האיגרת אל-העברים 3 – HHH & HCB

Habrit Hakhadasha/Haderekh

האיגרת אל-העברים 3:1-19

1לכן, אחים יקרים, אשר אלוהים קרא לכם והקדיש אתכם לשירותו, ברצוני שתתבוננו אל ישוע המשיח שהוא שליח ה׳ והכוהן הגדול של אמונתנו. 2המשיח היה נאמן לאלוהים אשר מינהו לתפקיד הכוהן הגדול, כשם שמשה רבנו שרת בנאמנות בבית ה׳. 3אך כבודו של ישוע גדול מכבודו של משה, כשם שבנאי שבונה בית לתפארת זוכה לשבחים רבים יותר מהבית עצמו. 4אמנם לכל בית יש בנאי, אך בונה הכול הוא האלוהים.

5משה שרת את ה׳ בנאמנות בכל ענייני המשכן – שהוא בית אלוהים – אולם משה היה משרת בלבד, ותפקידו היה לרמוז על הדברים שאלוהים עמד לומר בעתיד. 6ואילו המשיח, בנו הנאמן של אלוהים, שולט באופן מוחלט על בית אלוהים. אנחנו, המאמינים, הננו בית אלוהים – בתנאי שנשמור על אומץ־לבנו עד הסוף ונשמח בתקוותנו.

7לכן עלינו לציית לרוח הקודש שמזהיר אותנו ואומר:3‏.7 ג 7 תהלים צה 7‏-11

”היום אם בקולו תשמעו,

8אל תקשו לבבכם כמריבה,

כיום מסה במדבר,

9אשר נסוני אבותיכם,

בחנוני גם ראו פעלי, 10ארבעים שנה“.

רוח הקודש ממשיך ואומר שאלוהים מאס בדור ההוא, שכן היו בו רשעים שלא קיימו את תורתו ולא הלכו בדרכיו. 11משום כך כעס עליהם אלוהים מאוד ונשבע שלא יכנסו לעולם אל מקום מנוחתו.

12לפיכך, אחים יקרים, בחנו את לבכם, כדי שלא יימצאו ביניכם רשעים וחסרי־אמונה שמסרבים לבטוח בה׳.

13הוכיחו זה את זה בכל יום, כל עוד יש אפשרות לכך, כדי שאיש מכם לא ירומה על־ידי החטא ולא יקשיח את לבו נגד אלוהים. 14שכן רק אם נישאר נאמנים עד הסוף, ונבטח בה׳ כמו שבטחנו בו לראשונה, נשתתף וניקח חלק בכל מה ששייך למשיח.

15לעולם אל תשכחו את האזהרה: ”היום אם בקולו תשמעו, אל תקשו לבבכם כמריבה!“

16במי מדובר? מי הם אלה אשר שמעו את דבר ה׳, אך רבו איתו וסרבו לציית לו? מדובר בבני־ישראל שיצאו ממצרים בהנהגת משה. 17ומי הכעיס את ה׳ במדבר במשך ארבעים שנה? אלה שחטאו וכתוצאה מכך מתו במדבר. 18ולמי נשבע ה׳ שלא ייכנסו אל ארץ ההבטחה? לסוררים אשר לא שמעו בקולו. 19ומדוע לא יכלו להיכנס? כי לא האמינו בה׳ ולא בטחו בו.

Hausa Contemporary Bible

Ibraniyawa 3:1-19

Yesu ya fi Musa

1Saboda haka, ’yan’uwa tsarkaka, waɗanda suke da rabo a kiran nan na sama, ku kafa tunaninku a kan Yesu, manzo da kuma babban firist wanda muke shaidawa. 2Ya yi aminci ga wanda ya naɗa shi, kamar yadda Musa ya yi aminci ga dukan gidan Allah. 3An ga Yesu ya cancanci girma fiye da Musa, kamar yadda mai ginin gida ya fi gidan daraja. 4Gama kowane gida yana da wanda ya gina shi, amma maginin dukan abu Allah ne. 5Musa ya yi aminci a matsayin bawa cikin dukan gidan Allah, yana ba da shaida a kan abubuwan da za a faɗa nan gaba. 6Amma Kiristi mai aminci ne kamar ɗa a gidan Allah. Mu kuwa gidansa ne, in muka tsaya gabanmu gadi da kuma begen da muke taƙama a kai.

Gargaɗi a kan rashin bangaskiya

7Kamar dai yadda Ruhu Mai Tsarki ya ce,

“Yau, in kuka ji muryarsa,

8kada ku taurare zukatanku,

yadda kuka yi a tawayen nan,

a lokacin gwaji a hamada,

9inda kakanninku suka gwada ni, suka kuma gwada ni,

ko da yake a cikin shekaru arba’in sun ga abin da na yi.

10Shi ya sa na yi fushi da wancan zamani,

na kuma ce, ‘Kullum zukatansu a karkace suke,

ba su kuma san hanyoyina ba.’

11Saboda haka na yi rantsuwa a cikin fushina,

‘Ba za su taɓa shiga hutuna ba.’ ”3.11 Zab 95.7-11

12Ku lura fa, ’yan’uwa, cewa kada waninku yă kasance da zuciya mai zunubi marar bangaskiya da takan juye daga bin Allah mai rai. 13Sai dai ku ƙarfafa juna kullum, muddin akwai lokacin da ana ce da shi Yau, don kada waninku yă zama mai taurin zuciya ta wurin ruɗun zunubi. 14Mu masu tarayya ne da Kiristi idan mun riƙe bangaskiyarmu da ƙarfi daga farko har zuwa ƙarshe. 15Kamar yadda aka faɗa cewa,

“Yau, in kuka ji muryarsa,

kada ku taurare zukatanku

kamar yadda kuka yi a tawayen nan.”3.15 Zab 95.7,8

16Su wane ne suka ji suka kuma yi tawaye? Ba su ne duk waɗanda Musa ya bi da su daga Masar ba? 17Da su wane ne kuwa ya yi fushi har shekaru arba’in? Ba da waɗanda suka yi zunubi, waɗanda suka mutu a hamada ba? 18Kuma ga su wane ne Allah ya rantse cewa ba za su taɓa shiga hutunsa ba, in ba ga marasa biyayyan nan ba? 19Saboda haka mun ga cewa ba su iya shiga ba, saboda rashin bangaskiyarsu ne.