Mattiyu 28 – HCB & CCB

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 28:1-20

Yesu ya tashi daga matattu

(Markus 16.1-8; Luka 24.1-12; Yohanna 20.1-10)

1Bayan ranar Asabbaci, da sassafe, a ranar farko ta mako, Maryamu Magdalin tare da ɗaya Maryamun, suka je don su ga kabarin.

2Sai aka yi wata babbar girgizar ƙasa. Don wani mala’ikan Ubangiji ya sauka daga sama, ya je kabarin, ya gungurar da dutsen, ya kuma zauna a kai. 3Kamanninsa yana kama da walƙiya, tufafinsa kuma fari fat kamar dusan ƙanƙara. 4Masu gadin kabarin kuma suka ji tsoro ƙwarai, suka yi rawan jiki, suka zama kamar matattu.

5Mala’ikan ya ce wa matan, “Kada ku ji tsoro, domin na san cewa kuna neman Yesu wanda aka gicciye ne. 6Ai, ba ya nan, ya tashi kamar yadda ya faɗa. Ku zo ku ga inda ya kwanta. 7Sai ku tafi da sauri ku gaya wa almajiransa cewa, ‘Ya tashi daga matattu, ya kuma ya sha gabanku zuwa Galili. Can za ku gan shi.’ Ga shi na faɗa muku.”

8Sai matan suka bar kabarin da hanzari, da tsoro, sai dai cike da farin ciki, suka tafi a guje don su gaya wa almajiransa. 9Kwaram, sai ga Yesu ya gamu da su ya ce, “Gaisuwa.” Sai suka zo kusa da shi, suka rungumi ƙafafunsa, suka yi masa sujada. 10Sai Yesu ya ce musu, “Kada ku ji tsoro, ku tafi ku gaya wa ’yan’uwana, su tafi Galili. A can za su gan ni.”

Rahoton masu gadi

11Yayinda matan nan suna cikin tafiya, sai waɗansu daga cikin masu gadin suka shiga gari, suka ba wa manyan firistoci labarin duk abin da ya faru. 12Da manyan firistoci da dattawa suka taru, sai suka ƙulla wata dabara, suka ba wa sojojin kuɗi mai yawa. 13Suka ce musu, “Ku, za ku ce, ‘Almajiransa ne sun zo da dare suka sace shi, lokacin da muke barci.’ 14In wannan labari ya kai kunnen gwamna, za mu lallashe shi, mu kuma kāre ku daga duk wata wahala.” 15Sai sojojin suka karɓi kuɗin, suka kuma yi kamar yadda aka umarce su. Wannan labarin kuwa shi ne ake bazawa ko’ina a cikin Yahudawa, har yă zuwa yau.

Babban umarni

(Markus 16.14-18; Luka 24.36-49; Yohanna 20.19-23; Ayyukan Manzanni 1.6-8)

16Sa’an nan almajiransa goma sha ɗaya, suka tafi Galili, suka je dutsen da Yesu ya gaya musu. 17Da suka gan shi, sai suka yi masa sujada, amma waɗansu suka yi shakka. 18Sai Yesu ya zo wurinsu ya ce, “An ba ni dukan iko a sama da kuma ƙasa. 19Saboda haka ku tafi, ku mai da dukan al’umman duniya su zama almajiraina, kuna yi musu baftisma a cikin28.19 Ko kuwa cikin; dubi Ayy M 8.16; 19.5; Rom 6.3; 1Kor 1.13; 10.2 da Gal 3.27 sunan Uba, da na Ɗa, da na Ruhu Mai Tsarki, 20kuna kuma koya musu, su yi biyayya da duk abin da na umarce ku, kuma tabbatacce, ina tare da ku kullum, har ƙarshen zamani.”

Chinese Contemporary Bible (Simplified)

马太福音 28:1-20

耶稣复活

1安息日刚过,周日黎明时分,抹大拉玛丽亚和另一位玛丽亚一同到坟墓去察看。

2突然,大地剧烈地震动,上帝的天使从天而降,推开堵着墓穴的石头,坐在上面。 3他的容貌如闪电,衣裳洁白如雪。 4看守墓穴的卫兵吓得要死,浑身发抖。

5天使对那两个女人说:“不要怕,我知道你们是在找那位被钉十字架的耶稣。 6祂不在这里,正如祂所说的,祂已经复活了。你们来看,这是安放祂的地方。 7现在你们快回去,把这消息告诉祂的门徒,祂已经从死里复活,先你们一步去了加利利,你们将在那里见到祂。记住,我已经告诉你们了。”

8她们听了又惊又喜,连忙离开坟墓,跑去告诉门徒。 9忽然,耶稣迎面而来,对她们说:“愿你们平安!”她们就上前抱住祂的脚敬拜祂。

10耶稣对她们说:“不要害怕。去告诉我的弟兄,叫他们到加利利去,他们将在那里见到我。”

行贿造谣

11她们还在赶路的时候,有些守墓的卫兵已经进城把整件事告诉祭司长。 12祭司长和长老聚集商议,决定用重金买通守墓的卫兵,又吩咐他们: 13“你们就说,‘半夜里我们熟睡的时候,耶稣的门徒把祂的尸体偷走了。’ 14如果这件事传到总督那里,我们一定会替你们出面,保你们无事。” 15守卫收下钱,便依照吩咐去做。于是,这说法在犹太人中一直流传到今天。

大使命

16十一个门徒赶到加利利,到了耶稣和他们约定的山上, 17看到耶稣就敬拜祂,但有些人仍然心存疑惑。 18耶稣上前对门徒说:

“天上地下所有的权柄都交给我了。 19所以,你们要去使万民做我的门徒,奉父、子、圣灵的名给他们施洗, 20教导他们遵守我吩咐你们的一切。记住,我必常与你们同在,一直到世界的末了。”