אגרת פולוס השליח אל האפסיים 2 – HHH & HCB

Habrit Hakhadasha/Haderekh

אגרת פולוס השליח אל האפסיים 2:1-22

1פעם הייתם מתים באופן רוחני; הייתם תחת קללת האל בגלל מעשיכם הרעים. 2חייתם לפי דרך־החיים של העולם הזה ושמעתם לקול השטן, שהוא השליט הרשע של הרוחות הרעות, והפועל עדיין בכל כוחו באנשים המורדים בה׳. 3כולנו חיינו בעבר בצורה כזאת. אורח־חיינו ביטא את רוע לבנו וכניעתנו לתשוקותינו ותאוותינו. נולדנו בעלי טבע מושחת, והיינו תחת זעם אלוהים כשאר בני־האדם.

4אבל אלוהים הוא אב מלא רחמים! הוא אהב אותנו כל־כך, 5עד כי למרות שהיינו מתים (באופן רוחני) ואשמים בעיניו בגלל חטאינו, הוא החזיר אותנו לחיים כשהקים לתחייה את המשיח – זכרו שנושענו רק בזכות חסדו הרב – 6והעלה אותנו מהקבר עם המשיח, כדי שנשב איתו במרומים. 7כך הוא מראה לכל הדורות הבאים את רוחב־לבו, טובו וחסדו הנפלא, שביטא כלפינו בישוע המשיח.

8נושעתם בזכות חסדו וטוב־לבו, על־ידי אמונתכם במשיח. כל זאת אינה שלכם; זוהי מתנתו של אלוהים, ואין היא תלויה בשום מעשה שעשיתם. 9איננו יכולים להתפאר בישועה זאת, שכן איש מאיתנו לא הרוויח אותה! אלוהים נתן לנו את הישועה הזאת במתנה. 10אלוהים עצמו עשה אותנו כפי שאנחנו עכשיו; הוא בחר בנו בישוע המשיח כדי שנעשה מעשים טובים, לפי תוכניתו מקדם.

11אל תשכחו שנולדתם ”ערלים“, ואלה אשר נימולו בידי אדם הם כינו אתכם ”ערלים“. 12באותה עת הייתם רחוקים מהמשיח, ונחותים מעם ישראל בחיר האלוהים; לא הייתה לכם כל זכות לבריתות ההבטחה, לא הייתה לכם תקווה ולא היה לכם אל.

13אבל עכשיו אתם שייכים לישוע המשיח, ולמרות שפעם הייתם רחוקים מאלוהים, כעת אתם קרובים אליו בזכות דמו של המשיח שנשפך למענכם. 14כי המשיח עצמו הוא שלומנו; הוא השכין שלום בינינו היהודים לביניכם הגויים, כשהרס את המחיצה בינינו ועשה משנינו אחד. 15על־ידי מותו שם המשיח קץ לשנאה ולאיבה שהייתה בינינו – איבה שנבעה מכך שחוקי התורה היו לטובת היהודים ולא כללו את הגויים – כי המשיח מת כדי לבטל את שיטת חוקי התורה. ואז הוא לקח את שתי הקבוצות שהתנגדו זו לזו ועשה מהן גוף אחד. כך הוא מיזג אותנו יחדיו ויצר מאיתנו אדם אחד חדש, וכך עשה שלום. 16כאיברים של גוף אחד, נעלמה האיבה שהייתה בינינו, כי המשיח שם קץ לאיבה המתמדת בינינו וריצה אותנו לאלוהים בהקריבו את עצמו על הצלב. 17ואז הוא בישר את בשורת השלום לכם, הגויים, שהייתם רחוקים ממנו, ולנו, היהודים, שהיינו קרובים. 18עתה באמצעותו ובזכותו יכולים כולנו, יהודים וגויים, לבוא אל אלוהים האב בעזרת רוח הקודש.

19אם כן, עתה אינכם זרים ונחותים, אלא בני־משפחתו של אלוהים ואזרחים בממלכת אלוהים, יחד עם כל המאמינים האחרים. 20אתם בנויים על היסודות שהניחו השליחים והנביאים, וישוע המשיח עצמו הוא אבן הפינה. 21אנחנו, המאמינים, מחוברים אל המשיח ואיש אל רעהו בהתאמה, וכולנו מהווים היכל קודש לה׳. 22גם אתם מחוברים אל המשיח ואיש אל רעהו, ומהווים משכן לרוח הקודש של אלוהים.

Hausa Contemporary Bible

Afisawa 2:1-22

An raya ku a cikin Kiristi

1Ku kam, a dā ku matattu ne saboda laifofinku da kuma zunubanku. 2Kun yi rayuwa kamar yadda sauran mutanen duniya suke yi, cike da zunubi, kuna biyayya ga sarki masu ikon sarari sama, wato, ruhun nan da yanzu yake aiki a cikin masu ƙin biyayya ga Allah. 3Dukanmu a dā mun yi irin rayuwan nan a cikinsu, muna bin kwaɗayi da sha’awace-sha’awacen jikunanmu da tunaninmu. Kamar sauran mutane, mun cancanci fushin Allah. 4Amma saboda yawan ƙaunar da yake mana, Allah, wanda yake mai yawan jinƙai, 5ya ba mu rai sa’ad da ya tashe Kiristi daga matattu. Ta wurin alherin Allah ne aka cece ku. 6Allah ya tashe mu tare da Kiristi, ya kuma ba mu wurin zama tare da shi a cikin mulkin samaniya. 7Allah ya yi haka domin a tsararraki masu zuwa yă nuna yalwar alherinsa da ya wuce misali, an bayyana alheransa da ya yi mana ta wurin Kiristi Yesu. 8Allah ya cece ku ta wurin alheri sa’ad da kuka ba da gaskiya. Wannan kuwa ba yinku ba ne, kyauta ce daga Allah. 9Ba kuwa saboda aikin lada ba, don kada wani yă ɗaga kai. 10Ai, mu aikinsa ne, an sāke halittarmu a cikin Kiristi Yesu musamman domin mu yi kyawawan ayyuka, waɗanda Allah ya tanadar mana tun da fari, mu yi.

An sulhunta Yahudawa da al’ummai su zama ɗaya ta wurin Kiristi

11Saboda haka, ku tuna dā ku Al’ummai ne bisa ga haihuwa, waɗanda kuma ake kira masu “kaciya” sukan kira ku “marasa kaciya” (ga shi kuwa, kaciyar nan ta jiki ce, wadda ake yi da hannu). 12Ku kuma tuna a lokacin ba ku san Kiristi ba. A ware kuke daga mutanen Isra’ila, ba ku kuma da dangantaka da alkawaran da Allah ya yi da su. Kun yi zama a duniyan nan babu bege kuma babu Allah. 13Amma yanzu a cikin Kiristi Yesu, ku da dā kuke can da nesa an kawo ku kusa ta wurin jinin Kiristi.

14Gama shi kansa shi ne salamarmu, shi ne ya kawo ƙungiyoyi biyu suka zama ɗaya, ya kuma rushe katangan nan ta ƙiyayya wadda ta raba mu. 15Kiristi ya ba da jikinsa don yă kawar da doka da dukan umarnanta da kuma ƙa’idodinta. Ya yi haka domin yă halicci sabuwar zuriya daga zuriyoyin nan biyu. Ta haka kuma ya kawo salama tsakaninsu. 16A kan gicciye, Kiristi ya kawar da ƙiyayyar da take tsakaninmu da juna. Ya kuma kawo sulhu tsakaninmu da Allah. 17Ya zo ya yi muku wa’azin salama; ku da kuke nesa da shi, ya kuma yi wa waɗanda suke kusa. 18Gama ta wurinsa dukanmu za mu iya zuwa gun Uba ta wurin Ruhu guda.

19Don haka, yanzu ku ba baƙi ba ne, ku kuma ba bare ba ne. Ku ’yan ƙasa ne tare da mutanen Allah, iyalin gidan Allah kuma. 20Ku gini ne wanda manzanni da annabawa suke tushensa, Kiristi kuma shi ne dutse mafi muhimmanci na ginin. 21Ta wurinsa ne dukan ginin yake a haɗe, shi ne kuma yake sa ginin yă yi girma, yă zama haikali mai tsarki domin Ubangiji. 22Ku ma sashe ne na wannan ginin da Kiristi ya yi inda Allah yake zaune ta wurin Ruhunsa.