Mattiyu 28 – HCB & CARSA

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 28:1-20

Yesu ya tashi daga matattu

(Markus 16.1-8; Luka 24.1-12; Yohanna 20.1-10)

1Bayan ranar Asabbaci, da sassafe, a ranar farko ta mako, Maryamu Magdalin tare da ɗaya Maryamun, suka je don su ga kabarin.

2Sai aka yi wata babbar girgizar ƙasa. Don wani mala’ikan Ubangiji ya sauka daga sama, ya je kabarin, ya gungurar da dutsen, ya kuma zauna a kai. 3Kamanninsa yana kama da walƙiya, tufafinsa kuma fari fat kamar dusan ƙanƙara. 4Masu gadin kabarin kuma suka ji tsoro ƙwarai, suka yi rawan jiki, suka zama kamar matattu.

5Mala’ikan ya ce wa matan, “Kada ku ji tsoro, domin na san cewa kuna neman Yesu wanda aka gicciye ne. 6Ai, ba ya nan, ya tashi kamar yadda ya faɗa. Ku zo ku ga inda ya kwanta. 7Sai ku tafi da sauri ku gaya wa almajiransa cewa, ‘Ya tashi daga matattu, ya kuma ya sha gabanku zuwa Galili. Can za ku gan shi.’ Ga shi na faɗa muku.”

8Sai matan suka bar kabarin da hanzari, da tsoro, sai dai cike da farin ciki, suka tafi a guje don su gaya wa almajiransa. 9Kwaram, sai ga Yesu ya gamu da su ya ce, “Gaisuwa.” Sai suka zo kusa da shi, suka rungumi ƙafafunsa, suka yi masa sujada. 10Sai Yesu ya ce musu, “Kada ku ji tsoro, ku tafi ku gaya wa ’yan’uwana, su tafi Galili. A can za su gan ni.”

Rahoton masu gadi

11Yayinda matan nan suna cikin tafiya, sai waɗansu daga cikin masu gadin suka shiga gari, suka ba wa manyan firistoci labarin duk abin da ya faru. 12Da manyan firistoci da dattawa suka taru, sai suka ƙulla wata dabara, suka ba wa sojojin kuɗi mai yawa. 13Suka ce musu, “Ku, za ku ce, ‘Almajiransa ne sun zo da dare suka sace shi, lokacin da muke barci.’ 14In wannan labari ya kai kunnen gwamna, za mu lallashe shi, mu kuma kāre ku daga duk wata wahala.” 15Sai sojojin suka karɓi kuɗin, suka kuma yi kamar yadda aka umarce su. Wannan labarin kuwa shi ne ake bazawa ko’ina a cikin Yahudawa, har yă zuwa yau.

Babban umarni

(Markus 16.14-18; Luka 24.36-49; Yohanna 20.19-23; Ayyukan Manzanni 1.6-8)

16Sa’an nan almajiransa goma sha ɗaya, suka tafi Galili, suka je dutsen da Yesu ya gaya musu. 17Da suka gan shi, sai suka yi masa sujada, amma waɗansu suka yi shakka. 18Sai Yesu ya zo wurinsu ya ce, “An ba ni dukan iko a sama da kuma ƙasa. 19Saboda haka ku tafi, ku mai da dukan al’umman duniya su zama almajiraina, kuna yi musu baftisma a cikin28.19 Ko kuwa cikin; dubi Ayy M 8.16; 19.5; Rom 6.3; 1Kor 1.13; 10.2 da Gal 3.27 sunan Uba, da na Ɗa, da na Ruhu Mai Tsarki, 20kuna kuma koya musu, su yi biyayya da duk abin da na umarce ku, kuma tabbatacce, ina tare da ku kullum, har ƙarshen zamani.”

Священное Писание (Восточный перевод), версия с «Аллахом»

Матай 28:1-20

Воскресение Исы аль-Масиха

(Мк. 16:1-8; Лк. 24:1-12; Ин. 20:1-18)

1После субботы, на рассвете первого дня недели28:1 У иудеев неделя начиналась с воскресенья., Марьям из Магдалы и другая Марьям пошли посмотреть на могильную пещеру. 2Вдруг произошло сильное землетрясение, потому что ангел от Вечного спустился с неба, подошёл к могильной пещере и отвалил камень. И теперь он сидел на нём. 3Лицо его излучало сияние, подобное молнии, а его одежда была белой, как снег. 4Стражники настолько испугались его, что задрожали и стали как мёртвые.

5Ангел сказал женщинам:

– Не бойтесь, я знаю, что вы ищете распятого Ису. 6Его здесь нет, Он воскрес, как и говорил ранее. Подойдите и посмотрите на место, где Он лежал. 7Идите же скорее и скажите Его ученикам, что Он воскрес из мёртвых и отправился прежде вас в Галилею. Там вы Его и увидите. Запомните то, что я вам сказал.

8Женщины ушли от могилы испуганные, но в то же время очень обрадованные. Они побежали, чтобы поскорее рассказать обо всём ученикам Исы. 9Вдруг их встретил Сам Иса.

– Приветствую вас, – сказал Он.

Они подошли, обняли Его ноги и поклонились Ему. 10Тогда Иса сказал им:

– Не бойтесь. Идите и скажите Моим братьям (ученикам), чтобы они шли в Галилею. Там они Меня и увидят.

Религиозные вожди подкупают стражу

11Женщины ещё были в пути, когда несколько человек из стражи пришли в город и рассказали обо всём главным священнослужителям. 12Главные священнослужители посовещались со старейшинами и разработали план. Они дали солдатам много денег 13и сказали:

– Говорите всем так: «Его ученики пришли ночью и выкрали тело, пока мы спали». 14А если это дойдёт до наместника, то мы с ним поговорим и тем вас избавим от неприятностей.

15Солдаты взяли деньги и поступили так, как их научили. И эта выдумка распространена среди отвергающих Ису иудеев и по сегодняшний день.

Великое поручение

16А одиннадцать учеников пошли в Галилею, на гору, куда Иса велел им прийти. 17Там они увидели Ису и поклонились Ему, однако некоторые засомневались, что это Он. 18Тогда, подойдя, Иса сказал им:

– Мне дана вся власть на небе и на земле. 19Поэтому пойдите ко всем народам и сделайте их Моими учениками, совершая над ними обряд погружения в воду28:19 Или: «обряд омовения». в знак единения с Отцом, Сыном и Святым Духом28:19 Букв.: «во имя Отца, Сына и Святого Духа». Слово «имя» стоит в единственном числе, что говорит об одном, триедином Боге, а не о трёх богах., и 20учите их исполнять всё, что Я вам повелел. А Я буду с вами всегда, до скончания века.