Mattiyu 8 – HCB & NRT

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 8:1-34

Mutum mai kuturta

(Markus 1.40-45; Luka 5.12-16)

1Da ya sauko daga dutsen, sai taron mutane mai yawan gaske suka bi shi. 2Wani mutum mai kuturta ya zo ya durƙusa a gabansa ya ce, “Ubangiji, in kana so, kana iya tsabtacce ni.”

3Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin. Ya ce, “Ina so, ka tsabtacce!” Nan da nan aka warkar8.3 Girik aka tsabtacce da shi daga kuturtarsa. 4Sai Yesu ya ce masa, “Ka lura kada ka gaya wa kowa. Sai dai ka tafi, ka nuna kanka ga firist ka kuma yi bayarwar da Musa ya umarta, a matsayin shaida gare su.”

Bangaskiyar jarumi

(Luka 7.1-10; Yohanna 4.43-54)

5Da Yesu ya shiga Kafarnahum, sai wani jarumi ya zo wurinsa, yana neman taimako. 6Ya ce, “Ubangiji, bawana yana kwance a gida shanyayye, yana kuma shan azaba ƙwarai.”

7Yesu ya ce masa, “Zan je in warkar da shi.”

8Jarumin ya amsa, “Ubangiji, ban cancanci in sa ka zo gidana ba, ka dai yi magana kawai, bawana zai warke. 9Gama ni kaina mutum ne a ƙarƙashin iko, da kuma sojoji a ƙarƙashina. Nakan ce wa wannan, ‘Je ka,’ sai yă tafi; wancan kuma, ‘Zo nan,’ sai yă zo. Nakan ce wa bawana, ‘Yi wannan,’ sai kuwa yă yi.”

10Da Yesu ya ji wannan, sai ya yi mamaki ya kuma ce wa waɗanda suke binsa, “Gaskiya nake gaya muku, ban taɓa samun wani a Isra’ila da bangaskiya mai girma haka ba. 11Ina kuma gaya muku da yawa za su zo daga gabas da kuma yamma, su ɗauki wuraren zamansu a biki tare da Ibrahim, Ishaku, da Yaƙub a cikin mulkin sama. 12Amma za a jefar da ’ya’yan mulki waje, zuwa cikin baƙin duhu, inda za a yi kuka da cizon haƙora.”

13Sa’an nan Yesu ya ce wa jarumin, “Je ka! Za a yi bisa ga bangaskiyarka.” A daidai wannan lokaci bawansa kuwa ya warke.

Yesu ya warkar da mutane da yawa

(Markus 1.29-34; Luka 4.38-41)

14Da Yesu ya zo cikin gidan Bitrus, sai ya ga surukar Bitrus tana kwance a gado tana da zazzaɓi. 15Ya taɓa hannunta sai zazzaɓin ya sake ta, ta kuwa tashi ta fara yin masa hidima.

16Da yamma ta yi, aka kawo masa masu aljanu da yawa, ya kuwa fitar da ruhohin ta wurin magana, ya kuma warkar da dukan marasa lafiya. 17Wannan ya faru ne domin a cika abin da aka faɗa ta bakin annabi Ishaya cewa,

“Ya ɗebi rashin lafiyarmu,

ya kuma ɗauki cututtukanmu.”8.17 Ish 53.4

Wahalar bin Yesu

(Luka 9.57-62)

18Da Yesu ya ga taron mutane kewaye da shi, sai ya ba da umarni a ƙetare zuwa ɗayan hayin tafkin. 19Sai wani malamin dokoki ya zo wurinsa ya ce, “Malam, zan bi ka duk inda za ka.”

20Sai Yesu ya amsa ya ce, “Yanyawa suna da ramummuka, tsuntsayen sararin sama suna da sheƙuna, amma Ɗan Mutum ba shi da wurin da zai sa kansa.”

21Sai wani almajiri ya ce masa, “Ubangiji, da farko bari in je in binne mahaifina.”

22Amma Yesu ya ce masa, “Ka bi ni, ka bar matattu su binne matattunsu.”

Yesu ya kwantar da hadari

(Markus 4.35-41; Luka 8.22-25)

23Sai ya shiga jirgin ruwa, almajiransa kuwa suka bi shi. 24Ba zato ba tsammani, sai wani babban hadari ya taso a tafkin, har raƙuman ruwan suka sha kan jirgin. Amma Yesu yana barci. 25Almajiran suka je suka tashe shi, suna cewa, “Ubangiji, ka cece mu! Za mu nutse!”

26Ya amsa ya ce, “Ku masu ƙarancin bangaskiya, me ya sa kuke tsoro haka?” Sa’an nan ya tashi ya tsawata wa iskar da kuma raƙuman ruwan, sai wuri ya yi tsit gaba ɗaya.

27Mutanen suka yi mamaki suka ce, “Wane irin mutum ne wannan? Har iska da raƙuman ruwa suna masa biyayya!”

Warkar da mutum biyu masu aljanu

(Markus 5.1-20; Luka 8.26-39)

28Da ya isa ɗayan gefen a yankin Gadarenawa8.28 Waɗansu rubuce-rubucen hannu na dā suna da Gergesenawa; waɗansu kuma Gerasenawa ne a nan (ko kuwa Gerasenawa), sai ga mutum biyu masu aljanu suna fitowa daga kaburbura suka tarye shi. Su abin tsoro ne ƙwarai, har ba mai iya bin wannan hanya. 29Suka yi ihu suka ce, “Me ya haɗa ka da mu, Ɗan Allah?” Ka zo ne nan don ka ji mana kafin lokaci yă yi?

30Nesa kaɗan da su kuwa akwai babban garken aladu da yake kiwo. 31Aljanun suka roƙi Yesu suka ce, “In ka fitar da mu, tura mu cikin garken aladun nan.”

32Ya ce musu, “Ku tafi!” Sai suka fita suka shiga cikin aladun, dukan garken kuwa ya gangara a guje daga kan tudun zuwa cikin tafkin aladun kuma suka mutu a cikin ruwa. 33Masu kiwon aladun suka ruga, suka je cikin gari suka ba da labarin dukan wannan, haɗe da abin da ya faru da mutanen nan masu aljanu. 34Sai dukan garin suka fito don su taryi Yesu. Da suka kuwa gan shi, sai suka roƙe shi yă bar musu yanki.

New Russian Translation

Матфея 8:1-34

Исцеление прокаженного

(Мк. 1:40-44; Лк. 5:12-14)

1Когда Иисус спустился с горы, за Ним последовало множество людей. 2Тут к Нему подошел человек, больной проказой, поклонился Ему и сказал:

– Господи, если Ты захочешь, Ты можешь меня очистить.

3Иисус протянул руку и прикоснулся к нему, сказав:

– Хочу, очистись!

В тот же миг человек исцелился от проказы. 4Иисус тогда сказал ему:

– Смотри, никому не говори об этом, но пойди, покажись священнику и принеси в жертву дар, как это повелел Моисей8:4 См. Лев. 14:1-32.. Так твое исцеление будет удостоверено перед людьми.

Вера офицера

(Лк. 7:1-10; Лк. 13:28-29)

5Когда Иисус пришел в Капернаум, к Нему подошел сотник и попросил о помощи.

6– Господин, – сказал он, – мой слуга лежит дома парализованный и ужасно мучается.

7Иисус ответил ему:

– Хорошо, Я приду и исцелю его.

8Сотник возразил Иисусу:

– Господи, я не достоин, чтобы Ты вошел под крышу моего дома. Скажи лишь слово, и мой слуга выздоровеет. 9Ведь и сам я подчиняюсь приказам, и у меня в подчинении тоже есть воины. Я говорю одному: «Ступай!» – и он идет, другому: «Ко мне!» – и тот приходит. Слуге моему говорю: «Сделай это!» – и он делает.

10Иисус, услышав это, удивился и сказал тем, кто шел за Ним:

– Говорю вам истину, что даже в Израиле Я не встречал такой сильной веры. 11Говорю вам, что многие из других народов придут с востока и запада и возлягут на пиру с Авраамом, Исааком и Иаковом в Небесном Царстве. 12Сыны же Царства будут выброшены вон, во тьму, где будет плач и скрежет зубов.

13И Иисус сказал сотнику:

– Иди! По твоей вере будет тебе.

И в тот же час слуга выздоровел.

Исцеления больных

(Мк. 1:29-34; Лк. 4:38-41)

14Придя в дом Петра, Иисус увидел, что его теща лежит в горячке. 15Он прикоснулся к ее руке, и жар оставил ее, она встала и начала накрывать для Него на стол. 16С наступлением вечера к Иисусу привели много людей, одержимых демонами. Он изгнал духов словом и исцелил всех больных. 17Это было исполнением слов пророка Исаии: «Он взял наши немощи и понес наши болезни»8:17 Ис. 53:4..

Будущие последователи Иисуса

(Лк. 9:57-60)

18Когда Иисус увидел, что вокруг Него собралась большая толпа, Он велел ученикам переправиться на другую сторону озера. 19Тут к Нему подошел один из учителей Закона и сказал:

– Учитель, я пойду за Тобой, куда бы Ты ни пошел.

20Иисус ответил:

– У лисиц есть норы, и у птиц небесных – гнезда, а Сыну Человеческому8:20 Сыну Человеческому – букв.: «Сыну Человека» – это один из титулов Христа, данный пророком Даниилом (см. Дан. 7:13-14). Иисус всегда употреблял этот титул применительно к Себе. Он делал это, чтобы намекнуть на то, что Он и есть Тот Самый, о Ком говорится у Даниила – Царь над всеми народами, Чье Царство будет вечным. негде и голову приклонить.

21А другой человек, из Его учеников, сказал:

– Господи, разреши мне прежде пойти и похоронить отца моего8:21 В первом веке существовал погребальный обычай, по которому тело усопшего на год помещали в пещеру. После этого времени, когда от тела ничего кроме костей не оставалось, их убирали и хоронили в урне. Этот стих может также быть переведен как: Господи, разреши остаться со своим отцом, чтобы, когда он умрет, я смог похоронить его..

22Но Иисус ответил ему:

– Следуй за Мной, пусть мертвые сами хоронят своих мертвецов.

Иисус усмиряет шторм

(Мк. 4:36-41; Лк. 8:22-25)

23Иисус вошел в лодку, и ученики сели вместе с Ним. 24Внезапно на озере поднялся такой сильный шторм, что лодку захлестывало волнами. А Иисус в это время спал. 25Ученики разбудили Его, говоря:

– Господи, спаси нас! Мы гибнем!

26Иисус ответил:

– Маловеры, ну что вы испугались?

Он встал, запретил ветру и волнам, и наступил полный штиль. 27Ученики удивленно спрашивали:

– Кто же Он, что даже ветер и волны повинуются Ему?

Иисус изгоняет демонов в стадо свиней

(Мк. 5:1-17; Лк. 8:26-37)

28Когда Иисус прибыл на другую сторону озера, в Гадаринскую землю, навстречу Ему из гробниц вышли два человека, одержимых демонами. Они были такие буйные, что никто не решался проходить той дорогой.

29– Что Ты от нас хочешь, Сын Божий? – закричали они. – Ты пришел мучить нас еще до назначенного срока?

30Неподалеку от них паслось большое стадо свиней. 31Демоны попросили Иисуса:

– Если Ты нас выгонишь, то пошли нас в это стадо свиней.

32Иисус сказал им:

– Идите!

Выйдя из людей, демоны вошли в свиней. Все стадо бросилось с обрыва в озеро и погибло в воде. 33А свинопасы побежали в город и все рассказали, включая и то, что произошло с одержимыми. 34Тогда все жители города вышли навстречу Иисусу и, увидев Его, попросили покинуть их края.