Mattiyu 4 – HCB & NRT

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 4:1-25

Gwajin Yesu

(Markus 1.12,13; Luka 4.1-13)

1Sa’an nan Ruhu ya kai Yesu cikin hamada don Iblis yă gwada shi. 2Bayan ya yi azumi yini arba’in da kuma dare arba’in, sai ya ji yunwa. 3Sai mai gwajin ya zo wurinsa ya ce, “In kai Ɗan Allah ne, ka ce wa duwatsun nan su zama burodi.”

4Yesu ya amsa ya ce, “A rubuce yake cewa, ‘Ba da abinci kaɗai mutum yake rayuwa ba, sai dai da kowace kalmar da take fitowa daga bakin Allah.’4.4 M Sh 8.3

5Sai Iblis ya kai shi birni mai tsarki, ya kai shi can wuri mafi tsayi duka na haikali. 6Ya ce, “In kai Ɗan Allah ne, yi tsalle ka sauka ƙasa. Gama a rubuce yake,

“ ‘Zai umarci mala’ikunsa game da kai,

za su tallafe ka da hannuwansu,

don kada ka buga ƙafarka a kan dutse.’4.6 Zab 91.11,12

7Yesu ya amsa masa ya ce, “A rubuce yake kuma cewa, ‘Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.’4.7 M Sh 6.16

8Har wa yau, Iblis ya kai shi bisa wani dutse mai tsawo sosai, ya nunnuna masa dukan mulkokin duniya da darajarsu. 9Ya ce, “Zan ba ka dukan wannan, in za ka durƙusa ka yi mini sujada.”

10Sai Yesu ya ce masa, “Rabu da ni, Shaiɗan! Gama a rubuce yake, ‘Yi wa Ubangiji Allahnka sujada, shi kaɗai kuma za ka bauta wa.’4.10 M Sh 6.13

11Sa’an nan Iblis ya bar shi, mala’iku kuwa suka zo suka yi masa hidima.

Yesu ya fara wa’azi

(Markus 1.14,15; Luka 4.14,15)

12Da Yesu ya ji labari cewa an kulle Yohanna a kurkuku, sai ya koma zuwa Galili. 13Ya bar Nazaret, ya je ya zauna a Kafarnahum, wadda take a bakin tafki wajen Zebulun da Naftali 14don a cika abin da aka faɗa ta bakin annabi Ishaya cewa,

15“Ƙasar Zebulun da ƙasar Naftali,

da kuke a hanyar zuwa tekun Galili, a ƙetaren Urdun,

wannan yankin Galili ta Al’ummai,

16mutanen da suke zama cikin duhu

sun ga babban haske;

haske kuma ya haskaka

a kan waɗanda suke zama a inuwar mutuwa.”4.16 Ish 9.1,2f

17Tun daga wannan lokaci, Yesu ya fara wa’azi yana cewa, “Ku tuba, gama mulkin sama ya yi kusa.”

Kiran almajirai na farko

(Markus 1.16-20; Luka 5.1-11)

18Da Yesu yana kan tafiya a bakin Tekun Galili, sai ya ga waɗansu ’yan’uwa guda biyu, Siman wanda ake kira Bitrus da ɗan’uwansa Andarawus. Suna jefa abin kamun kifi a tafki, gama su masunta ne. 19Sai Yesu ya ce, “Zo, ku bi ni, ni kuwa zan mai da ku masu jan mutane zuwa wurina.” 20Nan da nan suka bar abin kamun kifinsu suka bi shi.

21Da ya ci gaba daga nan, sai ya ga waɗansu ’yan’uwa guda biyu, Yaƙub ɗan Zebedi da ɗan’uwansa Yohanna. Suna cikin jirgin ruwa tare da mahaifinsu Zebedi, suna shirya abin kamun kifinsu. Yesu ya kira su, 22nan take suka bar jirgin ruwan da mahaifinsu suka kuwa bi Yesu.

Yesu ya warkar da marasa lafiya

(Luka 6.17-19)

23Yesu ya zazzaga dukan Galili, yana koyarwa a cikin majami’unsu, yana wa’azin labari mai daɗi na mulkin sama, yana kuma warkar da kowace cuta da rashin lafiyar mutane. 24Labarinsa ya bazu ko’ina a Suriya, mutane kuwa suka kawo masa dukan waɗanda suke fama da cututtuka iri-iri, da waɗanda suke da zafin ciwo, da masu aljanu, da waɗanda suke masu farfaɗiya, da shanyayyu, ya kuwa warkar da su. 25Taron mutane mai yawa daga Galili, Dekafolis,4.25 Wato, Birane Goma Urushalima, Yahudiya da kuma yankin hayin Urdun suka bi shi.

New Russian Translation

Матфея 4:1-25

Искушения Иисуса

(Мк. 1:12-13; Лк. 4:1-13)

1Затем Дух повел Иисуса в пустыню для того, чтобы Ему пройти искушение от дьявола. 2После сорока дней и сорока ночей, проведенных в посте, Иисус почувствовал сильный голод. 3Тогда искуситель подошел и сказал Ему:

– Если Ты Сын Божий, то прикажи этим камням стать хлебом.

4Но Иисус ответил:

– Написано: «Не одним хлебом живет человек, но и каждым словом, исходящим из уст Божьих»4:4 Втор. 8:3..

5Затем дьявол поставил Иисуса на самый верх храма святого города.

6– Если Ты Сын Божий, – сказал он Ему, – то бросься вниз. Ведь написано же:

«Своим ангелам повелит о Тебе»,

и «они понесут Тебя на руках,

чтобы ноги Твои не ударились о камень»4:6 Пс. 90:11-12..

7Иисус ответил ему:

– Написано также: «Не испытывай Господа, Бога твоего».

8Тогда дьявол привел Его на очень высокую гору и показал Ему все царства мира во всем их блеске.

9И он сказал Ему:

– Все это я передам Тебе, если Ты падешь и поклонишься мне!

10Тогда Иисус ответил ему:

– Прочь от Меня, сатана! Ведь написано: «Поклоняйся Господу, Богу твоему, и служи Ему одному!»4:10 Втор. 6:13.

11Тогда дьявол оставил Его, а к Иисусу приступили ангелы и служили Ему.

Начало служения в Галилее

(Мк. 1:14-15; Лк. 4:14-15)

12Когда Иисус услышал о том, что Иоанна заключили в темницу, Он возвратился в Галилею. 13Покинув Назарет, Он поселился в Капернауме, который расположен на берегу озера в земле, принадлежавшей родам Завулона и Неффалима. 14Так исполнилось пророчество Исаии:

15«Земля Завулона и земля Неффалима,

на пути к морю, за Иорданом,

Галилея языческая!

16Народ, живущий во тьме,

увидел великий свет,

и на живущих в стране смертной тени

воссиял свет»4:15-16 Ис. 9:1-2..

17С этого времени Иисус начал проповедовать:

– Покайтесь, потому что Царство Небесное уже близко!

Первые ученики

(Мк. 1:16-20; Лк. 5:2-11; Ин. 1:35-42)

18Однажды, проходя вдоль Галилейского озера, Иисус увидел двух братьев: Симона, прозванного Петром, и его брата Андрея. Они забрасывали в озеро сети, так как были рыбаками.

19– Идите за Мной, – сказал им Иисус, – и Я сделаю вас ловцами людей.

20Братья сразу же оставили сети и пошли за Ним.

21Пройдя дальше, Иисус увидел двух других братьев: Иакова, сына Зеведея, и его брата Иоанна. Они были в лодке со своим отцом Зеведеем и чинили свои сети. Иисус позвал и их. 22Они сразу же, оставив лодку и отца, пошли за Ним.

Служение Иисуса народу

(Мк. 3:7-12; Лк. 6:17-19)

23Иисус ходил по всей Галилее и учил в синагогах, проповедовал о Царстве и исцелял людей от всех болезней и недугов. 24Слух о Нем распространился по всей Сирии, и к Нему приносили страдающих от самых различных болезней, испытывающих сильные боли, одержимых демонами, людей, подверженных припадкам, парализованных, и Он их исцелял. 25За Ним следовали большие толпы людей из Галилеи, Десятиградия, Иерусалима, Иудеи и из-за реки Иордана.