Mattiyu 4 – HCB & OL

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 4:1-25

Gwajin Yesu

(Markus 1.12,13; Luka 4.1-13)

1Sa’an nan Ruhu ya kai Yesu cikin hamada don Iblis yă gwada shi. 2Bayan ya yi azumi yini arba’in da kuma dare arba’in, sai ya ji yunwa. 3Sai mai gwajin ya zo wurinsa ya ce, “In kai Ɗan Allah ne, ka ce wa duwatsun nan su zama burodi.”

4Yesu ya amsa ya ce, “A rubuce yake cewa, ‘Ba da abinci kaɗai mutum yake rayuwa ba, sai dai da kowace kalmar da take fitowa daga bakin Allah.’4.4 M Sh 8.3

5Sai Iblis ya kai shi birni mai tsarki, ya kai shi can wuri mafi tsayi duka na haikali. 6Ya ce, “In kai Ɗan Allah ne, yi tsalle ka sauka ƙasa. Gama a rubuce yake,

“ ‘Zai umarci mala’ikunsa game da kai,

za su tallafe ka da hannuwansu,

don kada ka buga ƙafarka a kan dutse.’4.6 Zab 91.11,12

7Yesu ya amsa masa ya ce, “A rubuce yake kuma cewa, ‘Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.’4.7 M Sh 6.16

8Har wa yau, Iblis ya kai shi bisa wani dutse mai tsawo sosai, ya nunnuna masa dukan mulkokin duniya da darajarsu. 9Ya ce, “Zan ba ka dukan wannan, in za ka durƙusa ka yi mini sujada.”

10Sai Yesu ya ce masa, “Rabu da ni, Shaiɗan! Gama a rubuce yake, ‘Yi wa Ubangiji Allahnka sujada, shi kaɗai kuma za ka bauta wa.’4.10 M Sh 6.13

11Sa’an nan Iblis ya bar shi, mala’iku kuwa suka zo suka yi masa hidima.

Yesu ya fara wa’azi

(Markus 1.14,15; Luka 4.14,15)

12Da Yesu ya ji labari cewa an kulle Yohanna a kurkuku, sai ya koma zuwa Galili. 13Ya bar Nazaret, ya je ya zauna a Kafarnahum, wadda take a bakin tafki wajen Zebulun da Naftali 14don a cika abin da aka faɗa ta bakin annabi Ishaya cewa,

15“Ƙasar Zebulun da ƙasar Naftali,

da kuke a hanyar zuwa tekun Galili, a ƙetaren Urdun,

wannan yankin Galili ta Al’ummai,

16mutanen da suke zama cikin duhu

sun ga babban haske;

haske kuma ya haskaka

a kan waɗanda suke zama a inuwar mutuwa.”4.16 Ish 9.1,2f

17Tun daga wannan lokaci, Yesu ya fara wa’azi yana cewa, “Ku tuba, gama mulkin sama ya yi kusa.”

Kiran almajirai na farko

(Markus 1.16-20; Luka 5.1-11)

18Da Yesu yana kan tafiya a bakin Tekun Galili, sai ya ga waɗansu ’yan’uwa guda biyu, Siman wanda ake kira Bitrus da ɗan’uwansa Andarawus. Suna jefa abin kamun kifi a tafki, gama su masunta ne. 19Sai Yesu ya ce, “Zo, ku bi ni, ni kuwa zan mai da ku masu jan mutane zuwa wurina.” 20Nan da nan suka bar abin kamun kifinsu suka bi shi.

21Da ya ci gaba daga nan, sai ya ga waɗansu ’yan’uwa guda biyu, Yaƙub ɗan Zebedi da ɗan’uwansa Yohanna. Suna cikin jirgin ruwa tare da mahaifinsu Zebedi, suna shirya abin kamun kifinsu. Yesu ya kira su, 22nan take suka bar jirgin ruwan da mahaifinsu suka kuwa bi Yesu.

Yesu ya warkar da marasa lafiya

(Luka 6.17-19)

23Yesu ya zazzaga dukan Galili, yana koyarwa a cikin majami’unsu, yana wa’azin labari mai daɗi na mulkin sama, yana kuma warkar da kowace cuta da rashin lafiyar mutane. 24Labarinsa ya bazu ko’ina a Suriya, mutane kuwa suka kawo masa dukan waɗanda suke fama da cututtuka iri-iri, da waɗanda suke da zafin ciwo, da masu aljanu, da waɗanda suke masu farfaɗiya, da shanyayyu, ya kuwa warkar da su. 25Taron mutane mai yawa daga Galili, Dekafolis,4.25 Wato, Birane Goma Urushalima, Yahudiya da kuma yankin hayin Urdun suka bi shi.

O Livro

Mateus 4:1-25

Jesus é tentado

(Mc 1.12-13; Lc 4.1-13)

1Depois disto, Jesus foi levado pelo Espírito Santo ao deserto para ser tentado pelo Diabo. 2Durante quarenta dias e quarenta noites nada comeu; por fim, sentiu fome. 3Então o Tentador instigou-o a arranjar alimento, dizendo: “Se és o Filho de Deus, manda a estas pedras que se transformem em pão.”

4Mas Jesus respondeu: “Não! Porque as Escrituras dizem:

‘Nem só de pão viverá o homem,

mas de toda a palavra que sai da boca de Deus.’ ”4.4 Dt 8.3.

5Depois o Diabo levou-o à cidade santa4.5 O texto refere-se a Jerusalém., ao telhado do templo: 6“Se és o Filho de Deus, salta! Pois, segundo as Escrituras:

‘Deus dará ordens aos seus anjos a teu respeito.

Eles te susterão com as suas mãos,

para que não tropeces nas pedras do caminho.’ ”4.6 Sl 91.11-12.

7Jesus retorquiu-lhe: “Mas as Escrituras também dizem:

‘Não deves provocar o Senhor, teu Deus.’ ”4.7 Dt 6.16.

8Por fim, o Diabo levou-o a um monte muito alto e mostrou-lhe todos os reinos do mundo e a sua glória: 9“Tudo isto te darei se te ajoelhares e me adorares.”

10“Vai-te, Satanás! As Escrituras dizem:

‘Adorarás o Senhor, teu Deus. Só a ele servirás.’ ”4.10 Dt 6.13.

11Então o Diabo foi-se embora e os anjos vieram e serviam-no.

Jesus começa a pregar

(Mc 1.14-15; Lc 4.14-15)

12Quando Jesus soube que João tinha sido preso, saiu da Judeia e voltou para casa, em Nazaré na Galileia. 13Porém, cedo deixou Nazaré e mudou-se para Cafarnaum, junto ao mar da Galileia, perto de Zebulão e Naftali. 14Assim, cumpriu-se a profecia de Isaías:

15“A terra de Zebulão e de Naftali,

uma estrada para o mar, além do Jordão,

na Galileia onde vivem tantos gentios,

16o povo que anda nas trevas viu uma grande luz,

uma luz que brilhou sobre todos os

que vivem na terra da sombra da morte.”4.16 Is 9.1-2.

17Dali em diante, Jesus começou a pregar: “Deixem os vossos pecados e voltem-se para Deus, pois o reino dos céus está próximo.”

A chamada dos primeiros discípulos

(Mc 1.16-20; Lc 5.2-11)

18Certo dia, caminhando ao longo da costa do mar da Galileia, Jesus viu dois irmãos; Simão, também chamado Pedro, e André, que num barco pescavam com uma rede, pois eram pescadores por ofício. 19Então chamou-os: “Venham e sigam-me. Farei de vocês pescadores de pessoas!” 20No mesmo instante, deixaram as redes e seguiram-no.

21Avançando dali, viu na praia outros dois irmãos, Tiago e João, num barco a remendar as redes, na companhia de Zebedeu seu pai. Também chamou estes para o seguirem. 22Logo pararam o trabalho e, deixando o pai, foram com Jesus.

Jesus cura os enfermos

(Mc 3.7-12; Lc 6.17-19)

23Jesus andava por toda a Galileia ensinando nas sinagogas e pregando as boas novas do reino dos céus. E curava toda a casta de doenças e enfermidades entre o povo. 24A fama dos seus milagres espalhou-se para lá dos limites da Galileia, de tal modo que em breve começaram a aparecer muitos enfermos em busca de cura, vindo mesmo de regiões tão distantes como a Síria. Qualquer que fosse a doença ou mal, mesmo os possessos dos demónios, os loucos e os paralíticos, a todos curava. 25Multidões enormes seguiam-no, vindas da Galileia, das Dez Cidades, de Jerusalém e da Judeia, e até do outro lado do Jordão.