אגרת פולוס השנייה אל-הקורנתים 5 – HHH & HCB

Habrit Hakhadasha/Haderekh

אגרת פולוס השנייה אל-הקורנתים 5:1-21

1אנו יודעים שכאשר משכננו הארצי ייהרס, כלומר כאשר נמות ונצא מגופנו הגשמי, יצפה לנו בשמים משכן נצחי מאת אלוהים, שאינו מעשה ידי אדם. 2מה עייפנו מגופנו הנוכחי! אנו נכספים ליום שבו נקבל גוף חדש מן השמים אשר נלבשהו כבגד, 3כדי שלא נהיה נשמות ללא גוף. 4כל עוד אנו בגופנו הגשמי, אנו נאנחים מתוך דיכאון ומועקה, אך איננו רוצים למות ולהיוותר ללא גוף. ברצוננו ללבוש את הגוף החדש, כך שהגוף בן התמותה יבלע על־ידי החיים. 5אלוהים הוא שהכין כל זאת למעננו, וכערבות לכך נתן לנו את רוח הקודש.

6עתה אנו מצפים בביטחון לגופנו הרוחני, כי אנו יודעים שכל עוד אנו שוכנים בגופנו הגשמי אנו רחוקים מן האדון. 7אנו יודעים שאלה דברי אמת מתוך אמונה, ולא ממראה עיניים. 8אנו כה בטוחים בדבר, עד כי אנו מעדיפים לצאת מן הגוף ולבוא הביתה אל האדון. 9משום כך אנו משתדלים למצוא־חן בעיניו בכל מעשינו, אם אנו בגופנו הגשמי ואם בשמים. 10כי כולנו עתידים לעמוד לפני המשיח ולהישפט על־ידו. כל אחד יקבל את המגיע לו על־פי מעשיו הטובים או הרעים בחייו הגשמיים.

11מתוך הכרת יראת ה׳ אנו משתדלים להביא אנשים לידי אמונה בו. מניעינו הטהורים בעניין זה גלויים לפני אלוהים, ואני מקווה שגם לפני מצפונכם! 12האם אנו שוב טופחים לעצמנו על השכם? לא! אני נותן לכם הזדמנות להתגאות בנו לפי אלה המתפארים בהופעתם החיצונית ובדרך הטפתם, במקום בטוהר לבם. אנחנו לפחות ישרים ומניעינו טהורים. 13האם יצאנו מדעתנו? אם כן, הרי זה כדי להביא כבוד לאלוהים. אך אם דעתנו שפויה, הרי זה למענכם. 14איננו עושים דבר למען עצמנו, שכן אהבת המשיח מכוונת עתה את מעשינו. הואיל ואנו מאמינים שהמשיח מת בעד כולנו, עלינו להאמין שמתנו לגבי החיים שנהגנו לחיות. 15הוא מת למען כולם כדי שכל החיים – אשר קיבלו ממנו חיי נצח – שוב לא יחיו למען עצמם, אלא למען המשיח אשר מת וקם לתחייה בעדם.

16לכן חדלו לשפוט את המאמינים על־פי חיצוניותם או על־פי דעתם של הלא־מאמינים. פעם שגיתי ושפטתי את המשיח על־פי קנה מידה אנושי, אך איני עושה זאת שוב. 17המאמין במשיח נעשה בריאה חדשה; שוב אין הוא אותו אדם כמקודם, שכן יש בו עתה חיים חדשים. 18כל הדברים החדשים האלה הינם מאת האלוהים אשר השיבנו לעצמו בזכות קורבנו של המשיח. אלוהים העניק לנו את הזכות לעודד אחרים לשוב אליו, 19ולבשר להם שהוא מקרב אליו את כל בני־האדם באמצעות המשיח, ושוב אין הוא זוכר להם את חטאיהם. זוהי הבשורה הנפלאה שמסר לנו לבשר לאחרים.

20לפיכך שגרירי המשיח אנחנו, ואלוהים מזהיר אתכם באמצעותנו. על כן אנו מתחננים לפניכם בשם המשיח: אנא, היענו לאהבתו והתרצו לאלוהים. 21למרות שהמשיח היה ללא חטא, אלוהים שם בו את חטאינו, ואחר כך שם בנו את צדקת אלוהים.5‏.21 ה 21 או: אם כי המשיח היה ללא חטא, אלוהים עשהו לחטאה בעדנו, כדי שנלבש את צדקת אלוהים בו.

Hausa Contemporary Bible

2 Korintiyawa 5:1-21

Wurin zamanmu a sama

1Yanzu mun san cewa in an hallaka tentin duniyan nan da muke ciki, muna da wani gini daga Allah, madawwamin gida a sama, wanda ba da hannuwan mutum ne suka gina shi ba. 2Kafin nan muna nishi, da marmari a yi mana sutura da gidanmu na sama, 3don sa’ad da aka yi mana sutura, ba za a same mu tsirara ba. 4Sa’ad da muke zaune a cikin jikin nan na duniya, nishi muke domin matsuwar da muke sha, ba domin muna so mu rabu da jikinmu na wannan duniya ba ne, sai dai don so muke yi a suturta mu da na Sama, domin mai rai ya shafe mai mutuwa. 5Allah ne ya yi mu domin wannan, ya kuma ba mu Ruhu a matsayin abin ajiya, yana kuma tabbatar da abin da zai zo nan gaba.

6Saboda haka, kullum muna da tabbaci mun kuma san cewa, muddin muna a duniya cikin jikin nan, ana raba mu da Ubangiji. 7Rayuwa bangaskiya muke, ba ta ganin ido ba. 8Ina cewa muna da tabbaci, za mu fi so mu rabu da jikin nan, mu kuma kasance a sama tare da Ubangiji. 9Saboda haka, niyyarmu ita ce, mu gamshe shi, ko muna a duniya cikin jikin nan, ko ba mu nan. 10Gama dole dukanmu mu bayyana a gaban kujerar shari’ar Kiristi, domin kowannenmu yă karɓi ladan aikin da ya yi a wannan jiki, ko mai kyau ne ko marar kyau.

Hidimar sulhuntawa

11To, da yake mun san ko mene tsoron Ubangiji yake, muna ƙoƙari mu rinjaye mutane. Yadda muke kuwa, yana sane a sarari ga Allah, ina kuma fata yana nan a sarari a lamirinku. 12Ba ƙoƙari muke mu yabe kanmu a gare ku ba ne, sai dai muna ba ku damar yin taƙama da mu ne, don ku sami amsar da za ku ba wa waɗanda suke taƙama da abin da ake gani ne, a maimakon abin da yake cikin zuciya. 13In hankalinmu a taɓe yake, ai, saboda Allah ne, in kuwa cikin hankalinmu muke, ai, saboda ku ne. 14Ƙaunar Kiristi a gare mu, ita take mallakarmu, saboda haka mun tabbata, da yake wani ya mutu saboda dukan mutane, ashe kuwa, mutuwarsu ce dukansu. 15Ya kuwa mutu ne saboda dukan mutane, domin kada waɗanda suke rayuwa kada su yi zaman ganin dama a nan gaba, sai dai su yi zaman wannan da ya mutu saboda su, aka kuma tashe shi saboda su.

16Saboda haka, daga yanzu zuwa nan gaba, ba mu ƙara ɗaukan wani mutum bisa ga ganin duniya ba. Ko da yake a dā, mun ɗauki Kiristi haka, amma yanzu mun daina yin haka. 17Saboda haka, duk wanda yake cikin Kiristi, sabuwar halitta ce, tsohon al’amari ya shuɗe, sabon ya zo! 18Duk wannan kuwa daga Allah ne, wanda ya sulhunta mu da kansa ta wurin Kiristi, ya kuma ba mu hidimar sulhu, 19wato, Allah ya sulhunta duniya zuwa kansa ta wurin Kiristi, ba ya lissafta zunuban mutane a kansu. Ya kuma danƙa mana saƙon sulhu. 20Saboda haka, mu jakadu ne na Kiristi, sai ka ce Allah kansa yake magana ta wurinmu. Muna roƙonku a madadin Kiristi. Ku sulhuntu da Allah. 21Shi da bai san zunubi ba, Allah ya mai da shi kamar hadayar zunubi saboda mu, domin mu sami adalcin Allah ta wurinsa.