אגרת פולוס השליח אל-הרומיים 3 – HHH & HCB

Habrit Hakhadasha/Haderekh

אגרת פולוס השליח אל-הרומיים 3:1-31

1אם כן, מהו יתרונו של היהודי? ומה יתרונה של המילה? 2יש יתרון רב בכל דרך.

ראשית כל, אלוהים הפקיד את דברו הכתוב בידי היהודים. 3אמנם חלק מהם לא האמין, אך האם אתם חושבים כי משום שהיהודים הפרו את הבטחתם לאלוהים, יפר אלוהים את הבטחותיו להם? 4חלילה! גם אם כל בני האדם משקרים, אלוהים נאמן ודובר אמת! הרי כתוב בתהלים שדברי אלוהים הם דברי אמת, ומשפטו תמיד משפט צדק.3‏.4 ג 4 כלשונו: למען תצדק בדבריך, תזכה בשפטיך. תהלים נא 6

5אך אם הרשעות שלנו מבליטה ומדגישה את טובו של ה׳, האם נאמר שאלוהים גורם לנו עוול בהענישו אותנו? (יש אנשים החושבים כך!)

6חלילה! אם אלוהים יתעלם מחטא, כיצד יוכל לשפוט את העולם? 7אנו כאילו אומרים, שאם על־ידי השקרים שלנו יוצאת אמת אלוהים לאור וגדל כבודו, מדוע עלינו להישפט כחוטאים? 8אם־כך, מדוע שלא נרבה לעשות מעשים רעים כדי שתצא מהם טובה? (שונאינו העלילו עלינו שכך אמרנו!) אמרו אתם, האין זה צודק להרשיע ולהעניש את אלה האומרים זאת?

9אם כן, האם היהודים טובים מהגויים? כלל לא. כבר הוכחנו שכל בני־האדם חוטאים – יהודים וגויים ללא הבדל. 10כפי שכתוב בתהלים3‏.10 ג 10 ראה תהלים נג, קמ, י, ישעיעהו נט, תהלים לו

”אין עושה טוב, אין גם אחד.

אין אף צדיק!

11אין משכיל, אין דורש את אלוהים;

12הכול סר3‏.12 ג 12 כלשונו: כולו סג יחדיו נאלחו.

אין עושה טוב, אין גם אחד.

13גרונם כקבר פתוח,

פיהם מלוכלך ומלא שקר

ולשונם נוטפת ארס.

14כן, הם מנבלים את פיהם,

15צמאי דם וחמי מזג.

16לכל מקום שהם הולכים

הם מותירים אחריהם סבל וצער.

17הם מעולם לא התנסו בתחושת השלום

והשלווה שאלוהים לבדו מעניק.

18אין הם מקדישים לאלוהים כל מחשבה,

ולא אכפת להם מה הוא חושב עליהם.“

19אנחנו יודעים כי דברי התורה מכוונים אל אלה הכפופים לה – היהודים – ואלוהים ישפוט ויעניש אותם, שכן עליהם לשמור את מצוותיו ולא להתנהג בצורה כזאת. לאיש מהם אין תירוץ! למעשה, העולם כולו עומד אשם לפני אלוהים. 20שהרי איש לא יצדק לפני אלוהים בזכות קיום התורה, מכיוון שחוקי התורה מצביעים על חטאינו ומראים לנו שאנו חוטאים. 21עתה נתגלה האופן שבו מצדיק ה׳ את האדם ללא התורה, אם כי התורה והנביאים כבר העידו על כך. 22צידוק זה ניתן לכל המאמינים בישוע המשיח, ללא הפליה. 23כי כל בני־האדם חטאו, וכולם חסרי כבוד אלוהים. 24בכל זאת, אלוהים הצדיק אותנו בחסדו חינם, על־ידי קורבנו של ישוע המשיח שהוקרב למעננו.

25אלוהים שלח את המשיח לשאת את העונש על חטאינו, כדי שעל־ידי אמונה בדמו, הוא יהיה כפרתנו – כלומר, יכפר על חטאינו. וכל זאת כדי להראות לנו את צדקתו, לאחר שברחמיו הרבים מחק את חטאי העבר. 26במעשה זה רצה אלוהים לגלות לנו את צדקתו – את סליחתו לחוטאים – ולהוכיח כי הוא עצמו צדיק, וכי הוא מצדיק את כל המאמין בישוע המשיח בנו.

27ובכן, האם יש למישהו סיבה להתגאות? ודאי שלא. מדוע? משום שאלוהים זיכה והצדיק אותנו בזכות קרבנו של המשיח ואמונתנו בו, ולא בזכות מעשינו הטובים. 28לפיכך אנו מסיקים שאדם נצדק לפני אלוהים על־ידי אמונתו בישוע המשיח בן־האלוהים, ולא על־ידי הישגיו בקיום מצוות התורה.

29החושבים אתם שאלוהים הוא אלוהי היהודים בלבד, ורק אותם הוא מושיע? ודאי שלא! אלוהים הוא גם אלוהי הגויים. 30ומכיוון שאלוהי היהודים הוא גם אלוהי הגויים, הוא מצדיק את כולנו על־ידי האמונה. 31האם בהדגישנו את חשיבות האמונה מבטלים אנו את התורה? חס וחלילה! למעשה אנחנו מקיימים אותה – דבר האפשרי רק על־ידי אמונה במשיח.

Hausa Contemporary Bible

Romawa 3:1-31

Amincin Allah

1To, mece ce ribar zama mutumin Yahuda, ko kuwa mene ne amfanin kaciya? 2Akwai riba ƙwarai ta kowace hanya! Da farko dai, su ne aka danƙa wa kalmomin nan na Allah.

3Amma a ce waɗansu ba su da bangaskiya fa? Rashin bangaskiyarsu nan zai shafe amincin Allah? 4Ko kaɗan! Bari Allah yă zama mai gaskiya, kowane mutum kuma yă zama maƙaryaci. Kamar yadda yake a rubuce cewa,

“Gama a tabbatar kana da gaskiya, sa’ad da ka yi magana,

ka kuma yi nasara sa’ad da ka yi shari’a.”3.4 Zab 51.4

5Amma in rashin adalcinmu ya bayyana adalcin Allah a fili, me za mu ce ke nan? Za mu ce Allah ya yi rashin adalci ke nan da ya saukar da fushinsa a kanmu? (Ina magana kamar yadda mutum zai yi ne.) 6Sam, ko kusa! Da a ce haka ne, ta yaya Allah zai shari’anta duniya? 7Wani zai iya ce, “In a dalilin ƙaryata, gaskiyar Allah ta ƙara bayyana, har aka ƙara ɗaukaka shi, to, ta yaya zan zama mai zunubi, in ƙaryata tana kawo ɗaukaka ga Allah?” 8In haka ne, “Ba sai mu yi ta yin mugunta don yă zama hanyar samun nagarta ba”? Kamar yadda masu baƙar magana game da mu suna cewa wai haka muke faɗa. Tabbatacce za a hukunta irin waɗannan da hukuncin da ya dace da su.

Babu mai adalci

9To, me za mu ce ke nan? Mun fi su ke nan? Ina, ko kaɗan! Mun riga mun zartar cewa da Yahudawa da Al’ummai duk suna a ƙarƙarshin zunubi. 10Kamar yadda yake a rubuce cewa,

“Babu wani mai adalci, babu ko ɗaya;

11babu wani mai fahimta,

babu wani mai neman Allah.

12Duk sun kauce gaba ɗaya,

sun zama marasa amfani;

babu wani mai aikata nagarta,

babu ko ɗaya.”3.12 Zab 14.1-3; Zab 53.1-3; M Had 7.20

13“Maƙogwaronsu kamar buɗaɗɗun kaburbura ne,

harsunansu suna yin ƙarya.”3.13 Zab 5.9

“Dafin mugun maciji yana a leɓunansu.”3.13 Zab 140.3

14“Bakunansu sun cike da la’ana da ɗacin rai.”3.14 Zab 10.7

15“Ƙafafunsu suna saurin kai su zuwa ga zub da jini;

16hallaka da baƙin ciki suna ko’ina a hanyoyinsu,

17ba su kuma san hanyar salama ba.”3.17 Ish 59.7,8

18“Babu tsoron Allah a idanunsu.”3.18 Zab 36.1

19Yanzu mun san cewa dukan abin da doka ta ce, tana magana ne ga waɗanda suke ƙarƙarshin doka, saboda a rufe kowane baki; dukan duniya kuma ta ba da lissafin kanta a gaban Allah. 20Saboda haka babu wanda Allah zai ce da shi mai adalci ta wurin kiyaye doka kawai; a maimako, ta wurin doka ne muke sane da zunubi.

Adalci ta wurin bangaskiya

21Amma yanzu an bayyana wani adalci daga Allah, wannan adalcin bai danganta ga doka ba, Doka da Annabawa suna ba da shaida game da wannan adalci. 22Wannan adalcin Allah yana zuwa ta wurin bangaskiya a cikin Yesu Kiristi ga dukan waɗanda suka ba da gaskiya ne. Ba bambanci, 23gama duka sun yi zunubi suka kuma kāsa ga ɗaukakar Allah, 24an kuma kuɓutar da su kyauta ta wurin alherinsa bisa ga aikin fansar da ya zo ta wurin Yesu Kiristi. 25Allah ya miƙa Yesu Kiristi a matsayin hadayar kafara, ta wurin bangaskiya cikin jininsa. Ya yi haka domin yă nuna adalcinsa, domin a cikin haƙurinsa bai hukunta zunuban da aka aikata a dā ba 26ya yi haka domin yă nuna adalcinsa a wannan lokaci, saboda yă zama mai adalci da mai kuɓutar da waɗanda suke ba da gaskiya a cikin Yesu.

27To, me za mu yi taƙama a kai? Babu wani abin da zamu yi taƙama a kai. A kan wace ƙa’ida ce za mu yi taƙama? Ta hanyar bin doka ne? A’a, sai dai ta wurin bangaskiya. 28Gama mun tsaya a kan cewa ta wurin bangaskiya ne ake kuɓutar da mutum, ba ta wurin kiyaye doka ba. 29Allah ɗin, Allahn Yahudawa ne kaɗai? Shi ba Allahn Al’ummai ba ne? I, shi Allahn Al’ummai ne ma, 30da yake Allah ɗaya ne kaɗai, shi kuma zai kuɓutar da masu kaciya bisa ga bangaskiya da kuma marasa kaciya ta wurin wannan bangaskiya ɗin. 31To, za mu soke dokar saboda wannan bangaskiyar ne? Ko kaɗan! A maimako, sai ma tabbatar da ita muke yi.