Yahuda 1 – HCB & CRO

Hausa Contemporary Bible

Yahuda 1:1-25

1Yahuda, bawan Yesu Kiristi, ɗan’uwan Yaƙub,

Zuwa ga waɗanda aka kira, waɗanda Allah Uba yake ƙauna, waɗanda kuma Yesu Kiristi ya kiyaye.

2Jinƙai, salama da kuma ƙauna, su kasance tare da ku a yalwace.

Zunubi da hallakar marasa tsoron Allah

3Abokaina ƙaunatattu, ko da yake na yi marmari ƙwarai in rubuta muku game da ceton nan namu, sai na ga ya dace in rubuta, in gargaɗe ku ku tsaya da ƙarfi cikin bangaskiya wadda aka danƙa wa mutane masu tsarki na Allah sau ɗaya tak. 4Na faɗa haka ne domin waɗansu mutanen da aka rubuta hukuncinsu tun dā sun shiga cikinku a ɓoye. Su fa marasa tsoron Allah ne. Su ne waɗanda suka mai da alherin Allahnmu ya zama dalilin yin fasikanci, suna kuma mūsun Yesu Kiristi wanda shi ne Makaɗaici Mai Iko Duka da kuma Ubangijinmu.

5Ko da yake kun riga kun san duk wannan, ina so in tuna muku cewa Ubangiji ya ceci mutanensa daga Masar, duk da haka daga baya ya hallaka waɗanda ba su ba da gaskiya ba. 6Haka ma mala’ikun da ba su riƙe matsayinsu na iko ba, waɗanda suka bar ainihin mazauninsu, su ne ya tsare a duhu daure da dawwammamun sarƙoƙi don hukunci ta babbar Ranan nan. 7Haka ma Sodom da Gomorra da garuruwan da suke kewaye da su, waɗanda su ma suka ba da kansu ga fasikanci da muguwar sha’awar jiki, sun zama misalin waɗanda suke shan hukuncin madawwamiyar wuta.

8Haka yake da masu mafarke-mafarken nan, gama sun ƙazantar da jikunansu, suka ƙi bin masu mulki, suna ɓata sunan talikan sararin sama. 9Kai, ko Mika’ilu babban shugaban mala’iku ma, sa’ad da yake mūsu da Iblis game da gawar Musa, bai yi garajen ɗora masa laifi da baƙar magana ba, sai dai ya ce, “Ubangiji yă tsawata maka!” 10Duk da haka mutanen nan suna maganar banza a kan kome da ba su gane ba; kuma abubuwan da suka fahimta bisa ga jiki, kamar dabbobi marasa hankali, waɗannan abubuwa ne suke hallaka su.

11Kaitonsu! Gama sun kama hanyar Kayinu; sun ruga a guje garin neman riba cikin kuskure kamar Bala’am; aka kuma hallaka su cikin tawayen Kora.

12Waɗannan mutane sun zama kamar ƙazanta a taronku na soyayya, suna ta ciye-ciye a cikinku, ba kunya ba tsoro. Su masu kiwo ne da suke ciyar da kansu kawai. Su kamar hadari ne da babu ruwa da iska take kori. Su kamar itatuwa ne, marasa ’ya’ya da rani, waɗanda aka tumɓuke, ko kamar itatuwan da aka tumɓuke suka kuma mutu ƙurmus. 13Su kamar raƙuman ruwan teku ne masu hauka, suna taƙama da tumbatsan kumfar kunyarsu. Su kamar taurari ne masu yawo barkatai, waɗanda aka ajiye mugun duhu saboda su har abada.

14Enok ma, wanda yake na bakwai daga Adamu, ya yi annabci game da waɗannan mutane cewa, “Duba, Ubangiji yana zuwa da dubu dubban tsarkakansa 15don yă yi wa kowa shari’a, yă kuma hukunta duk marasa tsoron Allah game da dukan ayyukansu na rashin tsoron Allah da suka aikata ta hanyar rashin tsoron Allah, da kuma dukan baƙaƙen kalmomin da masu zunubi marasa tsoron Allah suka faɗa game da shi.” 16Waɗannan mutane dai, gunaguni gare su, kullum ganin laifin waɗansu suke yi. Muguwar sha’awa ce kaɗai tunaninsu. Sun cika da banzar magana ta yabon kansu. Suna ruɗin mutane da zaƙin baki don samun ribar kansu.

Kira don jimiri

17Amma ku abokaina ƙaunatattu, ku tuna da abin da manzannin Ubangijinmu Yesu Kiristi suka faɗa a dā. 18Sun ce muku, “A kwanakin ƙarshe za a kasance da masu ba’a waɗanda za su bi sha’awace-sha’awacensu na rashin tsoron Allah.” 19Waɗannan mutanen ne, suke kawo rabe-rabe, masu bin abin da jiki yake so, marasa Ruhu.

20Amma ku, abokaina ƙaunatattu, ku gina kanku cikin bangaskiyarku mafi tsarki, ku kuma yi addu’a cikin Ruhu Mai Tsarki. 21Ku zauna cikin ƙaunar Allah yayinda kuke jira jinƙan Ubangijinmu Yesu Kiristi don yă kawo ku ga rai madawwami.

22Ku ji tausayin waɗanda suke shakka; 23ku cece waɗansu ta wurin fizge su daga wuta. Ga waɗansu kuma ku ji tausayinsu, amma tare da tsoro, har ma ku yi ƙyamar tufafin da suka ɓata da ayyukansu na jiki.

Yabo

24To, yabo yă tabbata a gare shi, shi wanda yake da iko yă tsare ku daga fāɗuwa, yă kuma miƙa ku marasa laifi a gaban ɗaukakarsa da matuƙar farin ciki. 25Gare shi kuma, shi da yake kaɗai Allah Mai Cetonmu, ta wurin Yesu Kiristi Ubangijinmu, bari ɗaukaka, daraja, iko da mulki, su tabbata a gare shi, tun farkon zamanai, yanzu, da har abada abadin! Amin.

Knijga O Kristu

Judina 1:1-25

Pozdrav od Jude

1Od Jude, sluge Isusa Krista i Jakovljeva brata.

Pišem svima koji su pozvani živjeti u ljubavi Boga Oca i u skrbi Isusa Krista.

2Želim vam obilje Božje milosti, mira i ljubavi!

Opasnost od lažnih učitelja

3Ljubljeni prijatelji, kanio sam vam pisati o našemu zajedničkom spasenju, ali sada vidim da moram pisati o nečemu drugome: potaknuti vas da se borite za istinu Radosne vijesti.1:3 U grčkome: da se borite za vjeru. Tu nepromjenljivu istinu Bog je zauvijek dao svojemu svetom narodu. 4Kažem to zato što su se među vas uvukli neki bezbožnici koji govore da nam milost Božjega praštanja dopušta živjeti poročnim životom. Propast takvih već je odavno zapisana jer su se okrenuli protiv našega jedinoga Gospodara i Gospodina, Isusa Krista.

5Želim vas podsjetiti na to—iako to i sami dobro znate—da je Gospodin, pošto je iz Egipta izbavio cijeli izraelski narod, poslije uništio one koji mu nisu ostali vjerni. 6Sjetite se anđela koji su pogazili granicu ovlasti koju im je Bog dao te napustili svoje boravište. Bog ih drži okovane u paklenoj tami, gdje čekaju Dan suda. 7Ne zaboravite Sodomu i Gomoru te obližnje gradove u kojima su se ljudi toliko odavali izopačenu bludu da su pošli i za tijelom druge vrste. Ti su gradovi uništeni ognjem kao primjer kazne vječnim ognjem kojim će biti kažnjeni zlikovci.

8Tako i ti lažni učitelji, sanjari, i dalje žive pokvarenim životom, kaljaju svoje tijelo i ne priznaju Božju vlast te vrijeđaju Slavne.1:8 Vjerojatno zla nebeska bića. 9Čak ni arkanđeo Mihael, jedan od najmoćnijih anđela, nije se u prepirci s đavlom za Mojsijevo tijelo usudio izreći uvredljivu osudu, nego je samo rekao: “Gospodin te ukorio!” 10Ali ti se ljudi rugaju i vrijeđaju ono što ne razumiju. Kao nerazumne životinje, čine sve na što ih potiču tjelesni nagoni i tako srljaju u propast. 11Teško njima jer slijede primjer Kajina koji je ubio svojega brata, jer su, kao i Bileam, spremni učiniti sve za novac te će, poput Koraha, propasti zbog svoje pobune.

12Oni kaljaju vaša zajednička blagovanja kojima proslavljate ljubav Gospodnju i opasni su za vas jer na njima bestidno ugađaju sebi. Poput oblaka su koji suhoj zemlji ne donose kišu. Mnogo obećavaju, ali ništa ne daju. Oni su kao voćke koje u jesen ne donesu ploda. Već mrtve, i drugi put umiru kad se s korijenom iščupaju. 13Poput mahnitih su morskih valova što se pjene vlastitim sramotama, poput lutajućih zvijezda koje će završiti u vječitoj, mračnoj tmini.

14Patrijarh Henok, koji je živio sedam naraštaja nakon Adama, prorokovao je o takvim ljudima:

“Gle, Gospodin dolazi

s desettisućama svojih svetih.

15Osudit će bezbožnike za sva zlodjela

koja su počinili u svojoj pobuni i za sve uvrede što su ih bezbožni grešnici

izgovorili protiv njega.”

16Takvi su ljudi nezadovoljnici koji uvijek prigovaraju, a čine što god im se prohtije. Razmetljivi su hvalisavci i drugima laskaju da bi od njih izvukli korist.

Poziv na vjernost

17Dragi moji, sjetite se što su prorekli apostoli našega Gospodina Isusa Krista: 18Na koncu vremena doći će izrugivači koji će živjeti prema svojim bezbožnim požudama. 19Takvi među vama prave razdore. Žive prema tjelesnim nagonima jer nemaju u sebi Božjeg Duha.

20Ali vi, ljubljeni prijatelji, morate izgrađivati svoj život na temelju svoje svete vjere. Molite se kako vas upućuje Sveti Duh.1:20 U grčkome: molite se u Svetome Duhu. 21Očuvajte sebe u Božjoj ljubavi očekujući milosrđe našega Gospodina Isusa Krista za vječni život! 22Budite milosrdni prema onima koji se kolebaju u vjeri. 23Spašavajte ljude jer ih tako otimate iz samoga paklenog ognja. Ima i takvih kojima treba oprezno iskazivati milosrđe pazeći da njihovi grijesi i vas ne okaljaju.1:23 U grčkome: mrzeći i samu haljinu okaljanu njihovim tijelom.

Hvalospjev Bogu

24Sva slava Bogu, koji vas može očuvati da ne posrnete, koji će vas, čiste od grijeha i radosne, dovesti u svoju slavnu nazočnost. 25Sva slava jedinom Bogu Spasitelju kroz našega Gospodina Isusa Krista. Slava, veličanstvo, sila i vlast pripadali su mu prije početka vremena, pa mu tako pripadaju i danas, i zauvijek. Amen.