אגרת יהודה 1 – HHH & HCB

Habrit Hakhadasha/Haderekh

אגרת יהודה 1:1-25

1אל המאמינים המשיחיים באשר הם, בחירי אלוהים ואהוביו.

מאת יהודה, עבדו של ישוע המשיח ואחיו של יעקב.

2יהי רצון שיעניק לכם אלוהים שפע של אהבה, שלום ורחמים.

3ידידי היקרים, התכוונתי לכתוב לכם על הישועה שנתן לנו אלוהים, אך אני נאלץ לכתוב לכם על נושא אחר לגמרי. ברצוני לעודד אתכם להגן באומץ על האמונה שנתן אלוהים לאוהביו, אחת ולתמיד. 4אני אומר דברים אלה משום שמורי שקר אחדים הסתננו לחברתכם, שטוענים כי לאחר שאנו באים לאמונה באלוהים ובמשיח, מותר לנו לעשות ככל שעולה על רוחנו וה׳ לא יעניש אותנו! אני מזהיר אתכם מפניהם; דינם של הרשעים האלה כבר נחרץ לפני זמן רב, שכן הם מתכחשים לאדוננו היחיד ישוע המשיח.

5תשובתי למורי השקר האלה היא: אל תשכחו את העובדה הידועה לכם היטב, שה׳ הציל את עם־ישראל מידי המצרים, אך לאחר מכן השמיד את כל אלה שלא האמינו בו. 6אני מזכיר לכם גם את המלאכים שלא הסתפקו בסמכות שנתן להם אלוהים. הם מרדו באלוהים ובחרו בחיי חטא, ומשום כך הוא כבל אותם בשרשראות, ועתה הם מחכים בחשכה ליום־הדין. 7אל תשכחו את סדום ועמורה ואת הערים השכנות, שהיו מלאות מעשי תועבה, שחיתות מוסרית ופריצות. כל הערים האלה נשרפו ונחרבו, והן משמשות לקח ואזהרה עבורנו שה׳ מעניש את הרשעים באש הגיהינום.

8אבל למורי השקר האלה כלל לא אכפת! הם ממשיכים לחיות חיים לא־מוסריים, עושים מעשי שחיתות למיניהם, בזים לשלטונות ולועגים לרשויות הרוחניות העליונות. 9כאשר מיכאל שר המלאכים התווכח עם השטן על גופתו של משה רבנו, הוא לא העז להאשים את השטן ואף לא לעג לו. מיכאל פשוט אמר: ”יגער בך אלוהים.“ 10אבל אנשים אלה מקללים ומזלזלים בכל דבר שאינם מבינים. הם מתנהגים כמו חיות – עושים מה שעולה על רוחם, וכך מביאים אסון על עצמם.

11אוי להם! הם הולכים בעקבות קין אשר רצח את אחיו; הם מוכנים לעשות כל דבר תמורת בצע כסף כמו בלעם; הם הימרו את פי ה׳ כמו קורח, ועל כן קללתו רובצת גם עליהם.

12רשעים אלה מקלקלים את החגיגות הנעימות שלכם בקהילה, שותים וזוללים בלי להתחשב באחרים. הם דומים לעננים שמרחפים מעל אדמה צמאה בלי שיוכלו להשקותה; מבטיחים הרבה ואינם מקיימים דבר. הם דומים לעצי־פרי שאינם נותנים פרי בעונת הקטיף, והם מתים לא רק משום שאין להם פרי, אלא גם משום שנעקרו מהשורשים כדי להישרף באש. 13אנשים אלה משאירים אחריהם תמיד רק בושה וחרפה, כמו הרפש שפולטים גלי הים לחוף. בכל מקום שהם עוברים בו הם מבריקים ונוצצים כמו כוכבים, אך אלוהים הכין בשבילם חשכת עולם!

14חנוך, שחי שבעה דורות אחרי האדם הראשון, ידע על אנשים אלה ואף אמר עליהם: ”הנה בא ה׳ עם מיליוני קדושיו, 15כדי לשפוט את כל העולם וכדי להרשיע את הרשעים האלה. במשפט זה יוכיח אלוהים את כל מעשיהם המושחתים, ואת כל הדברים הנוראים שאמרו עליו.“ 16רשעים אלה לעולם אינם שמחים בחלקם, אלא תמיד מתלוננים, עושים מעשים רעים לפי תאוות לבם ואוהבים להתגאות ולהתפאר! אם הם חולקים כבוד למישהו, הרי זה משום שברצונם להשיג ממנו משהו.

17ידידים יקרים, זכרו מה שאמרו לנו שליחי אדוננו ישוע המשיח: 18”בימים האחרונים יופיעו אנשים ציניים ורשעים שמטרתם היחידה בחיים היא להשתעשע במעשים רעים ומתועבים.“ 19אנשים אלה מסכסכים, גורמים לוויכוחים ואוהבים את השחיתות. רוח הקודש אינו שוכן בהם.

20אבל אתם, אחים יקרים, חזקו את אמונתכם ואת חייכם הרוחניים והתפללו בעזרת רוח הקודש.

21הישמרו לכם! אל תעשו דבר שעלול להרחיקכם מאהבת האלוהים ומברכתו. חכו בסבלנות לחיי הנצח שעומד האדון ישוע לתת לכם ברוב רחמיו. 22השתדלו לעזור למתנגדיכם, והתנהגו ברחמים עם אלה שמהססים באמונתם. 23הצילו אותם מהאש, ואילו עם האחרים התנהגו באהבה וברחמים, אך היזהרו שלא תתפתו בעצמכם לחטוא כמותם. שנאו בהם כל דבר שמסמן חטא.

24‏-25כל התהילה והפאר לאלוהינו האחד, שמושיע אותנו על־ידי ישוע המשיח אדוננו. כל הכבוד, התפארת, הגבורה והסמכות שייכים לו מעולם ועד עולם! זהו האלוהים שיכול לשמור אתכם מכישלונות ומכשולים, ולהעמידכם לנוכח כבודו, בששון ושמחה, מושלמים וללא דופי. – אמן.

Hausa Contemporary Bible

Yahuda 1:1-25

1Yahuda, bawan Yesu Kiristi, ɗan’uwan Yaƙub,

Zuwa ga waɗanda aka kira, waɗanda Allah Uba yake ƙauna, waɗanda kuma Yesu Kiristi ya kiyaye.

2Jinƙai, salama da kuma ƙauna, su kasance tare da ku a yalwace.

Zunubi da hallakar marasa tsoron Allah

3Abokaina ƙaunatattu, ko da yake na yi marmari ƙwarai in rubuta muku game da ceton nan namu, sai na ga ya dace in rubuta, in gargaɗe ku ku tsaya da ƙarfi cikin bangaskiya wadda aka danƙa wa mutane masu tsarki na Allah sau ɗaya tak. 4Na faɗa haka ne domin waɗansu mutanen da aka rubuta hukuncinsu tun dā sun shiga cikinku a ɓoye. Su fa marasa tsoron Allah ne. Su ne waɗanda suka mai da alherin Allahnmu ya zama dalilin yin fasikanci, suna kuma mūsun Yesu Kiristi wanda shi ne Makaɗaici Mai Iko Duka da kuma Ubangijinmu.

5Ko da yake kun riga kun san duk wannan, ina so in tuna muku cewa Ubangiji ya ceci mutanensa daga Masar, duk da haka daga baya ya hallaka waɗanda ba su ba da gaskiya ba. 6Haka ma mala’ikun da ba su riƙe matsayinsu na iko ba, waɗanda suka bar ainihin mazauninsu, su ne ya tsare a duhu daure da dawwammamun sarƙoƙi don hukunci ta babbar Ranan nan. 7Haka ma Sodom da Gomorra da garuruwan da suke kewaye da su, waɗanda su ma suka ba da kansu ga fasikanci da muguwar sha’awar jiki, sun zama misalin waɗanda suke shan hukuncin madawwamiyar wuta.

8Haka yake da masu mafarke-mafarken nan, gama sun ƙazantar da jikunansu, suka ƙi bin masu mulki, suna ɓata sunan talikan sararin sama. 9Kai, ko Mika’ilu babban shugaban mala’iku ma, sa’ad da yake mūsu da Iblis game da gawar Musa, bai yi garajen ɗora masa laifi da baƙar magana ba, sai dai ya ce, “Ubangiji yă tsawata maka!” 10Duk da haka mutanen nan suna maganar banza a kan kome da ba su gane ba; kuma abubuwan da suka fahimta bisa ga jiki, kamar dabbobi marasa hankali, waɗannan abubuwa ne suke hallaka su.

11Kaitonsu! Gama sun kama hanyar Kayinu; sun ruga a guje garin neman riba cikin kuskure kamar Bala’am; aka kuma hallaka su cikin tawayen Kora.

12Waɗannan mutane sun zama kamar ƙazanta a taronku na soyayya, suna ta ciye-ciye a cikinku, ba kunya ba tsoro. Su masu kiwo ne da suke ciyar da kansu kawai. Su kamar hadari ne da babu ruwa da iska take kori. Su kamar itatuwa ne, marasa ’ya’ya da rani, waɗanda aka tumɓuke, ko kamar itatuwan da aka tumɓuke suka kuma mutu ƙurmus. 13Su kamar raƙuman ruwan teku ne masu hauka, suna taƙama da tumbatsan kumfar kunyarsu. Su kamar taurari ne masu yawo barkatai, waɗanda aka ajiye mugun duhu saboda su har abada.

14Enok ma, wanda yake na bakwai daga Adamu, ya yi annabci game da waɗannan mutane cewa, “Duba, Ubangiji yana zuwa da dubu dubban tsarkakansa 15don yă yi wa kowa shari’a, yă kuma hukunta duk marasa tsoron Allah game da dukan ayyukansu na rashin tsoron Allah da suka aikata ta hanyar rashin tsoron Allah, da kuma dukan baƙaƙen kalmomin da masu zunubi marasa tsoron Allah suka faɗa game da shi.” 16Waɗannan mutane dai, gunaguni gare su, kullum ganin laifin waɗansu suke yi. Muguwar sha’awa ce kaɗai tunaninsu. Sun cika da banzar magana ta yabon kansu. Suna ruɗin mutane da zaƙin baki don samun ribar kansu.

Kira don jimiri

17Amma ku abokaina ƙaunatattu, ku tuna da abin da manzannin Ubangijinmu Yesu Kiristi suka faɗa a dā. 18Sun ce muku, “A kwanakin ƙarshe za a kasance da masu ba’a waɗanda za su bi sha’awace-sha’awacensu na rashin tsoron Allah.” 19Waɗannan mutanen ne, suke kawo rabe-rabe, masu bin abin da jiki yake so, marasa Ruhu.

20Amma ku, abokaina ƙaunatattu, ku gina kanku cikin bangaskiyarku mafi tsarki, ku kuma yi addu’a cikin Ruhu Mai Tsarki. 21Ku zauna cikin ƙaunar Allah yayinda kuke jira jinƙan Ubangijinmu Yesu Kiristi don yă kawo ku ga rai madawwami.

22Ku ji tausayin waɗanda suke shakka; 23ku cece waɗansu ta wurin fizge su daga wuta. Ga waɗansu kuma ku ji tausayinsu, amma tare da tsoro, har ma ku yi ƙyamar tufafin da suka ɓata da ayyukansu na jiki.

Yabo

24To, yabo yă tabbata a gare shi, shi wanda yake da iko yă tsare ku daga fāɗuwa, yă kuma miƙa ku marasa laifi a gaban ɗaukakarsa da matuƙar farin ciki. 25Gare shi kuma, shi da yake kaɗai Allah Mai Cetonmu, ta wurin Yesu Kiristi Ubangijinmu, bari ɗaukaka, daraja, iko da mulki, su tabbata a gare shi, tun farkon zamanai, yanzu, da har abada abadin! Amin.