Mattiyu 27 – HCB & HHH

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 27:1-66

Yahuda ya rataye kansa

(Markus 15.1; Luka 23.1,2; Yohanna 18.28-32)

1Da wayewar gari, sai dukan manyan firistoci da dattawan mutane suka yanke shawara su kashe Yesu. 2Suka daure shi, suka tafi da shi, suka ba da shi ga gwamna Bilatus.

(Ayyukan Manzanni 1.18,19)

3Sa’ad da Yahuda, wanda ya bashe Yesu, ya ga an yanke wa Yesu hukuncin kisa, sai ya yi “da na sani.” Ya je mayar wa manyan firistoci da dattawan kuɗin azurfa talatin ɗin. 4Ya ce, “Na yi zunubi da na ci amanar marar laifi.”

Suka ce masa, “Ina ruwanmu da wannan? Wannan dai ruwanka ne.”

5Sai Yahuda ya zubar da kuɗin a cikin haikalin ya tafi. Sa’an nan ya je ya rataye kansa.

6Manyan firistoci suka ɗauki kuɗin, suka ce, “Doka ta hana a sa kuɗin a cikin ma’aji, da yake kuɗin jini ne.” 7Saboda haka, sai suka yanke shawara su yi amfani da kuɗin suka sayi filin mai yin tukwane, saboda binne baƙi. 8Shi ya sa ake kiran filin, Filin Jini har yă zuwa yau. 9Sai abin da aka faɗa ta bakin annabi Irmiya ya cika cewa, “Suka ɗauki azurfa talatin, kuɗin da mutanen Isra’ila suka sa a kansa, 10suka kuma yi amfani da su, suka sayi filin mai yin tukwane, kamar yadda Ubangiji ya umarce ni.”27.10 Dubi Zak 11.12,13; Irm 19.1-13; Irm 32.6-9.

Yesu a gaban Bilatus

(Markus 15.2-5; Luka 23.3-5; Yohanna 18.33-38)

11Ana cikin haka, Yesu kuwa yana tsaye a gaban gwamna, sai gwamnan ya tambaye shi, “Kai ne Sarkin Yahudawa?”

Yesu ya ce, “I, haka ne, kamar yadda ka faɗa.”

12Da manyan firistoci da dattawa suka zarge shi, bai ba da amsa ba. 13Sai Bilatus ya tambaye shi ya ce, “Ba ka jin shaidar da suke kawowa a kanka?” 14Amma Yesu bai ce uffam game da ko ɗaya daga cikin zargin da suka yi masa ba. Har gwamna ya yi mamaki ƙwarai.

(Markus 15.6-15; Luka 23.13-26; Yohanna 18.39–19.16)

15A wannan irin Biki, gwamna yana da wata al’ada, ta sakin ɗan kurkuku guda wanda taron suka zaɓa. 16To, a wannan lokaci kuwa suna da wani shahararren ɗan kurkuku da ake kira Barabbas. 17Saboda haka da taron suka taru, sai Bilatus ya tambaye su ya ce, “Wane ne a cikinsu kuke so in sakar muku. Barabbas ko Yesu wanda ake kira Kiristi?” 18Don ya san saboda sonkai ne suka ba da Yesu a gare shi.

19Yayinda Bilatus yake zaune a kan kujerar shari’a, sai matarsa ta aika masa da wannan saƙo cewa, “Kada ka sa hannunka a kan marar laifin nan, domin na sha wahala ƙwarai, a cikin mafarki yau game da shi.”

20Amma manyan firistoci da dattawa suka shawo kan taron, su ce, a ba su Barabbas, amma a kashe Yesu.

21Gwamna ya yi tambaya ya ce, “Wane ne cikin biyun nan, kuke so in sakar muku?”

Suka ce, “Barabbas.”

22Bilatus ya yi tambaya, “To, me zan yi da Yesu wanda ake kira Kiristi?”

Duka suka ce, “A gicciye shi!”

23Bilatus ya ce, “Don me? Wane laifi ya yi?”

Amma suka ƙara tā da ihu, suna cewa, “A gicciye shi!”

24Da Bilatus ya ga cewa ba ya kaiwa ko’ina, sai ma hargitsi ne yake so yă tashi, sai ya ɗibi ruwa, ya wanke hannuwansa a gaban taron ya ce, “Ni kam, ba ruwana da alhakin jinin mutumin nan. Wannan ruwanku ne!”

25Sai dukan mutane suka amsa, suka ce, “Bari alhakin jininsa yă zauna a kanmu da ’ya’yanmu!”

26Sai ya sakar musu Barabbas. Amma ya sa aka yi wa Yesu bulala, sa’an nan ya ba da shi a gicciye.

Sojoji sun yi wa Yesu ba’a

(Markus 15.16-21; Yohanna 19.2,3)

27Sai sojojin gwamna suka ɗauki Yesu suka kai shi Fadar mai mulki, sa’an nan suka tara dukan kamfanin sojoji kewaye da shi. 28Suka tuɓe shi, suka yafa masa wata jar riga. 29Suka kuma tuƙa wani rawanin ƙaya, suka sa masa a kā. Suka sa sanda a hannun damansa. Suka durƙusa a gabansa, suka yi masa ba’a, suna cewa, “Ranka yă daɗe sarkin Yahudawa!” 30Suka tattofa masa miyau, suka karɓe sandan, suka yi ta ƙwala masa shi a kai. 31Bayan sun yi masa ba’a, sai suka tuɓe masa rigar, suka sa masa nasa tufafin. Sai suka tafi da shi, domin su gicciye shi.

Gicciyewa

(Markus 15.16-21; Yohanna 19.2,3)

32Suna fitowa ke nan, sai suka sadu da wani mutumin Sairin, mai suna Siman. Sai suka tilasta shi ya ɗauki gicciyen. 33Sai suka iso wani wurin da ake kira Golgota (wanda yake nufin Wurin Ƙoƙon Kai). 34A can, suka ba shi ruwan inabi gauraye da wani abu mai ɗaci yă sha. Amma da ya ɗanɗana, sai ya ƙi sha. 35Bayan da suka gicciye shi, sai suka raba tufafinsa a tsakaninsu ta wurin jefa ƙuri’a. 36Sa’an nan suka zauna suna tsaronsa. 37Bisa da kansa kuwa, an kafa rubutun zargin da aka yi masa, da ya ce,

Wannan shi ne Yesu Sarkin Yahudawa.

38An gicciye ’yan fashi biyu tare da shi, ɗaya a damansa, ɗaya kuma a hagunsa. 39Masu wucewa, suka zazzage shi, suna kaɗa kai, 40suna cewa, “Kai da za ka rushe haikali, ka kuma gina shi cikin kwana uku, ceci kanka mana! In kai Ɗan Allah ne, ka sauka daga gicciyen!”

41Haka ma, manyan firistoci da malaman dokoki da kuma dattawa, suka yi ta yin masa ba’a, suna cewa, 42“Ya ceci waɗansu, amma ya kāsa ceton kansa! In shi ne Sarkin Isra’ila! To, yă sauko daga kan gicciyen nan, mu kuwa mu gaskata shi. 43Ya dogara ga Allah. Bari Allah yă cece shi yanzu, in yana sonsa, domin ya ce, ‘Ni Ɗan Allah ne.’ ” 44Haka ma, ’yan fashin da aka gicciye tare da shi, suka zazzage shi.

Mutuwar Yesu

(Markus 15.33-41; Luka 23.44-49; Yohanna 19.28-30)

45Daga sa’a ta shida, har zuwa sa’a ta tara, duhu ya rufe ƙasa duka. 46Wajen sa’a ta tara, Yesu ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce, “Eloi, Eloi,27.46 Waɗansu rubuce-rubucen hannu na dā suna da Eloi, Eloi lama sabaktani?” (Wato, “Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni?”).27.46 Zab 22.1

47Sa’ad da waɗanda suke tsattsaye a wurin suka ji haka, sai suka ce, “Yana kiran Iliya.”

48Nan da nan, ɗaya daga cikinsu ya ruga, ya sami soso, ya jiƙa shi da ruwan tsami, ya sa a sanda, ya miƙa wa Yesu, yă sha. 49Sauran kuwa suka ce, “Ƙyale shi mu ga, ko Iliya zai zo yă cece shi.”

50Da Yesu ya sāke ɗaga murya da ƙarfi, sai ya saki ruhunsa.

51A daidai wannan lokaci, sai labulen haikali ya tsage gida biyu, daga sama har ƙasa. Ƙasa ta jijjiga, duwatsu kuma suka farfashe. 52Kaburbura suka bubbuɗe, jikunan tsarkaka da yawa kuwa cikin waɗanda da suka mutu, suka tashi. 53Suka firfito daga kaburbura, sa’an nan bayan tashin Yesu daga matattu, suka shiga birni mai tsarki, suka bayyana ga mutane da yawa.

54Da jarumin nan tare da waɗanda suke tsaron Yesu, suka ga girgizar ƙasa, da kuma abin da ya faru, sai tsoro ya kama su, suka kuma ce, “Gaskiya, wannan Ɗan Allah ne!”

55Akwai mata da yawa a can, suna kallo daga nesa. Sun bi Yesu tun daga Galili, suna masa hidima. 56A cikinsu, akwai Maryamu Magdalin, da Maryamu uwar Yaƙub da Yoses, da kuma uwar ’ya’yan Zebedi.

Bizinar Yesu

(Markus 15.42-47; Luka 23.50-56; Yohanna 19.38-42)

57Da yamma ta yi, sai ga wani mutum mai arziki daga Arimateya, sunansa Yusuf, wanda shi da kansa almajirin Yesu ne. 58Ya je wurin Bilatus, ya roƙe shi yă ba shi jikin Yesu. Sai Bilatus ya umarta a ba shi. 59Yusuf ya ɗauki jikin ya nannaɗe shi da zanen lilin mai tsabta. 60Sa’an nan ya sa shi a sabon kabarinsa, wanda ya haƙa a dutse. Bayan ya gungura wani babban dutse ya rufe bakin kabarin, sai ya tafi abinsa. 61Maryamu Magdalin da ɗayan Maryamun, suna zaune a wurin, ɗaura da kabarin.

Masu gadi a kabari

62Kashegari, wato, bayan Ranar Shirye-shirye, sai manyan firistoci da Farisiyawa, suka je wurin Bilatus. 63Suka ce, “Ranka yă daɗe, mun tuna, mai ruɗin nan tun yana da rai ya ce, ‘Bayan kwana uku, zan tashi daga matattu.’ 64Saboda haka, ka ba da umarni, a tsare kabarin sai rana ta uku ɗin. In ba haka ba, almajiransa za su iya zuwa su sace jikin, sa’an nan su faɗa wa mutane cewa, an tashe shi daga matattu. Ruɗin ƙarshen nan fa, sai yă fi na farkon muni.”

65Sai Bilatus ya ce, “Shi ke nan, ku ɗebi soja, ku je ku tsare kabarin iya ƙoƙarinku.” 66Sai suka je suka tsare kabarin ta wurin buga masa hatimi, suka kuma sa masu gadi.

Habrit Hakhadasha/Haderekh

הבשורה על-פי מתי 27:1-66

1לפנות בוקר שוב התכנסו ראשי הכוהנים וזקני העם, כדי להתייעץ כיצד לשכנע את המושל הרומאי להוציא את ישוע להורג. 2הם כבלו אותו ושלחו אותו לפילטוס, המושל הרומאי. 3כאשר ראה יהודה הבוגד שישוע נידון למוות, התחרט על המעשה שעשה והחזיר את הכסף לראשי הכוהנים והזקנים.

4”חטאתי“, הכריז יהודה. ”בגדתי באדם חף מפשע.“

”לא אכפת לנו“, השיבו. ”זאת הבעיה שלך.“

5יהודה זרק את הכסף על הרצפה במקדש, והלך לתלות את עצמו.

6ראשי הכוהנים אספו את הכסף מהרצפה ואמרו: ”איננו יכולים להכניס את הכסף לאוצר, כי התורה אוסרת קבלת כסף דמים.“

7הם התייעצו ביניהם, ולבסוף החליטו לקנות בכסף זה את שדה היוצר בירושלים, שהשתמשו בו לקבורת גויים.

8משום כך נקרא השדה ההוא עד היום הזה: ”שדה הדם“.

9‏-10בזאת התקיימה נבואת זכריה: ”הם לקחו את שלושים שקלי הכסף – המחיר שבו העריכו אותו בני ישראל – וקנו שדה מאת הקדר, כפי שהדריך אותי ה׳.“27‏.9‏-10 כז 9‏-10 תרגום חופשי של זכריה יא 12‏-13

11ישוע עמד לפני פילטוס, המושל הרומאי, וזה שאל אותו: ”האם אתה מלך היהודים?“

”אתה אומר“, השיב ישוע.

12אולם כאשר ראשי הכוהנים והזקנים האשימו אותו, ישוע לא אמר דבר.

13”האם אינך שומע את מה שהם אומרים?“ שאל פילטוס.

14אך להפתעתו הרבה של המושל לא אמר ישוע דבר.

15כל שנה, לכבוד חג הפסח, נהג המושל לשחרר אסיר יהודי אחד לפי בחירת העם. 16באותה שנה היה בכלא אסיר ידוע לשמצה בשם ישוע בר־אבא. 17כאשר התאסף באותו בוקר המון רב לפני ביתו של פילטוס, הוא שאל: ”את מי אשחרר לכם, את ישוע בר־אבא, או את ישוע הנקרא משיח?“ 18כי פילטוס ידע היטב שמסרו את ישוע מתוך קנאה.

19באותו זמן, כשישב פילטוס על כסאו בבית־הדין, שלחה אליו אשתו הודעה: ”עזוב את האיש הטוב הזה לנפשו, כי בלילה האחרון חלמתי עליו חלום נורא.“

20בינתיים הספיקו ראשי הכוהנים והזקנים לשכנע את ההמון לדרוש את שחרורו של בר־אבא, ואת הוצאתו להורג של ישוע. 21וכך כשחזר המושל ושאל: ”את מי מהשניים אשחרר לכם?“ צעק הקהל: ”את בר־אבא!“

22”אם כך, מה אעשה עם ישוע הנקרא משיח?“ שאל פילטוס.

”צלוב אותו!“ הם צעקו.

23”מדוע? מה עשה?“ שאל פילטוס.

הם לא ענו, ורק הגבירו את צעקותיהם: ”צלוב אותו!“

24כשראה פילטוס שאין טעם להמשיך ושעלולה לפרוץ מהומה, דרש שיביאו אליו קערת מים. הוא רחץ את ידיו לעיני הקהל ואמר: ”הידיים שלי נקיות מדמו של האיש הצדיק הזה. האחריות מוטלת עליכם!“

25וההמון השיב בצעקה: ”דמו עלינו ועל בנינו!“

26אז שחרר להם פילטוס את בר־אבא, ולאחר שהלקה את ישוע בשוטים מסרו לידי החיילים הרומאים, כדי שיקחו אותו לצליבה. 27אולם לפני כן הם לקחו אותו אל ארמון המושל וקראו לכל חיילי המשמר. 28הם הפשיטוהו והלבישוהו גלימת ארגמן. 29לאחר מכן שזרו זר מקוצים ארוכים והניחו על ראשו ככתר, בידו הימנית שמו מקל כשרביט, כרעו ברך לפניו בלגלוג והתגרו בו בקריאות לעג: ”יחי מלך היהודים!“ 30הם ירקו בפניו, חטפו מידו את המקל והכוהו על ראשו.

31לאחר שסיימו החיילים להתלוצץ ולצחוק עליו, הפשיטו מעליו את הגלימה והלבישו אותו בבגדיו, והוציאו אותו החוצה לצליבה.

32בדרך למקום הצליבה הם פגשו את שמעון מקירניה ואילצו אותו לסחוב את הצלב של ישוע. 33הם המשיכו בדרכם עד שהגיעו למקום הנקרא ”גלגלתא“, או ”מקום הגולגולת“. 34החיילים נתנו לו יין מסומם, אולם לאחר שטעם ממנו סרב לשתות אותו. 35לאחר הצליבה הפילו החיילים גורל, כדי לחלק ביניהם את בגדיו של ישוע. 36ואז התיישבו והביטו בישוע על הצלב. 37מעל ראשו הם תלו שלט: ”זהו ישוע מלך היהודים.“

38יחד עם ישוע נצלבו גם שני פושעים – אחד לימינו ואחד לשמאלו. 39העוברים ושבים קללו אותו, לעגו לו וקראו: 40”נו, אתה יכול להרוס את בית המקדש ולבנותו מחדש בשלושה ימים? אם אתה בן־אלוהים, מדוע אינך יורד מהצלב ומציל את עצמך?“

41גם ראשי הכוהנים, הסופרים והזקנים חרפו אותו ולעגו לו: 42”הוא יכול להושיע את כולם חוץ מאשר את עצמו!“ צחקו. ”משיח שכמוהו!“ קראו. ”מלך ישראל, הבה נראה אותו יורד מהצלב, ואז נאמין בו! 43הרי בטח באלוהים, נראה אם אלוהים באמת יציל אותו. הרי אמר שהוא בן־אלוהים!“

44גם הפושעים שנצלבו לידו העליבו אותו בצורה דומה.

45בשעה שתים־עשרה בצהריים כיסה חושך את כל הארץ למשך שלוש שעות.

46בשעה שלוש אחר־הצהריים זעק ישוע זעקת שבר:27‏.46 כז 46 בארץ ישראל בתקופה הזו היהודים דיברו בעברית ובארמית. כאשר מופיע תעתיק ביוונית המקורית בברית החדשה, מלבד מקרים בודדים (התגלות ט 11, טז 16), הציטוט מובא בארמית ולא בעברית. עובדה זו מומחשת במעשי השליחים א 19: ”הדבר הזה נודע לכל יושבי ירושלים ולפיכך נקרא אותו שדה בלשונם ’חקל דמא‘, שפירושו שדה הדם“. ”אלי, אלי, למה שבקתני?“ (כלומר: ”אלי, אלי, למה עזבתני?“)

47אחדים מהנוכחים חשבו שהוא קורא לאליהו הנביא. 48אחד מהם רץ והביא ספוג טבול בחומץ, שם אותו בקצה מקל והושיטו לישוע כדי שישתה. 49אך יתר האנשים אמרו: ”עזוב אותו. הבה נראה אם אליהו באמת יבוא להציל אותו!“

50אז זעק ישוע שנית ונפח את נשמתו. 51באותו רגע הפרוכת שלפני קודש הקודשים בבית־המקדש נקרעה לשניים – מלמעלה עד למטה. האדמה רעדה, סלעים נבקעו, 52קברים נפתחו, וצדיקים רבים קמו לתחייה. 53לאחר תחייתו של ישוע, אלה עזבו את בית־הקברות, נכנסו לירושלים והופיעו לפני אנשים רבים.

54קצין רומאי והחיילים שהיו ליד הצלב, נבהלו מאוד מרעידת האדמה ומכל מה שקרה, וקראו: ”איש זה באמת היה בן־אלוהים!“

55נשים רבות שבאו עם ישוע מהגליל, כדי לשרתו, עמדו מרחוק והתבוננו. 56ביניהן היו מרים המגדלית, מרים אמם של יעקב ויוסף, ואמם של יעקב ויוחנן (בני זבדי).

57‏-58בערב ניגש אל פילטוס יוסף מן־הרמתיים, שהיה אדם עשיר ותלמיד של ישוע, וביקש את גופתו. פילטוס ציווה לשחרר את הגופה ולהעביר אותה ליוסף. 59יוסף לקח את הגופה, עטף אותה בסדין לבן, 60הניח אותה בתוך קבר חדש שחצב בשביל עצמו, סתם את הפתח באבן גדולה והלך לדרכו. 61מרים המגדלית ומרים השנייה ישבו במרחק והסתכלו.

62למחרת, בתום טקסי החג, באו ראשי הכוהנים והפרושים אל פילטוס 63ואמרו: ”אדוננו, השקרן הזה אמר פעם שלאחר שלושה ימים ישוב ויקום לתחייה. 64משום כך אנחנו מבקשים ממך לחתום את הקבר עד לאחר היום השלישי, כדי שתלמידיו לא יגנבו את הגופה ויפיצו את השמועה שהוא קם מן המתים. אחרת תהיה התרמית גרועה מזו הראשונה.“

65פילטוס אמר להם: ”יש לכם משמר שלכם, אתם יודעים איך לטפל בזה כמו שצריך“.

66וכך הם חתמו את הקבר והציבו שומרים.