים לבית־לחם וציווה עליהם להרוג כל ילד זכר עד גיל שנתיים (כי החוזים סיפרו לו שראו את הכוכב כשנתיים קודם לכן), בבית לחם עצמה ובכל כפרי הסביבה. 17מעשה אכזרי זה של הורדוס קיים את הנבואה של ירמיהו:2‏.17 ב 17 ירמיהו לא 15

18”קול ברמה נשמע, נהי בכי תמרורים,

רחל מבכה על בניה,

מאנה להינחם על בניה כי איננו.“

19לאחר מותו של הורדוס נגלה מלאך ה׳ בחלום ליוסף במצרים, ואמר לו: 20”קום, קח את התינוק ואת אמו לישראל, כי אלה שרצו להרוג את הילד כבר מתו.“ 21יוסף לקח את ישוע ואת מרים ויצא אתם בדרך לישראל.

22בהיותם בדרך שמעו שהמלך החדש אינו אלא ארכילאוס, בנו של הורדוס, ופחדו מאוד. בחלום נוסף יוסף הוזהר שלא להתיישב ביהודה, אז הם המשיכו לגליל 23והשתקעו בנצרת. זה קרה כדי לקיים את דברי הנביאים שכינו אותו ”נצרי“.2‏.23 ב 23 5 ראה: ישעיהו יא 1

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 2:1-23

Ziyarar Masana

1Bayan an haifi Yesu a Betlehem, a Yahudiya, a zamanin Sarki Hiridus, sai waɗansu Masana,2.1 A al’adance Masu Hikima daga gabas suka zo Urushalima 2suka yi tambaya suka ce, “Ina shi wanda aka haifa sarkin Yahudawa? Gama mun ga tauraronsa a gabas2.2 Ko kuwa a tauraro sa’ad da ya taso mun kuwa zo ne domin mu yi masa sujada.”

3Da Sarki Hiridus ya ji wannan, sai hankalinsa ya tashi haka ma na dukan Urushalima. 4Bayan ya kira dukan manyan firistoci da malaman dokoki na mutane wuri ɗaya, sai ya tambaye su inda za a haifi Kiristi. 5Suka amsa suka ce, “A Betlehem ne, cikin Yahudiya, gama haka annabin ya rubuta.

6“ ‘Amma ke Betlehem, a cikin ƙasar Yahuda,

ba ke ce mafi ƙanƙanta a cikin masu mulki a Yahuda ba,

gama daga cikinki mai mulki zai zo,

wanda zai zama makiyayin mutanena Isra’ila.’2.6 Mik 5.2

7Sai Hiridus ya kira Masanan nan a ɓoye, yă gano daga wurinsu daidai lokacin da tauraron ya bayyana. 8Sai ya aike su Betlehem ya ce, “Ku je ku binciko a hankali game da yaron nan. Da kun same shi, sai ku kawo mini labari nan da nan, domin ni ma in je in yi masa sujada.”

9Bayan sun saurari sarki, sai suka kama hanyarsu, tauraron da suka gani a gabas kuwa yana tafe a gabansu, sai da ya kai inda yaron yake. 10Da suka ga tauraron, sai suka yi farin ciki ƙwarai. 11Suka shiga gidan, suka kuwa ga yaron tare da mahaifiyarsa Maryamu. Suka durƙusa har ƙasa, suka yi masa sujada. Sa’an nan suka kunce dukiyarsu, suka miƙa masa kyautai na zinariya da na turare da na mur. 12Bayan an gargaɗe su cikin mafarki kada su koma wurin Hiridus, sai suka koma ƙasarsu ta wata hanya dabam.

Tserewa zuwa Masar

13Bayan sun tafi, sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusuf a mafarki ya ce, “Tashi, ka ɗauki yaron da mahaifiyarsa, ku gudu zuwa Masar. Ku zauna a can sai na gaya muku, gama Hiridus zai nemi yaron don yă kashe.”

14Sai Yusuf ya tashi, ya ɗauki yaron da mahaifiyarsa da dad dare suka tafi Masar, 15inda ya zauna har sai da Hiridus ya mutu. Ta haka kuwa aka cika abin da Ubangiji ya faɗa ta bakin annabin cewa, “Daga Masar na kira ɗana.”2.15 Hos 11.1

16Da Hiridus ya gane cewa Masanan nan sun yi masa wayo, sai ya husata ƙwarai, ya yi umarni cewa a karkashe dukan ’yan yara maza da suke a Betlehem da kewayenta, daga masu shekara biyu zuwa ƙasa, bisa ga lokacin da ya sami labarin daga Masanan nan. 17Sai abin da aka faɗa ta bakin annabi Irmiya ya cika, cewa,

18“An ji murya a Rama,

tana kuka da makoki mai tsanani,

Rahila ce take kuka domin ’ya’yanta,

an kāsa ta’azantar da ita,

don ba su.”2.18 Irm 31.15

Komowa zuwa Nazaret

19Bayan Hiridus ya mutu, sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusuf a mafarki a Masar, 20ya ce, “Tashi, ka ɗauki yaron da mahaifiyarsa ku tafi ƙasar Isra’ila, domin waɗanda suke neman ran yaron sun mutu.”

21Sai ya tashi, ya ɗauki yaron da mahaifiyarsa suka tafi ƙasar Isra’ila. 22Amma da ya ji Arkelawus ne yake mulki a Yahudiya a matsayin wanda ya gāji mahaifinsa Hiridus, sai ya ji tsoron zuwa can. Bayan an gargaɗe shi a mafarki, sai ya ratse zuwa gundumar Galili, 23ya je ya zauna a wani garin da ake kira Nazaret. Ta haka aka cika abin da aka faɗa ta bakin annabawa cewa, “Za a ce da shi Banazare.”