Mattiyu 4 – HCB & NIRV

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 4:1-25

Gwajin Yesu

(Markus 1.12,13; Luka 4.1-13)

1Sa’an nan Ruhu ya kai Yesu cikin hamada don Iblis yă gwada shi. 2Bayan ya yi azumi yini arba’in da kuma dare arba’in, sai ya ji yunwa. 3Sai mai gwajin ya zo wurinsa ya ce, “In kai Ɗan Allah ne, ka ce wa duwatsun nan su zama burodi.”

4Yesu ya amsa ya ce, “A rubuce yake cewa, ‘Ba da abinci kaɗai mutum yake rayuwa ba, sai dai da kowace kalmar da take fitowa daga bakin Allah.’4.4 M Sh 8.3

5Sai Iblis ya kai shi birni mai tsarki, ya kai shi can wuri mafi tsayi duka na haikali. 6Ya ce, “In kai Ɗan Allah ne, yi tsalle ka sauka ƙasa. Gama a rubuce yake,

“ ‘Zai umarci mala’ikunsa game da kai,

za su tallafe ka da hannuwansu,

don kada ka buga ƙafarka a kan dutse.’4.6 Zab 91.11,12

7Yesu ya amsa masa ya ce, “A rubuce yake kuma cewa, ‘Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.’4.7 M Sh 6.16

8Har wa yau, Iblis ya kai shi bisa wani dutse mai tsawo sosai, ya nunnuna masa dukan mulkokin duniya da darajarsu. 9Ya ce, “Zan ba ka dukan wannan, in za ka durƙusa ka yi mini sujada.”

10Sai Yesu ya ce masa, “Rabu da ni, Shaiɗan! Gama a rubuce yake, ‘Yi wa Ubangiji Allahnka sujada, shi kaɗai kuma za ka bauta wa.’4.10 M Sh 6.13

11Sa’an nan Iblis ya bar shi, mala’iku kuwa suka zo suka yi masa hidima.

Yesu ya fara wa’azi

(Markus 1.14,15; Luka 4.14,15)

12Da Yesu ya ji labari cewa an kulle Yohanna a kurkuku, sai ya koma zuwa Galili. 13Ya bar Nazaret, ya je ya zauna a Kafarnahum, wadda take a bakin tafki wajen Zebulun da Naftali 14don a cika abin da aka faɗa ta bakin annabi Ishaya cewa,

15“Ƙasar Zebulun da ƙasar Naftali,

da kuke a hanyar zuwa tekun Galili, a ƙetaren Urdun,

wannan yankin Galili ta Al’ummai,

16mutanen da suke zama cikin duhu

sun ga babban haske;

haske kuma ya haskaka

a kan waɗanda suke zama a inuwar mutuwa.”4.16 Ish 9.1,2f

17Tun daga wannan lokaci, Yesu ya fara wa’azi yana cewa, “Ku tuba, gama mulkin sama ya yi kusa.”

Kiran almajirai na farko

(Markus 1.16-20; Luka 5.1-11)

18Da Yesu yana kan tafiya a bakin Tekun Galili, sai ya ga waɗansu ’yan’uwa guda biyu, Siman wanda ake kira Bitrus da ɗan’uwansa Andarawus. Suna jefa abin kamun kifi a tafki, gama su masunta ne. 19Sai Yesu ya ce, “Zo, ku bi ni, ni kuwa zan mai da ku masu jan mutane zuwa wurina.” 20Nan da nan suka bar abin kamun kifinsu suka bi shi.

21Da ya ci gaba daga nan, sai ya ga waɗansu ’yan’uwa guda biyu, Yaƙub ɗan Zebedi da ɗan’uwansa Yohanna. Suna cikin jirgin ruwa tare da mahaifinsu Zebedi, suna shirya abin kamun kifinsu. Yesu ya kira su, 22nan take suka bar jirgin ruwan da mahaifinsu suka kuwa bi Yesu.

Yesu ya warkar da marasa lafiya

(Luka 6.17-19)

23Yesu ya zazzaga dukan Galili, yana koyarwa a cikin majami’unsu, yana wa’azin labari mai daɗi na mulkin sama, yana kuma warkar da kowace cuta da rashin lafiyar mutane. 24Labarinsa ya bazu ko’ina a Suriya, mutane kuwa suka kawo masa dukan waɗanda suke fama da cututtuka iri-iri, da waɗanda suke da zafin ciwo, da masu aljanu, da waɗanda suke masu farfaɗiya, da shanyayyu, ya kuwa warkar da su. 25Taron mutane mai yawa daga Galili, Dekafolis,4.25 Wato, Birane Goma Urushalima, Yahudiya da kuma yankin hayin Urdun suka bi shi.

New International Reader’s Version

Matthew 4:1-25

Jesus Is Tempted in the Desert

1The Holy Spirit led Jesus into the desert. There the devil tempted him. 2After 40 days and 40 nights of going without eating, Jesus was hungry. 3The tempter came to him. He said, “If you are the Son of God, tell these stones to become bread.”

4Jesus answered, “It is written, ‘Man must not live only on bread. He must also live on every word that comes from the mouth of God.’ ” (Deuteronomy 8:3)

5Then the devil took Jesus to the holy city. He had him stand on the highest point of the temple. 6“If you are the Son of God,” he said, “throw yourself down. It is written,

“ ‘The Lord will command his angels to take good care of you.

They will lift you up in their hands.

Then you won’t trip over a stone.’ ” (Psalm 91:11,12)

7Jesus answered him, “It is also written, ‘Do not test the Lord your God.’ ” (Deuteronomy 6:16)

8Finally, the devil took Jesus to a very high mountain. He showed him all the kingdoms of the world and their glory. 9“If you bow down and worship me,” he said, “I will give you all this.”

10Jesus said to him, “Get away from me, Satan! It is written, ‘Worship the Lord your God. He is the only one you should serve.’ ” (Deuteronomy 6:13)

11Then the devil left Jesus. Angels came and took care of him.

Jesus Begins to Preach

12John had been put in prison. When Jesus heard about this, he returned to Galilee. 13Jesus left Nazareth and went to live in the city of Capernaum. It was by the lake in the area of Zebulun and Naphtali. 14In that way, what the prophet Isaiah had said came true. He had said,

15“Land of Zebulun! Land of Naphtali!

Galilee, where Gentiles live!

Land along the Mediterranean Sea! Territory east of the Jordan River!

16The people who are now living in darkness

have seen a great light.

They are now living in a very dark land.

But a light has shined on them.” (Isaiah 9:1,2)

17From that time on Jesus began to preach. “Turn away from your sins!” he said. “The kingdom of heaven has come near.”

Jesus Chooses His First Disciples

18One day Jesus was walking beside the Sea of Galilee. There he saw two brothers, Simon Peter and his brother Andrew. They were throwing a net into the lake, because they were fishermen. 19“Come and follow me,” Jesus said. “I will send you out to fish for people.” 20At once they left their nets and followed him.

21Going on from there, he saw two other brothers. They were James, son of Zebedee, and his brother John. They were in a boat with their father Zebedee. As they were preparing their nets, Jesus called out to them. 22Right away they left the boat and their father and followed Jesus.

Jesus Heals Sick People

23Jesus went all over Galilee. There he taught in the synagogues. He preached the good news of God’s kingdom. He healed every illness and sickness the people had. 24News about him spread all over Syria. People brought to him all who were ill with different kinds of sicknesses. Some were suffering great pain. Others were controlled by demons. Some were shaking wildly. Others couldn’t move at all. And Jesus healed all of them. 25Large crowds followed him. People came from Galilee, from the area known as the Ten Cities, and from Jerusalem and Judea. Others came from the area across the Jordan River.