האיגרת אל-העברים 1 – HHH & HCB

Habrit Hakhadasha/Haderekh

האיגרת אל-העברים 1:1-14

1לפני שנים רבות דיבר אלוהים אל אבותינו באמצעות הנביאים בדרכים שונות, וסיפר להם, שלב אחרי שלב, על תוכניותיו.

2אך עתה, באחרית הימים, דיבר אלינו אלוהים באמצעות בנו, אשר בידו הפקיד את הכול ועל־ידו ברא את העולם ואת כל אשר בו.

3בן־האלוהים מקרין את זוהר כבוד האלוהים; הוא צלם תכונותיו של אלוהים, ובכוח דברו הוא נושא את העולם כולו. לאחר שהקריב את עצמו למעננו, כדי לטהר אותנו מחטאינו, עלה בן האלוהים למרומים וישב לימין האלוהים. 4בזאת הוכיח שהוא בעל חשיבות גדולה מכל המלאכים, ואלוהים אישר עובדה זאת כשהעניק לו את השם: ”בן־אלוהים“ – שם שלא הוענק לאף מלאך!

5לאיזה מלאך אמר אלוהים אי־פעם:1‏.5 א 5 תהלים ב 7 ”בני אתה, אני היום ילדתיך“?, או1‏.5 א 5 שמ״ב ז 14 ”אני אהיה לו לאב והוא יהיה לי לבן“? 6כשהציג אלוהים לפני העולם את בנו בכורו, את ישוע המשיח, אמר:1‏.6 א 6 תהלים צז 7 ”השתחוו לו כל־מלאכי אלוהים“.

7ועל המלאכים אלוהים אומר:1‏.7 א 7 תהלים קד 4

”עושה מלאכיו רוחות,

משרתיו אש לוהט“.

8אך לבנו הוא אומר:1‏.8 א 8 תהלים מה 7‏-8

”כסאך, אלוהים, עולם ועד,

שבט מישר שבט מלכותך.

9אהבת צדק ותשנא רשע,

על כן משחך אלהים אלהיך

שמן ששון מחבריך“.

10גם במקום אחר אנו מוצאים רמז לעליונותו של הבן:1‏.10 א 10 תהלים קב 26‏-28

”אתה, אדוני, לפנים הארץ יסדת,

ומעשה ידיך שמים.

11המה יאבדו, ואתה תעמד;

וכולם כבגד יבלו.

12כלבוש תחליפם, ויחלפו.

ואתה הוא ושנותיך לא יתמו“.

13האם אמר אלוהים אי־פעם לאחד המלאכים את אשר אמר לבנו:1‏.13 א 13 תהלים קי 1

”שב לימיני עד אשית ‎ א‎וֹיְבֶיךָ הֲד‎וֹם לרגליך“?

14לא! כי המלאכים הם רק רוחות שרת, אשר נשלחו לעזור ולהשגיח על העתידים להיוושע.

Hausa Contemporary Bible

Ibraniyawa 1:1-14

1A dā Allah ya yi wa kakanni-kakanninmu magana ta bakin annabawa a lokuta dabam-dabam da kuma a hanyoyi iri-iri, 2amma a waɗannan kwanaki a ƙarshe ya yi magana da mu ta wurin Ɗansa, wanda ya naɗa magājin dukan abubuwa, wanda kuma ta wurinsa ya halicci duniya. 3Ɗan shi ne hasken ɗaukakar Allah, shi ne kuma ainihin kamanninsa, yana riƙe da dukan abubuwa ta wurin kalmarsa mai iko. Bayan ya yi tsarkakewa don zunubai, sai ya zauna a hannun daman Maɗaukaki a sama. 4Ta haka yake da fifiko a kan mala’iku kamar yadda sunan da ya gāda ya fi nasu fifiko.

Ɗan ya fi Mala’iku

5Gama ga wane daga cikin mala’ikun Allah ya taɓa cewa,

“Kai Ɗana ne;

yau na zama Uba a gare ka”1.5 Zab 2.7?

Ko kuwa,

“Zan zama Ubansa,

shi kuma zai zama Ɗana”1.5 2Sam 7.14; 1Tar 17.13?

6Haka kuma, sa’ad da Allah ya kawo ɗan farinsa a duniya ya ce,

“Bari dukan mala’ikun Allah su yi masa sujada.”

7Da yake magana game da mala’iku kuwa ya ce,

“Ya mai da mala’ikunsa iska,

bayinsa kuma harsunan wuta.”1.7 Zab 104.4

8Amma game da Ɗan ya ce,

“Kursiyinka, ya Allah, zai kasance har abada abadin,

adalci kuma zai zama sandan mulkinka.

9Ka ƙaunaci abin da yake daidai, ka kuma ƙi mugunta;

saboda haka Allah, Allahnka, ya ɗora ka a bisan abokan zamanka,

ta wurin shafan da ya yi maka da man farin ciki.”1.9 Zab 45.6,7

10Ya kuma ce,

“Tun da farko, ya Ubangiji, ka kafa tushen duniya,

sammai kuma aikin hannuwanka ne.

11Su za su hallaka, amma kai kana nan;

dukansu za su tsufa kamar riga.

12Za ka naɗe su kamar mayafi,

kamar riga za su sauya.

Amma kai ba za ka canja ba,

shekarunka kuma ba za su taɓa ƙarewa ba.”1.12 Zab 102.25-27

13Ga wane daga cikin mala’iku Allah ya taɓa cewa,

“Zauna a hannun damana,

sai na sa abokan gābanka

su zama matashin sawunka”1.13 Zab 110.1?

14Ashe, dukan mala’iku ba ruhohi masu hidima ba ne da aka aika don su yi wa waɗanda za su gāji ceto hidima?