Yahuda 1 – HCB & CCBT

Hausa Contemporary Bible

Yahuda 1:1-25

1Yahuda, bawan Yesu Kiristi, ɗan’uwan Yaƙub,

Zuwa ga waɗanda aka kira, waɗanda Allah Uba yake ƙauna, waɗanda kuma Yesu Kiristi ya kiyaye.

2Jinƙai, salama da kuma ƙauna, su kasance tare da ku a yalwace.

Zunubi da hallakar marasa tsoron Allah

3Abokaina ƙaunatattu, ko da yake na yi marmari ƙwarai in rubuta muku game da ceton nan namu, sai na ga ya dace in rubuta, in gargaɗe ku ku tsaya da ƙarfi cikin bangaskiya wadda aka danƙa wa mutane masu tsarki na Allah sau ɗaya tak. 4Na faɗa haka ne domin waɗansu mutanen da aka rubuta hukuncinsu tun dā sun shiga cikinku a ɓoye. Su fa marasa tsoron Allah ne. Su ne waɗanda suka mai da alherin Allahnmu ya zama dalilin yin fasikanci, suna kuma mūsun Yesu Kiristi wanda shi ne Makaɗaici Mai Iko Duka da kuma Ubangijinmu.

5Ko da yake kun riga kun san duk wannan, ina so in tuna muku cewa Ubangiji ya ceci mutanensa daga Masar, duk da haka daga baya ya hallaka waɗanda ba su ba da gaskiya ba. 6Haka ma mala’ikun da ba su riƙe matsayinsu na iko ba, waɗanda suka bar ainihin mazauninsu, su ne ya tsare a duhu daure da dawwammamun sarƙoƙi don hukunci ta babbar Ranan nan. 7Haka ma Sodom da Gomorra da garuruwan da suke kewaye da su, waɗanda su ma suka ba da kansu ga fasikanci da muguwar sha’awar jiki, sun zama misalin waɗanda suke shan hukuncin madawwamiyar wuta.

8Haka yake da masu mafarke-mafarken nan, gama sun ƙazantar da jikunansu, suka ƙi bin masu mulki, suna ɓata sunan talikan sararin sama. 9Kai, ko Mika’ilu babban shugaban mala’iku ma, sa’ad da yake mūsu da Iblis game da gawar Musa, bai yi garajen ɗora masa laifi da baƙar magana ba, sai dai ya ce, “Ubangiji yă tsawata maka!” 10Duk da haka mutanen nan suna maganar banza a kan kome da ba su gane ba; kuma abubuwan da suka fahimta bisa ga jiki, kamar dabbobi marasa hankali, waɗannan abubuwa ne suke hallaka su.

11Kaitonsu! Gama sun kama hanyar Kayinu; sun ruga a guje garin neman riba cikin kuskure kamar Bala’am; aka kuma hallaka su cikin tawayen Kora.

12Waɗannan mutane sun zama kamar ƙazanta a taronku na soyayya, suna ta ciye-ciye a cikinku, ba kunya ba tsoro. Su masu kiwo ne da suke ciyar da kansu kawai. Su kamar hadari ne da babu ruwa da iska take kori. Su kamar itatuwa ne, marasa ’ya’ya da rani, waɗanda aka tumɓuke, ko kamar itatuwan da aka tumɓuke suka kuma mutu ƙurmus. 13Su kamar raƙuman ruwan teku ne masu hauka, suna taƙama da tumbatsan kumfar kunyarsu. Su kamar taurari ne masu yawo barkatai, waɗanda aka ajiye mugun duhu saboda su har abada.

14Enok ma, wanda yake na bakwai daga Adamu, ya yi annabci game da waɗannan mutane cewa, “Duba, Ubangiji yana zuwa da dubu dubban tsarkakansa 15don yă yi wa kowa shari’a, yă kuma hukunta duk marasa tsoron Allah game da dukan ayyukansu na rashin tsoron Allah da suka aikata ta hanyar rashin tsoron Allah, da kuma dukan baƙaƙen kalmomin da masu zunubi marasa tsoron Allah suka faɗa game da shi.” 16Waɗannan mutane dai, gunaguni gare su, kullum ganin laifin waɗansu suke yi. Muguwar sha’awa ce kaɗai tunaninsu. Sun cika da banzar magana ta yabon kansu. Suna ruɗin mutane da zaƙin baki don samun ribar kansu.

Kira don jimiri

17Amma ku abokaina ƙaunatattu, ku tuna da abin da manzannin Ubangijinmu Yesu Kiristi suka faɗa a dā. 18Sun ce muku, “A kwanakin ƙarshe za a kasance da masu ba’a waɗanda za su bi sha’awace-sha’awacensu na rashin tsoron Allah.” 19Waɗannan mutanen ne, suke kawo rabe-rabe, masu bin abin da jiki yake so, marasa Ruhu.

20Amma ku, abokaina ƙaunatattu, ku gina kanku cikin bangaskiyarku mafi tsarki, ku kuma yi addu’a cikin Ruhu Mai Tsarki. 21Ku zauna cikin ƙaunar Allah yayinda kuke jira jinƙan Ubangijinmu Yesu Kiristi don yă kawo ku ga rai madawwami.

22Ku ji tausayin waɗanda suke shakka; 23ku cece waɗansu ta wurin fizge su daga wuta. Ga waɗansu kuma ku ji tausayinsu, amma tare da tsoro, har ma ku yi ƙyamar tufafin da suka ɓata da ayyukansu na jiki.

Yabo

24To, yabo yă tabbata a gare shi, shi wanda yake da iko yă tsare ku daga fāɗuwa, yă kuma miƙa ku marasa laifi a gaban ɗaukakarsa da matuƙar farin ciki. 25Gare shi kuma, shi da yake kaɗai Allah Mai Cetonmu, ta wurin Yesu Kiristi Ubangijinmu, bari ɗaukaka, daraja, iko da mulki, su tabbata a gare shi, tun farkon zamanai, yanzu, da har abada abadin! Amin.

Chinese Contemporary Bible (Traditional)

猶大書 1:1-25

1我是耶穌基督的奴僕、雅各的兄弟猶大,現在寫信給蒙父上帝呼召、眷愛、被耶穌基督看顧的人。

2願上帝豐豐富富地賜給你們憐憫、平安和慈愛!

捍衛真道

3親愛的弟兄姊妹,我一直迫切地想寫信跟你們談談我們所共享的救恩,但現在我覺得有必要寫信勸勉你們竭力護衛一次就完整地交給聖徒的真道。 4因為有些不敬虔的人偷偷地混進你們中間,以上帝的恩典作藉口,放縱情慾,否認獨一的主宰——我們的主耶穌基督。聖經上早已記載,這樣的人必受到審判。

前車之鑑

5以下的事情,你們雖然都知道,但我還要再提醒你們:從前上帝1·5 上帝」有些抄本作「主」。把祂的子民從埃及救出來,後來把其中不信的人滅絕了。 6至於不守本分、擅離崗位的天使,上帝也用鎖鏈將他們永遠囚禁在幽暗裡,等候最後審判的大日子到來。 7此外,所多瑪蛾摩拉及其附近城鎮的人同樣因為荒淫無度、沉溺於變態的情慾而遭到永火的刑罰。這些事都成為我們的警戒。

假教師的惡行

8同樣,這些作夢的人玷污自己的身體,不服權柄,褻瀆有尊榮的。 9當天使長米迦勒摩西的屍體跟魔鬼爭辯的時候,尚且不敢用毀謗的話譴責牠,只說:「願主責罰你!」 10這些人卻毀謗自己不明白的事,像沒有理性的野獸一樣憑本能行事,結果自取滅亡。 11他們大禍臨頭了!他們步了該隱的後塵,為謀利而重蹈巴蘭的謬誤,又像可拉一樣因叛逆而滅亡。 12這些人在你們的愛宴中是敗類1·12 敗類」希臘文是「暗礁」或「污點」的意思。。他們肆無忌憚地吃喝,是只顧餵養自己的牧人;是沒有雨的雲,隨風飄蕩;是深秋不結果子的樹,被連根拔起,徹底枯死。 13他們是海中的狂濤,翻動著自己可恥的泡沫,是流蕩的星星,有幽幽黑暗永遠留給他們。

14亞當的第七代子孫以諾曾經針對這些人說預言:「看啊!主率領祂千萬的聖者一同降臨, 15要審判所有的人,按不虔不敬的罪人所行的惡事和他們褻瀆上帝的話定他們的罪。」 16這些人滿腹牢騷,怨天尤人,放縱自己的邪情私慾。他們口出狂言,為了謀利而阿諛奉承他人。

牢記警告

17親愛的弟兄姊妹,要謹記主耶穌基督的使徒從前給你們的警告。 18他們曾對你們說:「末世的時候,必定有不敬虔、好譏笑的人放縱自己的邪情私慾。」 19這些人製造分裂,血氣用事,心中沒有聖靈。

20親愛的弟兄姊妹,你們要在至聖的真道上造就自己,在聖靈的引導下禱告, 21常在上帝的愛中,等候我們主耶穌基督施憐憫賜給你們永生。

22那些心存疑惑的人,你們要憐憫他們; 23有些人,你們要將他們從火中搶救出來;還有些人,你們要懷著畏懼的心憐憫他們,甚至要厭惡被他們的邪情私慾玷污的衣服。

祝頌

24願榮耀歸給我們的救主——獨一的上帝!祂能保守你們不失足犯罪,使你們無瑕無疵、歡歡喜喜地站在祂的榮耀面前。 25願榮耀、威嚴、能力和權柄藉著我們的主耶穌基督都歸給祂,從萬世以前直到現今,一直到永永遠遠。阿們!