הבשורה על-פי לוקס 5 – HHH & HCB

Habrit Hakhadasha/Haderekh

הבשורה על-פי לוקס 5:1-39

1יום אחד עמד ישוע על חוף הכינרת ובישר את דבר האלוהים. מספר הנוכחים הלך וגדל, עד שהם נדחפו ונדחקו אליו מכל צד. 2ישוע הבחין בשתי סירות ריקות שעגנו ליד החוף. בעלי הסירות, שהיו דייגים במקצועם, רחצו באותו זמן את רשתותיהם. 3ישוע עלה על אחת הסירות, שהייתה של שמעון, וביקש ממנו להרחיק מעט את הסירה מהחוף, כדי שיוכל לשבת בתוכה ולדבר אל הקהל.

4לאחר שסיים ישוע לדבר אל הקהל, פנה אל שמעון ואמר: ”השט את הסירה אל מים עמוקים והשלך את הרשתות כדי לדוג.“

5”רבי,“ השיב שמעון, ”בלילה האחרון עבדנו קשה מאוד ולא תפסנו כלום. אולם אם אתה אומר לנו להשליך את הרשתות, נעשה כדברך.“

6הם השליכו את הרשתות לים, והפעם תפסו כל כך הרבה דגים עד שהרשתות היו כבדות מדי והחלו להיקרע! 7הם קראו לעזרתם את חבריהם שבסירה השנייה, ומילאו את שתי הסירות בדגים עד שכמעט טבעו!

8כשראה שמעון פטרוס את הפלא הגדול, נפל על ברכיו לרגלי ישוע ואמר: ”אדוני, עזוב אותי לנפשי, כי אני חוטא גדול מדי ואיני ראוי להיות במחיצתך.“ 9‏-10שמעון אמר דברים אלה משום שהוא וכל הנוכחים איתו, כולל שותפיו יעקב ויוחנן בני־זַבְדִּי, היו בתדהמה גדולה לנוכח השלל הבלתי רגיל.

”אל תפחד.“ אמר ישוע לשמעון. ”מעתה ואילך תהיה דייג של בני אדם.“

11לאחר שהשיטו את הסירות לחוף עזבו הכול והלכו אחרי ישוע. 12באחד הכפרים שבהם ביקר ישוע היה אדם נגוע בצרעת. בראותו את ישוע נפל האיש לרגליו והתחנן: ”אדוני, אם רק תרצה תוכל לרפא אותי.“

13ישוע הושיט את ידו, נגע במצורע ואמר: ”ודאי שאני רוצה. הירפא!“ ומיד נעלמה הצרעת.

14”אל תספר את הדבר לאיש!“ ציווה עליו ישוע. ”לך מיד אל הכהן והראה לו שנרפאת. אל תשכח לקחת איתך קרבן – כפי שציווה משה על המטוהרים מצרעת – כדי שכולם יראו שנרפאת.“ 15בכל זאת התפשטו השמועות על גבורתו של ישוע במהירות רבה, ואנשים רבים באו להקשיב לדבריו ולהירפא ממחלותיהם. 16אף־על־פי־כן התחמק מהם ישוע לעיתים קרובות והלך למקומות מבודדים כדי להתפלל.

17יום אחד, כשלימד ישוע כמנהגו, התקבצו סביבו בין השאר גם פרושים וסופרים שבאו מכפרי הגליל, מיהודה ומירושלים, וה׳ העניק לו גבורה גדולה לרפא את החולים.

18כעבור זמן קצר הופיעו מספר אנשים שנשאו חולה משותק על אלונקה. הם רצו להביא את החולה לפני ישוע, 19אולם בשל הצפיפות הרבה לא הצליחו לפלס דרך אל תוך הבית. נושאי האלונקה לא נואשו; הם עלו על גג הבית, עקרו כמה רעפים ממקומם והורידו את האלונקה מהגג אל אמצע החדר – לרגלי ישוע.

20כשראה ישוע את אמונתם, אמר לאיש המשותק: ”ידידי, נסלחו לך חטאיך!“

21”למי הוא חושב את עצמו?“ שאלו הפרושים והסופרים בלבם. ”הוא מחלל את שם האלוהים, רק אלוהים יכול לסלוח על חטאים!“ 22ישוע הבין את מחשבותיהם ולכן השיב להם: ”מדוע אתם חושבים שאני מחלל את שם אלוהים? 23מה לדעתכם קל יותר, לומר ’נסלחו לך חטאיך‘, או ’קום והתהלך‘? 24אני אוכיח לכם כי לבן־האדם יש בארץ סמכות מלאה לסלוח על חטאים!“ ישוע פנה אל האיש המשותק ופקד עליו: ”קום! קפל את האלונקה שלך ולך הביתה.“

25מיד קפץ האיש על רגליו לנגד עיניהם, קיפל את האלונקה שלו והלך לביתו כשהוא מהלל את האלוהים. 26כל הנוכחים נדהמו. ”היום ראינו פלא גדול“, אמרו ביראה והללו את האלוהים. 27לאחר מכן יצא ישוע מהעיר ופגש בדרך גובה־מכס אחד, לוי שמו, יושב בשער בית־המכס.

”בוא והיה תלמיד שלי“, אמר לו ישוע. 28לוי קם על רגליו, עזב הכול מאחוריו והלך אחרי ישוע.

29ערב אחד הכין לוי ארוחה חגיגית לכבוד ישוע והזמין גובי־מכס מהעבודה, ידידים, שכנים וקרובים.

30אולם הדבר לא מצא־חן בעיני הסופרים והפרושים, אשר התלוננו באוזני תלמידיו של ישוע: ”איך הוא יכול לאכול ולשתות בחברת החוטאים האלה?“ 31”החולים הם הזקוקים לרופא, לא הבריאים!“ השיב להם ישוע. 32”לא באתי לקרוא לצדיקים לחזור בתשובה, כי אם לחוטאים.“

33הם המשיכו להתלונן ואמרו: ”תלמידי יוחנן המטביל צמים לעיתים קרובות ומתפללים, וגם הפרושים נוהגים כך. מדוע אין תלמידיך צמים?“ 34”האם אנשים שמחים צמים?“ השיב ישוע. ”האם אורחים המוזמנים לחתונה צמים בחגיגת החתן? 35אולם יבוא יום שהחתן יילקח מהם ואז יצומו.“

36ישוע סיפר להם את המשל הבא: ”איש אינו קורע חולצה חדשה כדי לתפור ממנה טלאי על חולצה ישנה. מי שעושה כך לא זו בלבד שהוא מקלקל את החולצה החדשה, אלא שגם אינו יכול ליהנות מהחולצה הישנה, כי הטלאי אינו מתאים.

37”איש אינו שם יין חדש בחביות ישנות ורקובות, מפני שהיין החדש יבקע את החביות, וכך היין יישפך והחביות תיהרסנה. 38יין חדש יש לשים בחביות חדשות. 39אדם הרגיל לשתות יין ישן אינו חפץ לשנות את מנהגו ולשתות יין חדש. ’היין הישן מוצא־חן בעיני‘, הוא יאמר, ולא ירצה אפילו לטעום מהיין החדש.“

Hausa Contemporary Bible

Luka 5:1-39

Kiran almajirai na farko

(Mattiyu 8.14-17; Markus 1.29-34)

1Wata rana, Yesu yana tsaye a bakin Tafkin Gennesaret, mutane kuma suna ta matsawa kewaye da shi, domin su ji maganar Allah, 2sai ya hangi jiragen ruwa biyu a bakin tafkin, waɗanda masu kamun kifi suka bari suna wankin abin kamun kifinsu. 3Sai ya shiga ɗaya jirgin ruwan da yake na Siman, ya kuma roƙe shi yă tura shi kaɗan daga gaci. Sai ya zauna a jirgin ruwan, ya koyar da mutane daga ciki.

4Da ya gama magana, sai ya ce wa Siman, “Ka tuƙa jirgin zuwa inda akwai zurfi, ka saukar da abin kamun kifinka ka kama kifi.”

5Siman ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, duk dare mun yi ta fama ba mu kama kome ba, amma tun da ka ce haka, zan saki abin kamun kifin.”

6Da suka yi haka, sai suka kama kifi da yawa, har abin kamun kifinsu suka fara tsintsinkewa. 7Sai suka kira abokansu a ɗaya jirgin, su zo su taimake su, suka kuwa zo. Suka cika jiragen biyu da kifi cif, har jiragen suka fara nutsewa.

8Da Siman Bitrus ya ga wannan, sai ya fāɗi a gaban Yesu ya ce, “Rabu da ni, Ubangiji. Ni mai zunubi ne!” 9Gama mamaki ya kama shi da abokansa duka, saboda yawan kifin da suka kama. 10Yaƙub da Yohanna, ’ya’yan Zebedi, abokan aikin Siman su ma suka yi mamaki.

Sai Yesu ya ce wa Siman, “Kada ka ji tsoro, daga yanzu za ka riƙa kama mutane ne.” 11Sai suka jawo jiragen ruwansu zuwa gaci, suka bar kome da kome, suka bi shi.

Warkar da kuturu

(Mattiyu 8.1-4; Markus 1.40-45)

12Yayinda Yesu yake ɗaya daga cikin garuruwan nan, sai ga wani mutum wanda kuturta ta ci ƙarfinsa. Da ganin Yesu, sai ya fāɗi da fuskarsa a ƙasa, ya roƙe shi ya ce, “Ubangiji, in ka yarda, kana iya ka tsabtacce ni.”

13Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka zama da tsabta!” Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi.

14Sai Yesu ya umarce shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayu da Musa ya umarta, saboda tsarkakewarka ta zama shaida a gare su.”

15Duk da haka, labarinsa ya ƙara bazuwa sosai, har taron mutane suka dinga zuwa don jinsa, da kuma neman warkarwa daga cututtukansu. 16Amma Yesu sau da yawa, yakan keɓe kansa zuwa wuraren da ba kowa, yă yi addu’a.

Yesu ya warkar da shanyayye

(Mattiyu 9.1-8; Markus 2.1-12)

17Wata rana, da yake cikin koyarwa, waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki waɗanda suka zo daga kowane ƙauye a Galili, Yahudiya da Urushalima kuwa suna zaune. Ikon Ubangiji yana nan don yă warkar da masu ciwo. 18Sai ga waɗansu mutane suka kawo wani shanyayye a kan tabarma. Suka yi ƙoƙari su shigar da shi cikin gidan, domin su kwantar da shi a gaban Yesu. 19Da suka ga babu hanyar da za su bi saboda taron, sai suka haura rufin, suka saukar da shi a kan tabarmarsa, ta bakin ramin da suka huda a rufin, suka ajiye shi a tsakiyar taron, a gaban Yesu.

20Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce, “Saurayi, an gafarta maka zunubanka.”

21Farisiyawa da malaman dokoki suka fara yin tunani a zukatansu, “Wane ne wannan mutum da yake saɓo haka? Wa zai iya gafarta zunubai, in ba Allah kaɗai ba?”

22Yesu ya san abin da suke tunani, sai ya yi tambaya ya ce, “Don me kuke tunanin waɗannan abubuwa a zukatanku? 23Wanne ya fi sauƙi, a ce, ‘An gafarta maka zunubanka,’ ko kuma a ce, ‘Tashi, ka yi tafiya’? 24Amma domin ku san cewa Ɗan Mutum yana da iko a duniya ya gafarta zunubai.” Sai ya ce wa shanyayyen, “Na ce maka, tashi, ɗauki tabarmarka ka tafi gida.” 25Nan da nan, ya tashi tsaye a gabansu, ya ɗauki tabarmar da yake kwance a kai, ya tafi gida, yana yabon Allah. 26Kowa ya yi mamaki, ya kuma yabi Allah. Suka cika da tsoro, suna cewa, “Mun ga abubuwan banmamaki yau.”

Kiran Lawi

(Mattiyu 9.9-13; Markus 2.13-17)

27Bayan wannan, sai Yesu ya fita, ya ga wani mai karɓar haraji, mai suna Lawi, yana zaune a wurin da ake karɓar haraji. Yesu ya ce masa, “Bi ni.” 28Sai Lawi ya tashi, ya bar kome da kome, ya bi shi.

29Sai Lawi ya shirya wa Yesu wani babban liyafa a gidansa. Wani babban taron na masu karɓar haraji, tare da waɗansu suna cin abinci tare da su. 30Amma Farisiyawa da malaman dokokin da suke a ƙungiyarsu, suka yi wa almajiransa gunaguni, suna cewa, “Don me kuke ci, kuke sha tare da masu karɓar haraji da masu zunubi?”

31Yesu ya amsa musu ya ce, “Ai, masu lafiya ba sa bukatar likita, sai dai marasa lafiya. 32Ban zo don in kira masu adalci ba, sai dai masu zunubi zuwa ga tuba.”

An tuhumi Yesu a kan azumi

(Mattiyu 9.14-17; Markus 2.18-22)

33Suka ce masa, “Almajiran Yohanna sukan yi azumi da addu’a, haka ma almajiran Farisiyawa, amma naka sai ci da sha.”

34Yesu ya amsa ya ce, “Za ku iya sa abokan ango yin azumi yayinda yake tare da su? 35Amma lokaci yana zuwa, da za a ɗauke ango daga gare su. A waɗancan kwanakin ne za su yi azumi.”

36Sai ya faɗa musu wannan misali ya ce, “Ba wanda yakan yage ƙyalle daga sabuwar riga ya yi wa tsohuwar riga faci. In ya yi haka, zai yage sabuwar rigar, kuma facin daga sabuwar ba zai dace da tsohuwar rigar ba. 37Kuma ba wanda yakan zuba sabon ruwan inabi a cikin tsofaffin salkuna. In ya yi haka, sabon ruwan inabi zai farfashe salkunan, ruwan inabin yă zube, salkunan kuma su lalace. 38A’a, sai dai a zuba sabon ruwan inabi a sababbin salkuna. 39Kuma ba wanda yakan so shan sabon ruwan inabi bayan ya sha tsohon, don yakan ce, ‘Ai, tsohon ya fi kyau.’ ”