הבשורה על-פי לוקס 16 – HHH & HCB

Habrit Hakhadasha/Haderekh

הבשורה על-פי לוקס 16:1-31

1ישוע סיפר לתלמידיו את המשל הבא: ”לעשיר אחד היה עובד שניהל את הונו. יום אחד הגיעו שמועות לאוזני העשיר שמנהל עסקיו בוגד בו ומבזבז את רכושו וכספו.

2”קרא אליו העשיר את המנהל ואמר: ’שמעתי שאתה מרמה אותי ומועל באמוני. הכן לי דו״ח על מצב העסקים, משום שאני עומד לפטר אותך‘.

3”מנהל העסקים חשב לעצמו: ’מה אעשה לאחר שמעבידי יפטר אותי? אין לי כוח לעבוד עבודה פיזית, ואילו לבקש נדבות זה לא בכבוד שלי. 4יש לי רעיון! אני יודע מה אעשה כדי שאנשים יאספו אותי אל בתיהם לאחר שיפטרו אותי‘.

5”הוא הזמין אליו כל אחד מהאנשים שהיו חייבים כסף לאדוניו. ’כמה אתה חייב לאדוני?‘ שאל את הראשון. 6’מאה חביות שמן‘, ענה בעל החוב. ’נכון. קח את שטר־החוב שלך, קרע אותו וכתוב שטר חדש על חמישים חביות בלבד!‘

7” ’וכמה אתה חייב לאדוני?‘ שאל מנהל העסקים את בעל החוב הבא. ’מאה שקי חיטה‘, השיב האיש. אמר לו מנהל העסקים: ’קח את השטר הזה וכתוב במקומו שטר התחייבות על שמונים שקים בלבד‘.

8”האיש העשיר התפעל מעורמתו של המנהל שלו, שהרי בני העולם הזה יותר פיקחים מבני האור. 9מוסר ההשכל הוא זה: השתמשו במשאבים החומריים שלכם כדי לעזור לאחרים ולהשקיע במערכות יחסים. כי כאשר רכושכם בעולם הזה יאזל לכם, חבריכם יקבלו אתכם בשמחה לביתכם הנצחי.

10”מי שמרמה בדבר פעוט ירמה בדבר גדול. מי שמוכיח את יושרו ונאמנותו בדבר פעוט יהיה ישר ונאמן גם בדברים גדולים. 11ואם אי־אפשר לסמוך עליכם ולהפקיד בידיכם עושר הבא מן העולם הזה, מי יפקיד בידיכם את העושר האמיתי הבא מן השמים? 12ואם אי־אפשר לסמוך עליכם במה שנוגע לרכושם של אחרים, מי ייתן לכם רכוש משלכם?

13”אינך יכול לשרת שני אדונים; אתה תשנא את האחד ותאהב את האחר, או להיפך – תהיה נאמן לאחד ותזלזל באחר. אינך יכול לעבוד את האלוהים ואת הכסף!“

14הפרושים אהבו מאוד את כספם ולכן לעגו לישוע.

15אולם ישוע אמר להם: ”בפני הציבור אתם מעמידים פני צדיקים תמימים, אבל אלוהים יודע היטב מה מתרחש בלבכם. העמדת הפנים שלכם רכשה לכם כבוד בעיני בני־אדם, אולם היא שנואה ומתועבת בעיני אלוהים.

16”התורה והנביאים התבשרו עד ימי יוחנן המטביל. מאז, בשורת מלכות האלוהים מוכרזת ואנשים מתאמצים להיכנס אליה. 17אולם נקל יותר שהשמים והארץ ייעלמו מאשר שפרט קטן בתורה יאבד מאמיתותו.

18”איש שמגרש את אשתו ומתחתן עם אחרת הוא נואף. גם מי שמתחתן עם גרושה הוא נואף.“

19”פעם היה איש עשיר,“ סיפר ישוע, ”שהתלבש בצורה מפוארת ובילה את ימיו בעונג, בשחצנות ובבזבוז. 20בשער ביתו המפואר שכב קבצן אחד שהיה מכוסה כולו פצעים. ’אלעזר‘ קראו לו. 21הוא השתוקק להשביע את רעבונו מהפירורים שנפלו משולחנו של העשיר, והכלבים היו באים ומלקקים את פצעיו. 22יום אחד מת אלעזר הקבצן, והמלאכים נשאוהו אל חיק אברהם אבינו. כעבור זמן־מה מת גם העשיר, 23אולם הוא נלקח אל הגיהינום, שם התענה עינויים גדולים. כשהרים את ראשו בכאב, ראה מרחוק את אלעזר בחיקו של אברהם.

24” ’אברהם, אבי‘, קרא העשיר, ’אנא, רחם עלי. שלח אלי את אלעזר כדי שיטבול את אצבעו במים ויקרר את לשוני, כי אני מתענה באש הנוראה הזאת‘.

25”אולם אברהם ענה לו: ’בני, אל תשכח שנהנית בחייך מכל טוב, ואילו אלעזר סבל עוני וחולי. עכשיו התהפך הגלגל – אלעזר מנוחם ואילו אתה מתענה. 26מלבד זאת, תהום גדולה מפרידה בינינו. איש מאיתנו אינו יכול לעבור אליכם ואיש מכם אינו יכול לעבור אלינו‘.

27‏-28” ’אם כך, אבי‘ התחנן העשיר, ’עשה לי טובה; שלח בבקשה את אלעזר אל בית אבי, כדי שיזהיר את חמשת אחי מפני המקום הנורא הזה‘.

29”אולם אברהם השיב לו: ’כתבי־הקודש הזהירו את אחיך פעמים רבות. אחיך יכולים לקרוא את דברי משה והנביאים בכל עת שירצו‘.

30” ’אני מכיר אותם היטב‘, אמר לו העשיר. ’הם לא יטרחו לקרוא את דברי הנביאים. אבל אם יבוא אליהם מישהו מן המתים הם יחזרו בתשובה‘.

31”אך אברהם השיב: ’אם הם לא הקשיבו למשה ולנביאים, הם לא יקשיבו גם למי שיקום מן המתים‘. “

Hausa Contemporary Bible

Luka 16:1-31

Misalin manaja mai wayo

1Yesu ya ce wa almajiransa, “An yi wani mai arziki wanda aka yi wa manajansa zargin yin banza da dukiyarsa. 2Sai ya kira manajan, ya tambaye shi, ‘Me nake ji haka a kanka? Ka kawo lissafin aikinka, domin ba za ka iya cin gaba da aikinka ba.’

3“Sai manajan ya ce cikin tunaninsa, ‘Maigidana zai kore ni daga aiki, me zan yi? Ba ni da ƙarfin noma, kuma ina jin kunyan yin bara. 4Na san abin da zan yi, don mutane su karɓe ni a gidajensu, bayan an kore ni daga aiki a nan.’

5“Sai ya kira kowane ɗaya da maigidansa yake bin bashi. Ya tambayi na farkon ya ce, ‘Nawa ne maigidana yake bin ka?’

6“Ya amsa ya ce, ‘Garwar mai na zaitun guda ɗari tara.’

“Manajan ya ce, ‘Ga takardarka, ka zauna maza ka mai da shi ɗari huɗu.’

7“Ya kuma tambayi na biyun, ‘Kai fa, nawa ne ake bin ka?’

“Sai ya amsa ya ce, ‘Buhunan alkama dubu.’

“Ya ce, ‘Ga takardarka, ka mai da shi ɗari takwas.’

8“Maigidan kuwa ya yabi manajan nan marar gaskiya saboda wayonsa. Gama ’yan duniyan nan suna da wayon yin hulɗa da junansu fiye da ’yan haske. 9Ina gaya muku, ku yi amfani da dukiya na wannan duniya, domin ku sami wa kanku abokai. Saboda bayan dukiyar ta ƙare, za a karɓe ku a wuraren zama da sun dawwama.

10“Duk wanda ana amincewa da shi cikin ƙaramin abu, ana kuma amincewa da shi cikin babba. Kuma duk marar gaskiya cikin ƙaramin abu, zai zama marar gaskiya cikin babba. 11In fa ku ba amintattu ne cikin tafiyar da dukiya ta wannan duniya ba, wa zai amince muku da dukiya ta gaskiya? 12In fa ku ba amintattu ne cikin tafiyar da dukiyar wani ba, wa zai ba ku dukiya naku, na kanku?

13“Babu wani bawa mai iya bauta wa iyayengiji biyu ba. Ko dai ya ƙi ɗaya, ya so ɗayan, ko kuwa ya dāge ga yi wa ɗaya bauta, sa’an nan ya rena ɗayan. Ba za ku iya ku bauta wa Allah tare da bauta wa Mammon (wato, Kuɗi) a lokaci ɗaya ba.”

(Mattiyu 11.12,13; 5.31,32; Markus 10.11,12)

14Da Farisiyawa masu son kuɗi suka ji wannan duka, sai suka yi wa Yesu tsaki. 15Ya ce musu, “Ku ne masu mai da kanku marasa laifi a gaban mutane, amma Allah ya san zuciyarku. Abu mai daraja a gaban mutane, abin ƙyama ne a gaban Allah.

Ƙarin koyarwa

16“An yi shelar Doka da Annabawa har zuwa lokacin Yohanna. Tun daga lokacin nan, bisharar mulkin Allah ne ake wa’azinta, kowa kuma yana ƙoƙarin kutsa kai ya shiga. 17Gama ta fi sauƙi sama da ƙasa su shuɗe, da a ce ɗigo guda ɗaya na rubutun, ya fita ya fāɗi daga cikin Doka.

18“Duk wanda ya saki matarsa ya auri wata mace, zina ne yake yi. Kuma mutumin da ya auri macen da aka sake, zina ne yake yi.

Mai arziki da Lazarus

19“An yi wani mutum mai arziki wanda yakan sa tufafi masu ruwan shunayya, da kuma na lallausan lilin, yana kuma cikin rayuwar jin daɗi kullum. 20A ƙofar gidansa kuma akan ajiye wani mai bara, mai suna Lazarus, wanda jikinsa duk gyambuna ne. 21Shi kuwa yakan yi marmarin cin abin da yakan fāɗi daga tebur na mai arzikin nan. Har karnuka ma sukan zo su lashe gyambunansa.

22“Ana nan, sai mai baran ya mutu, kuma mala’iku suka ɗauke shi zuwa gefen Ibrahim. Mai arzikin ma ya mutu, aka kuma binne shi. 23A cikin jahannama ta wuta, inda yana shan azaba, ya ɗaga kai ya hangi Ibrahim can nesa, da kuma Lazarus a gefensa. 24Sai ya yi masa kira ya ce, ‘Baba, Ibrahim, ka ji tausayina, ka aiki Lazarus ya sa ɗan yatsarsa a ruwa, ya ɗiga mini a harshe saboda in ji sanyi, domin ina shan azaba cikin wannan wuta.’

25“Amma Ibrahim ya ce, ‘Ka tuna fa ɗana, a lokacin da kake duniya, ka sami abubuwa masu kyau naka, Lazarus kuwa ya sami munanan abubuwa. Amma yanzu ya sami ta’aziyya a nan, kai kuwa kana shan azaba. 26Ban da wannan duka ma, tsakaninmu da kai, akwai wani babban rami da aka yi, yadda waɗanda suke son ƙetarewa daga nan zuwa wurinku, ba za su iya ba, kuma ba mai iya ƙetarewa daga wurinku zuwa wurinmu.’

27“Ya amsa ya ce, ‘To, ina roƙonka, ya uba, ka aiki Lazarus zuwa gidan mahaifina, 28gama ina da ’yan’uwana biyar maza. Bari yă ba su gargaɗi, don kada su ma su zo wurin nan mai azaba.’

29“Ibrahim ya amsa ya ce, ‘Suna da Musa da Annabawa, ai, sai su saurare su.’

30“Sai ya ce, ‘A’a, ya uba, Ibrahim, in dai wani ya tashi daga matattu ya je wurinsu, za su tuba.’

31“Amma ya ce masa, ‘In ba su saurari Musa da Annabawa ba, kai, ko da wani ya tashi daga matattu ma, ba za su saurare shi ba.’ ”