Mattiyu 5 – HCB & SNC

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 5:1-48

Albarku

1Ganin taron mutane, sai ya hau kan gefen dutse ya zauna.

(Luka 6.20-23)

Almajiransa kuwa suka zo wurinsa, 2sai ya fara koya musu.

Yana cewa,

3“Masu albarka ne waɗanda suke matalauta a ruhu,

gama mulkin sama nasu ne.

4Masu albarka ne waɗanda suke makoki,

gama za a yi musu ta’aziyya.

5Masu albarka ne waɗanda suke masu tawali’u,

gama za su gāji duniya.

6Masu albarka ne waɗanda suke jin yunwa da ƙishirwa don gani an yi adalci,

gama za a ƙosar da su.

7Masu albarka ne waɗanda suke masu jinƙai,

gama za a nuna musu jinƙai.

8Masu albarka ne waɗanda suke masu tsabtar zuciya,

gama za su ga Allah.

9Masu albarka ne waɗanda suke masu ƙulla zumunci,

gama za a kira su ’ya’yan Allah.

10Masu albarka ne waɗanda ake tsananta musu don gani an yi adalci,

gama mulkin sama nasu ne.

11“Masu albarka ne ku, sa’ad da mutane suke zaginku, suna tsananta muku, suna kuma faɗin kowace irin muguwar magana a kanku saboda ni. 12Ku yi murna ku kuma yi farin ciki, domin ladarku mai yawa ne a sama, gama haka suka tsananta wa annabawan da suka riga ku.

Gishiri da kuma haske

(Markus 9.50; Luka 14.34,35)

13“Ku ne gishirin duniya, amma in gishiri ya rabu da daɗin ɗanɗanonsa, yaya za a sāke mai da daɗin ɗanɗanonsa? Ba shi da sauran amfani, sai dai a zubar da shi mutane kuma su tattaka.

14“Ku ne hasken duniya. Birnin da yake a bisan tudu ba ya ɓoyuwa. 15Mutane ba sa ƙuna fitila su rufe ta da murfi. A maimako, sukan ajiye ta a kan wurin ajiye fitila, takan kuma ba da haske ga kowa a cikin gida. 16Haka ma, bari haskenku yă haskaka a gaban mutane, domin su ga ayyukanku masu kyau, su kuwa yabi Ubanku da yake cikin sama.

Cikar doka

17“Kada ku yi tsammani na zo ne domin in kawar da Doka ko kuma Annabawa; ban zo domin in kawar da su ba ne, sai dai domin in ciccika su. 18Gaskiya nake gaya muku, kafin sama da ƙasa sun shuɗe, babu ko ɗan wasali, babu wani ɗigo ta kowace hanya da zai ɓace daga Dokar, sai an cika kome. 19Duk wanda ya karya ɗaya daga cikin mafi ƙanƙanta na umarnan nan, ya kuma koya wa waɗansu su yi haka, za a ce da shi mafi ƙanƙanta a mulkin sama. Amma duk wanda ya aikata, ya kuma koyar da waɗannan umarnai, za a kira shi mai girma a cikin mulkin sama. 20Gama ina faɗa muku cewa in dai adalcinku bai fi na Farisiyawa da na malaman dokoki ba, faufau, ba za ku shiga mulkin sama ba.

Kisankai

21“Kun dai ji an faɗa wa mutanen dā cewa, ‘Kada ka yi kisankai;5.21 Fit 20.13 kuma duk wanda ya yi kisankai za a hukunta shi.’ 22Amma ina gaya muku, duk wanda ya yi fushi da ɗan’uwansa, za a hukunta shi. Kuma duk wanda ya ce wa ɗan’uwansa ‘Raka,’5.22 Kalmar Arameyik ta reni za a kai shi gaban Majalisa. Amma duk wanda ya ce, ‘Kai wawa!’ Zai kasance a hatsarin shiga jahannama ta wuta.

23“Saboda haka, in kana cikin ba da baikonka a kan bagade, a can kuwa ka tuna cewa ɗan’uwanka yana riƙe da kai a zuci, 24sai ka bar baikonka a can gaban bagade. Ka je ka shirya tukuna da ɗan’uwanka; sa’an nan ka zo ka ba da baikonka.

25“Ka yi hanzari ka shirya al’amura da maƙiyinka wanda yake ƙararka a kotu. Ka yi haka, tun kana tare da shi a kan hanya, in ba haka ba, zai miƙa ka ga alƙali, alƙali kuma yă miƙa ka ga ɗan sanda, mai yiwuwa kuwa a jefa ka a kurkuku. 26Gaskiya nake gaya maka, ba za ka fita ba, sai ka biya kobo na ƙarshe.

Zina

27“Kun dai ji an faɗa, ‘Kada ka yi zina.’5.27 Fit 20.14 28Amma ina gaya muku, duk wanda ya dubi mace, sa’an nan ya yi sha’awarta a zuci, ya riga ya yi zina ke nan da ita a zuciyarsa. 29In idonka na dama yana sa ka yin zunubi, ƙwaƙule shi ka yar. Zai fiye maka ka rasa ɗaya daga cikin gaɓoɓin jikinka, da a jefa jikinka ɗungum a cikin jahannama ta wuta. 30In kuma hannunka na dama yana sa ka yin zunubi, yanke shi ka yar. Zai fiye maka ka rasa ɗaya daga cikin gaɓoɓin jikinka, da a jefa jikinka ɗungum a cikin jahannama ta wuta.

Kashen aure

(Mattiyu 19.9; Markus 10.11,12; Luka 16.18)

31“An kuma faɗa, ‘Duk wanda ya saki matarsa, dole yă ba ta takardar saki.’5.31 M Sh 24.1 32Amma ina gaya muku, duk wanda ya saki matarsa in ba a kan laifin zina ba, ya sa ta zama mazinaciya ke nan, kuma duk wanda ya auri macen da mijinta ya sake, shi ma yana zina ne.

Rantsuwa

33“Har wa yau dai kun ji an faɗa wa mutane a dā, ‘Kada ka karya alkawarinka, sai dai ka cika alkawaran da ka yi wa Ubangiji.’ 34Amma ina gaya muku, Kada ku yi rantsuwa sam, ko da sama, domin kursiyin Allah ne; 35ko da ƙasa, domin matashin ƙafafunsa ne; ko kuma da Urushalima, domin birnin Babban Sarki ne. 36Kada kuma ka rantse da kanka, domin ba za ka iya mai da ko gashi ɗaya yă zama fari ko baƙi ba. 37Abin da ya kamata ku ce kawai, shi ne, I, ko A’a. Abin da ya wuce haka kuwa daga wurin Mugun nan yake.

Ramuwa

(Luka 6.29,30)

38“Kun dai ji an faɗa, ‘Ido domin ido, haƙori kuma domin haƙori.’5.38 Fit 21.24; Fir 24.20; M Sh 19.21 39Amma ina gaya muku, Kada ku yi tsayayya da mugun mutum. In wani ya mare ka a kumatun dama, juya masa ɗayan ma. 40In kuma wani yana so yă yi ƙararka yă ƙwace rigarka, to, ba shi mayafinka ma. 41In wani ya tilasta ka yin tafiya mil ɗaya, to, tafi tare da shi mil biyu. 42Ka ba wa duk wanda ya roƙe ka abu, kada kuma ka hana wa wanda yake neman bashi daga gare ka.

Ƙauna don abokan gāba

(Luka 6.27,28,32-36)

43“Kun dai ji an faɗa, ‘Ka ƙaunaci maƙwabcinka,5.43 Fir 19.18 ka kuma ƙi abokin gābanka.’ 44Amma ina gaya muku, ku ƙaunaci abokan gābanku5.44 Waɗansu rubuce-rubucen hannun da ba su jima ba suna da abokan gāba, ku sa wa waɗanda suke la’antarku albarka, ku yi wa waɗanda suke ƙinku alheri kuma ku yi wa waɗanda suke tsananta muku addu’a, 45don ku zama ’ya’yan Ubanku na sama. Shi yakan sa ranarsa ta haskaka a kan mugaye da masu kirki; yakan kuma sako ruwan sama a bisa masu adalci da marasa adalci. 46In masoyarku kawai kuke ƙauna, wace lada ce gare ku? Ko masu karɓar haraji ma ba haka suke yi ba? 47In kuwa kuna gai da ’yan’uwanku ne kaɗai, me kuke yi fiye da waɗansu? Marasa bin Allah ma ba haka suke yi ba? 48Saboda haka sai ku zama cikakku, yadda Ubanku na sama yake cikakke.

Slovo na cestu

Matouš 5:1-48

Ježíš vyslovuje blahoslavenství

1Když Ježíš uviděl zástupy lidí, vystoupil se svými učedníky na návrší, posadil se v jejich středu 2a učil je:

3„Kteří lidé jsou skutečně šťastni?

Šťastni jsou pokorní, nenamyšlení,

vždyť těm patří Boží království.

4Šťastni jsou ti, kteří pláčou v zármutku,

vždyť Bůh je potěší.

5Šťastni jsou ti, kteří pro sebe nic nevymáhají,

vždyť jim Bůh dá celou zemi.

6Šťastni jsou ti, kteří touží po tom, co je správné,

jako žízniví po vodě,

vždyť jejich žízeň bude utišena.

7Šťastni jsou milosrdní,

vždyť Bůh k nim bude také milosrdný.

8Šťastni jsou ti, kteří si zachovali čistý pohled naživot,

vždyť oni uvidí Boha.

9Šťastni jsou ti, kteří působí pokoj,

vždyť k těm se Bůh bude hlásit jako ke svým dětem.

10Šťastni jsou ti, kteří mají těžkosti proto,

že poslouchají Boha;

jim se otevírá Boží svět.

11Šťastni jste, když vámi kvůli mně pohrdají, pronásledují vás a vymýšlejí si na vás pomluvy. 12Máte důvod k radosti a dokonce i k veselí, neboť co vás čeká v nebi, mnohonásobně převýší vaše utrpení. Ostatně takhle zacházeli s Božími lidmi vždycky.

Ježíš učí o soli a světle

13Vy jste sůl země. Když už sůl by měla ztratit svoji chuť, čím se bude solit? Sůl bez chuti se nehodí k ničemu a může být jen vyhozena a zašlapána.

14Vy jste světlo světa. Město postavené na hoře je odevšad vidět. 15Také svíčku nerozsvěcujete proto, abyste ji schovali, ale stavíte ji na svícen, aby svítila každému v domě. 16Tak ať svítí vaše světlo všem lidem; ať za vašimi dobrými činy vidí Boha a jeho chválí.

Ježíš učí o zákonu

17Nemyslete si, že jsem přišel proto, abych zrušil, co bylo přikázáno a předpověděno ve Starém zákoně. Naopak, přišel jsem, abych to všechno uskutečnil a dovršil. 18Ujišťuji vás, že dokud trvá nebe a země, ani písmenko nebo čárka z toho, co Bůh přikázal, neztratí svou platnost, dokud se nenaplní. 19A proto každý, kdo by nebral vážně i to nejmenší přikázání a vedl by tak lidi, bude poslední v Božím království. Ale ten, kdo se Božími příkazy řídí a učí tak druhé, bude velký v nebeském království. 20Pamatujte si: chcete-li vejít do nebeského království, musí vám jít o víc než jen o formální plnění příkazů a zákazů, jako to činí učitelé zákona a farizejové.

Ježíš učí o hněvu

21V Desateru stojí psáno: Nezabiješ. Proto kdo zabil, musí před soud. 22Ale já vám říkám, že bude souzen každý, kdo se hněvá na svého bližního. Pohrdání člověkem je zločin, a kdo svolává na druhého Boží trest, sám mu propadne.

23Dáváš-li do pořádku svůj vztah k Bohu a uvědomíš si, že máš s někým nesrovnalost, 24-26odstraň ji a smiř se s ním. Teprve potom předstup před Boha. Nejsi-li ochoten ke smíru s druhým člověkem, bude na tebe žalovat tvůj hněv před Bohem a neunikneš odsouzení. Je to tak, jako když tě věřitel vede k soudci. Nedomluvíš-li se s ním cestou, půjdeš do vězení a celý dluh si odpykáš.

Ježíš učí o smyslnosti

27Znáte další přikázání Desatera: Nebudeš cizoložit. 28Já vám však říkám, kdo by se podíval žádostivě na jinou ženu, porušil manželství, byť jenom v myšlenkách.

29-30Učiň všechno pro to, aby k tobě pokušení nepronikalo. Neboj se zříci se něčeho, co se ti dnes zdá pro tvůj život tak nepostradatelné jako oko nebo pravá ruka. Lépe je žít s jedním okem nebo jednou rukou než ztratit věčný život.

Ježíš učí o rozvodu

31Mojžíšův zákon připouští, aby se muž se ženou rozvedl, musí jí to však dát písemně. 32Já však říkám, že kdo se rozvádí se svojí ženou, aniž mu byla nevěrná, sám ji uvádí do nevěry. Kdo se ožení s takovou ženou, cizoloží.

Ježíš učí o přísaze

33A další přikázání: Nepřísahej křivě, ale splň své přísahy jako dané Pánu Bohu! 34Já vám však říkám: Nepřísahejte vůbec; neberte si za svědka nebe, protože je Božím trůnem; 35nedovolávejte se ničeho na zemi, protože je jeho podnoží. Nepřísahejte ani při posvátném Jeruzalému, protože je městem velikého Krále. 36Nepřísahejte ani při své hlavě, protože není ve vaší moci, aby vám rostly bílé nebo černé vlasy. 37Říkejte prostě ano, nebo ne. To stačí. Když zdůrazňujete svoje slova přísahou, dokazujete, že nemluvíte vždycky pravdu a každá lež pochází od zlého.

Ježíš učí o odplatě

38Je také psáno: Oko za oko, zub za zub. 39Já vám říkám, abyste neodpláceli zlým za zlé. Naopak, uhodí-li tě někdo přes pravou tvář, nastav mu i levou. 40A když by se s tebou chtěl někdo soudit a vzít ti šaty, dej mu i kabát; 41jestliže tě někdo nutí, abys s ním šel kus cesty, jdi s ním dvakrát tak daleko. 42Dej tomu, kdo tě prosí, a neodmítej toho, kdo si chce od tebe vypůjčit.

Ježíš učí o milování nepřátel

43A dále bylo řečeno: Miluj přítele a měj v nenávisti svého nepřítele! 44-45Ale já vám říkám: milujte své nepřátele, modlete se za ty, kteří vás pronásledují. Tak budete dělat čest svému Otci v nebi. On dovoluje, aby slunce svítilo na zlé i dobré, a déšť sesílá na ty, kdo ho ctí, i na ty, kdo jím pohrdají. 46Jakou máte zásluhu, když projevujete lásku těm, kteří vám ji oplácejí? Copak to nedokážou i sobci? 47A chováte-li se přátelsky jen ke svým blízkým, co děláte zvláštního? Na to ještě nemusíte věřit v Boha. 48Nevymlouvejte se na hranice svých možností, ale buďte tak dokonalí v lásce, jako je váš nebeský Otec.