הבשורה על-פי לוקס 20 – HHH & HCB

Habrit Hakhadasha/Haderekh

הבשורה על-פי לוקס 20:1-47

1באחד מאותם ימים, כשלימד ישוע את העם בבית־המקדש וסיפר לו את בשורת ה׳, ניגשו אליו הכוהנים, הסופרים והזקנים ושאלו: 2”באיזו רשות אתה עושה את כל הדברים האלה?“

3”אענה לשאלתכם בתנאי שתענו לשאלתי“, השיב להם ישוע. 4”האם יוחנן המטביל נשלח על־ידי אלוהים או על־ידי בני־אדם?“

5הם התייעצו ביניהם: ”אם נגיד שאלוהים שלח את יוחנן, ישוע ישאל אותנו מדוע לא האמנו בו. 6אבל אם נגיד שאלוהים לא שלח את יוחנן, העם יתנפל עלינו, כי כולם מאמינים שיוחנן היה נביא מאת אלוהים.“ 7לבסוף השיבו שאינם יודעים את התשובה. 8”אם כן, גם אני לא אשיב לשאלתכם“, אמר ישוע.

9ישוע פנה אל העם וסיפר להם את המשל הבא: ”איש אחד נטע כרם ענבים, השכיר אותו לכורמים זרים ונסע לארץ רחוקה לכמה שנים. 10בהגיע מועד הבציר שלח בעל הכרם אחד מאנשיו לאסוף את חלקו ביבול הענבים. אבל הכורמים הכו את השליח ושלחו אותו חזרה לאדוניו בידיים ריקות. 11בעל הכרם שלח שליח אחר, אולם גורלו היה כגורל קודמו; הכורמים הכו אותו, קיללו אותו ושלחוהו בידיים ריקות. 12בעל הכרם שלח אדם שלישי, אבל גם אותו הם פצעו וגירשו משם.

13” ’מה אעשה?‘ שאל את עצמו בעל הכרם. ’אולי אם אשלח את בני האהוב הם יפחדו מפניו ויכבדו אותו‘. 14אולם כשראו הכורמים את הבן אמרו: ’יש לנו כאן הזדמנות: הבן הזה יירש את הכרם לאחר מות אביו, אולם אם נהרוג אותו נזכה אנחנו בכרם!‘ 15והכורמים גירשו את הבן מהכרם והרגו אותו.

”מה לדעתכם יעשה בעל הכרם? 16אני אומר לכם, הוא יבוא בעצמו, יהרוג את הכורמים וישכיר את הכרם לאחרים.“

”חס וחלילה שיעשו כך האנשים!“ קראו השומעים.

17ישוע נעץ בהם את מבטו ואמר: ”מה לדעתכם כוונת הפסוק בתהלים:20‏.17 כ 17 תהלים קיח 22 ’אבן מאסו הבונים, הייתה לראש פינה‘?“ 18ישוע הוסיף: ”מי שייפול על האבן הזאת יתנפץ לרסיסים, ומי שתיפול עליו האבן ישחק לאבק.“

19הסופרים וראשי הכוהנים הבינו שהם הכורמים הרשעים במשל ורצו לאסור את ישוע, אבל הם פחדו שמא העם יחולל מהומות.

20הסופרים וראשי הכוהנים ציפו להזדמנות מתאימה לאסור את ישוע ולמסור אותו לידי השלטונות. יום אחד שלחו אליו מרגלים בדמות אנשים תמימים, כדי שינסו להכשילו בלשונו.

21”רבי,“ פתחו מרגלים אלה, ”אנחנו יודעים שאתה איש ישר, ושאיש אינו יכול להשפיע עליך לשקר. אנחנו גם יודעים שאתה באמת מלמד את דבר־אלוהים. 22אמור לנו, האם עלינו לשלם מס לקיסר הרומאי או לא?“

23ישוע הבין את מזימתם ולכן ענה: 24”תנו לי מטבע ואומר לכם. של מי הדמות החקוקה כאן? ושל מי השם החקוק מתחת לדמות?“

”של הקיסר“, השיבו.

25”אם כן, תנו לקיסר את מה ששייך לו, ותנו לאלוהים את מה ששייך לאלוהים!“

26ניסיונם להכשילו בלשונו לא הצליח. הם התפעלו כל־כך מתשובותיו עד שלא היו מילים בפיהם.

27חבורה של צדוקים (שאינם מאמינים בתחיית המתים) באה אל ישוע ושאלה: 28”רבי, משה רבנו לימד אותנו בתורה שאם אדם נשוי מת ואינו משאיר אחריו ילדים, חייב אחיו להתחתן עם האלמנה, כדי שתוכל ללדת בן שישא את שם המת. 29במשפחה אחת היו שבעה אחים. האח הבכור התחתן וכעבור זמן קצר מת ולא השאיר אחריו בן. 30האח השני התחתן עם האלמנה, וגם הוא מת ולא השאיר בן. 31כך היה גם עם האח השלישי. בקיצור, כל שבעת האחים התחתנו עם האישה האחת, כולם מתו ולא השאירו אחריהם ילדים. 32לבסוף מתה גם האישה.

33”רבי, למי תהיה שייכת האישה בתחיית המתים? הלא כל השבעה התחתנו אתה!“ 34”נשואין הם רק בשביל האנשים בעולם הזה“, השיב להם ישוע. 35”אלה שיזכו לקום מן המתים ולחיות לנצח בעולם הבא, לא יינשאו. 36בעולם הבא הם יהיו כמלאכים ושוב לא יכולים למות. הם גם בני־אלוהים, משום שקמו לתחייה. 37בנוגע לשאלתכם אם יקומו המתים לתחייה, משה רבנו אשרר בתורה את דבר תחיית המתים. כשתיאר משה כיצד נגלה אליו ה׳ בסנה הבוער, הוא קרא לה׳: ’אלוהי אברהם, אלוהי יצחק ואלוהי יעקב‘. 38זה כדי לומר שה׳ הוא אלוהי החיים ולא של המתים, כי בעיני אלוהים האנשים האלה חיים.“

39”יפה ענית, רבי“, שיבחו אותו סופרים אחדים, 40ואיש לא העז לשאול אותו שאלות נוספות.

41שאל אותם ישוע שאלה: ”מדוע טוענים האנשים שהמשיח הוא בן־דוד? 42הלא דוד עצמו אומר בתהלים:20‏.42 כ 42 תהלים קי 1 ’נאם ה׳ לאדני, שב לימיני 43עד אשית אויביך הדם לרגליך‘. 44כיצד יכול המשיח להיות בנו של דוד וגם אדוניו?“

45בעוד כל העם מקשיב לו פנה ישוע אל תלמידיו ואמר: 46”היזהרו מהסופרים שאוהבים ללבוש גלימות ולהיראות לפני האנשים בשווקים, כדי שכולם ייתנו להם כבוד. הם אוהבים לשבת במושבות הנכבדים בבית־הכנסת ובסעודות וחגיגות. 47הם מעמידים פני צדיקים תמימים, ומתפללים בציבור תפילות ארוכות כדי לעשות רושם, אבל באותה עת הם מרמים את האלמנות ומגרשים אותן מבתיהן. משום כך אלוהים ישפוט אותם בחומרה רבה מאוד.“

Hausa Contemporary Bible

Luka 20:1-47

An yi shakkar ikon Yesu

(Mattiyu 21.23-27; Markus 11.27-33)

1Wata rana da Yesu yana koyar da mutane, yana musu wa’azin bishara a filin haikalin, sai manyan firistoci da malaman dokoki, tare da dattawan suka zo wurinsa. 2Suka ce masa, “Gaya mana, da wane iko kake yin waɗannan abubuwa. Wa ya ba ka wannan ikon?”

3Ya amsa ya ce, “Ni ma zan yi muku wata tambaya. Ku faɗa mini, 4baftismar Yohanna, daga sama ne ta fito, ko kuwa daga wurin mutane ne?”

5Sai suka yi shawara da junansu, suka ce, “In muka ce, ‘Daga sama ne,’ zai tambaya, ‘To, don me ba ku gaskata shi ba?’ 6Amma in kuma muka ce, ‘Daga mutane ne,’ dukan mutanen za su jajjefe mu da duwatsu, domin sun tabbata cewa, Yohanna annabi ne.”

7Don haka, sai suka amsa cewa, “Ba mu san inda ta fito ba.”

8Yesu ya ce, “To, ni ma ba zan gaya muku, ko da wane iko ne, nake yin waɗannan abubuwa ba.”

Misalin ’yan haya

(Mattiyu 21.33-46; Markus 12.1-12)

9Sai ya ci gaba da gaya wa mutanen wannan misali ya ce, “Wani mutum ya yi gonar inabi, sai ya ba da hayarta ga waɗansu manoma, sa’an nan ya yi wata doguwar tafiya. 10A lokacin girbi, sai ya aiki bawa zuwa wurin masu hayan, don su ba shi daga cikin ’ya’yan inabin. Amma ’yan hayan suka yi wa bawan nan dūka, suka kore shi hannu wofi. 11Ya sāke aikan wani bawa, shi ma suka yi masa dūka, suka kunyata shi, suka kuma kore shi hannu wofi. 12Har yanzu, ya sāke aikan na uku, amma suka ji masa rauni, suka jefar da shi waje.

13“Sai mai gonar inabin ya ce, ‘Me zan yi? Zan aiki ɗana da nake ƙauna, wataƙila za su girmama shi.’

14“Amma da ’yan hayan suka gan shi, sai suka tattauna zancen, suka ce, ‘Wannan shi ne magājin, mu kashe shi sa’an nan gādon zai zama namu!’ 15Sai suka fitar da shi waje, suka kashe shi.

“To, me mai gonar inabin zai yi da su? 16Zai zo ya karkashe masu hayan nan, ya ba wa waɗansu gonar inabin.”

Da mutanen suka ji wannan, sai suka ce, “Allah ya sawwaƙa!”

17Yesu ya zura musu ido ya ce, “To, mene ne ma’anar abin da aka rubuta cewa,

“ ‘Dutsen da magina suka ƙi,

shi ne kuwa ya zama dutsen kan ginin’20.17 Ko kuwa dutsen kusurwa20.17 Zab 118.22

18Duk wanda ya fāɗi a kan dutsen nan, zai kakkarye. Kuma in dutsen nan ya fāɗi a kan wani, zai murƙushe shi.”

19Malaman dokoki da manyan firistoci, suka nemi hanyar kama shi nan da nan, domin sun san cewa, ya yi wannan misali a kansu ne, amma suna jin tsoron mutane.

Biyan haraji ga Kaisar

(Mattiyu 22.15-22; Markus 12.13-17)

20Sai suka sa masa ido, suka aiki ’yan leƙen asiri, waɗanda suka nuna kamar su masu gaskiya ne, suna nufin su kama shi game da abin da zai faɗa, domin su ba da shi ga gwamna mai mulki, da mai iko. 21Sai ’yan leƙen asirin suka tambaye shi, suka ce, “Malam, mun sani kana faɗin, kuma kana koyar da abin da yake daidai, ba ka kuma nuna bambanci, amma kana koyar da hanyar Allah bisa ga gaskiya. 22Daidai ne mu biya haraji ga Kaisar, ko babu?”

23Ya gane makircinsu, sai ya ce musu, 24“Nuna mini dinari. Hoton wane ne, kuma rubutun wane ne a kai?”

Suka amsa, “Na Kaisar.”

25Sai ya ce musu, “Ku ba wa Kaisar abin da yake na Kaisar, ku kuma ba wa Allah abin da yake na Allah.”

26Ba su iya kama shi a kan abin da ya faɗa a fili ba. Amsarsa ya ba su mamaki, shi ya sa suka yi shiru.

Ba aure a tashin matattu

(Mattiyu 22.23-33; Markus 12.18-27)

27Waɗansu Sadukiyawa da suke cewa, ba tashin matattu, suka zo wurin Yesu da tambaya cewa, 28“Malam, Musa ya rubuta mana cewa, ‘In ɗan’uwan wani mutum ya mutu, ya bar mata amma ba ’ya’ya, dole mutumin ya aure gwauruwar, ya samo wa ɗan’uwansa ’ya’ya.’ 29To, an yi waɗansu ’yan’uwa bakwai. Na fari ya auri wata mace, ya mutu ba ’ya’ya. 30Na biyun, 31da na ukun suka aure ta. Haka nan dukansu bakwai suka mutu babu ’ya’ya. 32A ƙarshe, ita macen ma ta mutu. 33Shin, a tashin matattu, matar wa za tă zama? Tun da su bakwan nan, sun aure ta.”

34Yesu ya amsa ya ce, “Mutanen zamanin nan suna aure, suna kuma ba da aure, 35amma su waɗanda aka ga sun cancantar kasancewa a zamanin can, da kuma na tashin matattu, ba za su yi aure, ko su ba da aure ba. 36Kuma ba za su sāke mutuwa ba, gama su kamar mala’iku ne. Su ’ya’yan Allah ne, tun da su ’ya’yan tashin matattu ne. 37Amma bisa ga labari na bishiya nan, mai cin wuta da Musa ya gani a jeji, ko Musa ma, ya nuna cewa, matattu suna tashi. Gama ya kira Ubangiji, ‘Allah na Ibrahim, da Allah na Ishaku, da kuma Allah na Yaƙub.’ 38Shi ba Allah na matattu ba ne, amma na masu rai ne, gama a gare shi, duka na da rai.”

39Sai waɗansu malaman dokoki suka amsa suka ce, “Ka faɗi daidai, malam!” 40Kuma ba wanda ya sami ƙarfin halin yin masa waɗansu tambayoyi.

Kiristi ɗan wane ne?

(Mattiyu 22.41-46; Markus 12.35-37)

41Sai Yesu ya ce musu, “Yaya suke cewa, ‘Kiristi ɗan Dawuda ne?’ 42Dawuda da kansa ya faɗa a cikin Zabura,

“ ‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina,

“Zauna a hannun damana,

43sai na sa abokan gābanka

su zama matashin sawunka.” ’20.43 Zab 110.1

44Dawuda ya kira shi ‘Ubangiji.’ Ta, yaya zai zama ɗansa?”

(Mattiyu 23.1-36; Markus 12.38-40; Luka 11.37-54)

45Yayinda dukan mutane suna cikin sauraronsa, sai Yesu ya ce wa almajiransa, 46“Ku yi hankali da malaman dokoki. Sukan so sa manyan riguna suna zaga, suna sha’awan karɓan gaisuwa a wuraren kasuwanci, da kuma wuraren zama mafi daraja a majami’u, da wuraren bangirma a bukukkuwa. 47Suna mamaye gidajen gwauraye, kuma don burga, suna dogayen addu’o’i. Ga irin waɗannan mutane, za a yi musu hukunci mai tsanani sosai.”