Yaƙub 1 – HCB & TNCV

Hausa Contemporary Bible

Yaƙub 1:1-27

1Yaƙub, bawan Allah da kuma na Ubangiji Yesu Kiristi,

Zuwa ga kabilan nan goma sha biyu, da suke warwartse a cikin al’ummai.

Gaisuwa mai yawa.

Gwaje-gwaje da jarrabobi

2Ku ɗauki wannan da farin ciki mai tsabta, ’yan’uwana, duk sa’ad da gwaje-gwaje na kowane iri suka zo muku, 3domin kun san cewa gwajin bangaskiyarku yakan haifi daurewa. 4Dole daurewa ta kammala aikinta don ku zama balagaggu da kuma cikakku, ba ku kuma rasa kome ba. 5In waninku ya rasa hikima, ya kamata yă roƙi Allah, mai bayarwa hannu sake ga kowa ba tare da gori ba, za a kuwa ba shi. 6Amma sa’ad da ya roƙa, dole yă gaskata, ba tare da shakka ba, domin shi mai shakka, yana kama da raƙumar ruwan tekun da iska take kori tana kuma ɓuɓɓugowa. 7Kada irin wannan mutum yă yi tsammani zai sami wani abu daga Ubangiji; 8shi mai zuciya biyu ne, marar tsai da zuciyarsa wuri ɗaya a cikin duk abin da yake yi.

9Bari ɗan’uwan da yake cikin halin ƙasƙanci yă yi taƙama a matsayinsa na ɗaukaka. 10Amma wanda yake mai arziki, ya kamata yă yi taƙama a matsayinsa na ƙasƙanci, gama ba zai daɗe ba kamar furen jeji. 11Gama in rana ta fito ta yi zafi mai tsanani sai ta sa tsiro yă yanƙwane tsiro; furensa yă kakkaɓe, kyansa kuma yă lalace. Haka ma mai arziki zai shuɗe yayinda yake cikin harkarsa.

12Mai albarka ne mutumin da yake daurewa cikin gwaji, gama bayan ya yi nasara da gwajin, zai sami rawanin rai wanda Allah ya yi alkawari ga waɗanda suke ƙaunarsa.

13Sa’ad da aka jarrabci mutum, kada yă ce, “Allah ne yake jarrabtarsa.” Gama ba ya yiwuwa a jarrabci Allah da mugunta, shi kuma ba ya jarrabtar kowa; 14amma akan jarrabce kowane mutum sa’ad da muguwar sha’awarsa ta janye shi ta kuma rinjaye shi. 15Sa’an nan, bayan da sha’awar ta yi ciki, takan haifi zunubi; zunubi kuwa, sa’ad da ya balaga yakan haifi mutuwa.

16Kada a ruɗe ku, ’yan’uwana ƙaunatattu. 17Kowane abu mai kyau da kuma kowace cikakkiyar kyauta daga sama suke, sun sauko ne daga wurin Uban haskoki, wanda ba sauyawa ko wata alamar sākewa a gare shi faufau. 18Ya zaɓa yă haife mu ta wurin kalmar gaskiya, domin mu zama ’ya’yan fari na dukan abin da ya halitta.

Saurarawa da kuma aikatawa

19’Yan’uwana ƙaunatattu, ku lura da wannan. Ya kamata kowa yă kasance mai saurin saurara, ba mai saurin magana ba, ba kuma mai saurin fushi ba, 20gama fushin mutum ba ya kawo rayuwar adalcin da Allah yake so. 21Saboda haka, ku rabu da ƙazamin hali da kuma kowace irin mugunta ku kuma yi na’am da maganar da aka shuka a cikinku da tawali’u, wadda za tă iya cetonku.

22Kada ku zama masu ji kawai, ku ruɗi kanku. A maimakon haka ku zama masu yin abin da ta ce. 23Duk wanda yake ji magana ne kawai, bai kuwa aikata abin da ta ce ba, yana kama da mutumin da ya kalli fuskarsa a madubi 24bayan ya kalli kansa, sa’ad da ya tashi daga wurin, nan da nan sai yă manta da kamanninsa. 25Amma duk mai duba cikakkiyar ƙa’idan nan ta ’yanci, ya kuma nace a kanta, ya zama ba mai ji ne kawai yă mance ba, sai dai mai yi ne yă zartar, to wannan shi za a yi wa albarka a cikin abin da yake yi.

26In wani ya ɗauki kansa mai addini ne duk da haka bai ƙame harshensa ba, ruɗin kansa yake yi addininsa kuwa banza ne. 27Addinin da Allah Ubanmu ya yarda da shi a matsayin mai tsabta da kuma marar aibi shi ne, a kula da marayu da gwauraye cikin damuwoyinsu, a kuma kiyaye kai daga lalacin da duniya take sa wa.

Thai New Contemporary Bible

ยากอบ 1:1-27

1จดหมายฉบับนี้จากข้าพเจ้ายากอบผู้เป็นผู้รับใช้ของพระเจ้าและขององค์พระเยซูคริสต์เจ้า

ถึงชนสิบสองเผ่าซึ่งกระจัดกระจายอยู่ในชาติต่างๆ

การทดสอบและการทดลอง

2พี่น้องทั้งหลายเมื่อใดที่ท่านเผชิญความทุกข์ยากนานาประการ จงถือเป็นเรื่องที่น่ายินดีจริงๆ 3เพราะท่านรู้ว่าการทดสอบความเชื่อของท่านนั้นทำให้เกิดความอดทนบากบั่น 4จงอดทนบากบั่นให้ถึงที่สุดเพื่อท่านจะเติบโตเต็มที่และสมบูรณ์เพียบพร้อมและไม่มีสิ่งใดบกพร่องเลย 5ถ้าผู้ใดในพวกท่านขาดสติปัญญา จงทูลขอจากพระเจ้าผู้ประทานด้วยพระทัยกว้างขวางแก่คนทั้งปวงโดยไม่ตำหนิ แล้วผู้นั้นจะได้รับ 6แต่เมื่อเขาทูลขอ เขาต้องเชื่อและไม่สงสัยเลย เพราะผู้ใดที่สงสัยก็เป็นเหมือนคลื่นในทะเลซึ่งซัดไปซัดมาตามแรงลม 7ผู้นั้นอย่าคิดว่าเขาจะได้รับสิ่งใดจากองค์พระผู้เป็นเจ้าเลย 8เขาเป็นคนสองใจเอาแน่อะไรไม่ได้

9พี่น้องที่ต่ำต้อยควรภูมิใจในฐานะอันสูงส่งของตน 10แต่ผู้ที่ร่ำรวยควรภูมิใจในฐานะอันต่ำต้อยของตนเพราะเขาจะต้องสูญสิ้นไปเหมือนดอกหญ้า 11เพราะเมื่อดวงอาทิตย์ขึ้น ความร้อนก็แผดเผาต้นหญ้าให้เหี่ยวแห้งไป ดอกหญ้าก็ร่วงโรย สูญสิ้นความงาม เช่นเดียวกันคนร่ำรวยก็จะเสื่อมสูญไปแม้ขณะดำเนินกิจการของตน

12ความสุขมีแก่ผู้ที่อดทนบากบั่นเมื่อถูกทดลอง เพราะเมื่อเขายืนหยัดผ่านการทดสอบก็จะได้รับมงกุฎแห่งชีวิตซึ่งพระเจ้าได้ทรงสัญญาไว้กับผู้ที่รักพระองค์

13ขณะถูกทดลองให้ทำบาป อย่าให้ใครพูดว่า “พระเจ้าทรงทดลองข้าพเจ้า” เพราะความชั่วไม่อาจล่อลวงพระเจ้าให้ทำบาปและพระองค์ก็ไม่ทรงล่อลวงผู้ใดเลย 14ทว่าแต่ละคนถูกทดลองเมื่อตัณหาชั่วของตนเองชักจูงไปให้ติดกับ 15หลังจากมีตัณหาแล้วก็ก่อให้เกิดบาป และเมื่อบาปโตเต็มที่ก็ก่อให้เกิดความตาย

16พี่น้องที่รัก อย่าให้ผู้ใดล่อลวงท่านเลย 17ของประทานทุกอย่างที่ดีและล้ำเลิศล้วนมาจากเบื้องบน จากพระบิดาแห่งดวงสว่างทั้งหลายในฟ้าสวรรค์ ผู้ไม่ได้ทรงผันแปรเหมือนเงาที่แปรเปลี่ยน 18พระองค์ทรงเลือกที่จะให้เราบังเกิดผ่านทางข่าวประเสริฐ1:18 หรือพระวจนะแห่งความจริง เพื่อเราจะได้เป็นเหมือนผลแรกอันดีเลิศของสรรพสิ่งที่ทรงสร้าง

จงฟังและทำตาม

19พี่น้องที่รักพึงทราบข้อนี้คือ ทุกคนควรไวในการฟัง ช้าในการพูด และช้าในการโกรธ 20เพราะความโกรธของมนุษย์ไม่ได้ก่อให้เกิดชีวิตอันชอบธรรมที่พระเจ้าทรงประสงค์ 21เหตุฉะนั้นจงขจัดสารพัดความโสมมทางศีลธรรมและความชั่วอันดาษดื่น และถ่อมใจน้อมรับพระวจนะที่ได้ปลูกฝังไว้ในท่านซึ่งสามารถช่วยท่านให้รอดได้

22อย่าเพียงแต่ฟังพระวจนะซึ่งเป็นการหลอกตัวเอง แต่จงปฏิบัติตามพระวจนะนั้น 23ผู้ใดที่ฟังพระวจนะแต่ไม่ได้ทำตาม ผู้นั้นก็เป็นเหมือนคนที่ส่องกระจกมองหน้าตัวเอง 24หลังจากส่องดูแล้วก็ไปและทันใดนั้นก็ลืมว่าหน้าตาตนเองเป็นอย่างไร 25ส่วนผู้ที่พินิจดูบทบัญญัติอันสมบูรณ์ซึ่งให้เสรีภาพและทำสิ่งนี้ต่อไปโดยไม่ลืมสิ่งที่เขาได้ยิน แต่ปฏิบัติตาม เขาก็จะได้รับพรในสิ่งที่ตนทำ

26ถ้าผู้ใดคิดว่าตนเองเคร่งศาสนาแต่ไม่ควบคุมลิ้นของตนให้ดีก็หลอกตัวเอง ศาสนาของเขาก็ไร้ค่า 27ศาสนาที่พระเจ้าพระบิดาของเรายอมรับว่าบริสุทธิ์และไร้ตำหนิคือ การดูแลลูกกำพร้าและหญิงม่ายที่ทุกข์ร้อนและการรักษาตนเองให้พ้นจากมลทินฝ่ายโลก