Mattiyu 25 – HCB & HHH

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 25:1-46

Misalin budurwai goma

1“A lokacin mulkin sama zai zama kamar budurwai goma waɗanda suka ɗauki fitilunsu suka fita don su taryi ango. 2Biyar daga cikinsu wawaye ne, biyar kuma masu hikima. 3Wawayen sun ɗauki fitilunsu, sai dai ba su riƙe mai ba. 4Masu hikimar kuwa suka riƙo tulunan mai da fitilunsu. 5Ango ya yi jinkirin zuwa, sai duk suka shiga gyangyaɗi har barci ya kwashe su.

6“Can tsakar dare, sai aka ji kira, ana cewa, ‘Ga ango nan! Ku fito, ku tarye shi!’

7“Sai dukan budurwan nan suka farka suka kuna fitilunsu. 8Sai wawayen suka ce wa masu hikimar, ‘Ku ɗan sassam mana manku; fitilunmu suna mutuwa.’

9“Su kuwa suka amsa, suka ce, ‘A’a, wataƙila ba zai ishe mu da ku ba. Gara ku je wurin masu sayarwa ku sayo.’

10“Amma yayinda suke kan tafiya garin sayen mai, sai ango ya iso. Budurwai da suke a shirye, suka shiga wajen bikin auren tare da shi. Aka kuma kulle ƙofa.

11“An jima can, sai ga sauran sun iso. Suka ce, ‘Ranka yă daɗe! Ranka yă daɗe! Ka buɗe mana ƙofa!’

12“Amma ya amsa ya ce, ‘Gaskiya nake gaya muku, ban san ku ba.’

13“Saboda haka sai ku zauna a faɗake, don ba ku san ranar ko sa’ar ba.

Misalin talenti

(Luka 19.11-27)

14“Har wa yau, za a kwatanta shi da mutumin da zai yi tafiya, wanda ya kira bayinsa ya kuma danƙa musu mallakarsa. 15Ga guda, ya ba shi talenti biyar na kuɗi, ga wani talenti biyu, ga wani kuma talenti ɗaya, kowa bisa ga azancinsa. Sa’an nan ya yi tafiyarsa. 16Mutumin da ya karɓi talenti biyar, nan da nan ya tafi ya yi kasuwanci da su har ya sami ribar talenti biyar. 17Haka ma, wannan mai talenti biyu, shi ma ya yi riba biyu. 18Amma mutumin da ya karɓi talenti ɗaya ɗin, ya tafi, ya tona rami, ya ɓoye kuɗin maigidansa.

19“Bayan an daɗe, sai maigidan bayin nan ya dawo, ya kuma daidaita lissafi da su. 20Mutumin da ya karɓi talenti biyar, ya kawo ƙarin talenti biyar. Ya ce, ‘Maigida, ka danƙa mini talenti biyar. Ga shi, na yi ribar biyar.’

21“Maigidansa ya amsa ya ce, ‘Madalla, bawan kirki mai aminci! Ka yi aminci a kan abubuwa kaɗan, zan sa ka lura da abubuwa masu yawa. Zo ka yi farin ciki tare da maigidanka!’

22“Mutumin da yake da talenti biyu, shi ma ya zo ya ce, ‘Maigida, ka danƙa mini talenti biyu; ga shi, na yi ribar biyu.’

23“Maigidansa ya amsa ya ce, ‘Madalla, bawan kirki mai aminci! Ka yi aminci a kan abubuwa kaɗan, zan sa ka lura da abubuwa masu yawa. Zo ka yi farin ciki tare da maigidanka!’

24“Sa’an nan mutumin da ya karɓi talenti ɗaya ya zo. Ya ce, ‘Maigida, na san cewa kai mutum ne mai wuyan sha’ani, kana girbi inda ba ka shuka ba, kana kuma tara inda ba ka yafa iri ba. 25Saboda haka na ji tsoro, na je na ɓoye talentinka a ƙasa. Ga abinka.’

26“Maigidansa ya amsa ya ce, ‘Kai mugun bawa, mai ƙyuya! Ashe, ka san cewa ina girbi inda ban yi shuka ba, ina kuma tarawa inda ban yafa iri ba? 27To, in haka ne, ai, da ka sa kuɗina a banki, don sa’ad da na dawo da na karɓi abina da riba.

28“ ‘Karɓi talentin daga hannunsa ku ba wanda yake da talenti goma. 29Gama duk mai abu za a ƙara masa, zai kuma same shi a yawalce. Duk wanda ba shi da shi kuwa, ko ɗan abin da yake da shi ma, sai an karɓe masa. 30Ku jefar da banzan bawan nan waje, cikin duhu, inda za a yi kuka da cizon haƙora.’

Tumaki da awaki

31“Sa’ad da Ɗan Mutum ya zo cikin ɗaukakarsa, tare da dukan mala’iku, zai zauna a kursiyinsa cikin ɗaukakar sama. 32Za a tara dukan al’ummai a gabansa, zai kuma raba mutane dabam-dabam yadda makiyayi yakan ware tumaki daga awaki. 33Zai sa tumaki a damansa, awaki kuma a hagunsa.

34“Sa’an nan Sarki zai ce wa waɗanda suke damansa, ‘Ku zo, ku da Ubana ya yi wa albarka; ku karɓi gādonku, mulkin da aka shirya muku tun halittar duniya. 35Gama da nake jin yunwa, kun ciyar da ni, da nake jin ƙishirwa, kun ba ni abin sha, da nake baƙunci, kun karɓe ni, 36da nake bukatar tufafi, kun yi mini sutura, da na yi rashin lafiya, kun lura da ni, da nake kurkuku, kun ziyarce ni.’

37“Sa’an nan masu adalci za su amsa masa, su ce, ‘Ubangiji, yaushe muka gan ka da yunwa muka ciyar da kai, ko da ƙishirwa muka ba ka abin sha? 38Yaushe kuma muka gan ka baƙo muka karɓe ka, ko cikin bukatar tufafi muka yi maka sutura? 39Yaushe kuma muka gan ka cikin rashin lafiya ko a kurkuku muka ziyarce ka?’

40“Sarkin zai amsa ya ce, ‘Gaskiya nake gaya muku, duk abin da kuka yi wa ɗaya daga cikin waɗannan ’yan’uwana mafi ƙanƙanta, ni kuka yi wa.’

41“Sa’an nan zai ce wa waɗanda suke a hagunsa, ‘Ku rabu da ni, la’anannu, zuwa cikin madawwamiyar wutar da aka shirya don Iblis da mala’ikunsa. 42Gama da nake jin yunwa, ba ku ba ni abinci ba, da nake jin ƙishirwa, ba ku ba ni abin sha ba, 43da na yi baƙunci, ba ku karɓe ni ba, da nake bukatar tufafi, ba ku yi mini sutura ba, da na yi rashin lafiya kuma ina a kurkuku, ba ku lura da ni ba.’

44“Su ma za su amsa, su ce, ‘Ubangiji, yaushe muka gan ka cikin yunwa ko ƙishirwa ko baƙo ko cikin bukatar tufafi ko cikin rashin lafiya ko cikin kurkuku, ba mu taimake ka ba?’

45“Zai amsa, yă ce, ‘Gaskiya nake gaya muku, duk abin da ba ku yi wa ɗaya daga cikin waɗannan mafi ƙanƙanta ba, ba ku yi mini ba ke nan.’

46“Sa’an nan za su tafi cikin madawwamiyar hukunci, amma masu adalci kuwa za su shiga rai madawwami.”

Habrit Hakhadasha/Haderekh

הבשורה על-פי מתי 25:1-46

1”אז תידמה מלכות השמים לסיפור על עשר עלמות, אשר לקחו את המנורות שלהן ויצאו לקבל את פני החתן. 2‏-4אולם רק חמש מהן היו חכמות ומילאו את מנורותיהן מראש בשמן. חמש האחרות היו טיפשות ולא מילאו מראש את המנורות.

5‏-6”מכיוון שהחתן איחר לבוא, שכבו העלמות לנוח. בחצות הלילה הן התעוררו לקול תרועה: ’החתן בא! צאנה לקבל את פניו!‘

7‏-8”כל הבחורות קמו מיד והיטיבו את המנורות. אלה שלא היה להן שמן ביקשו מעט מחברותיהן, כי מנורותיהן דעכו.

9”אולם הבחורות החכמות ענו: ’אם ניתן לכן מעט שמן לא יישאר לנו מספיק. לכו לחנות לקנות לעצמכן‘.

10”אך בזמן שהן הלכו לקנות שמן בא החתן, ואלה שהיו מוכנות נכנסו איתו אל החתונה והדלת ננעלה.

11”כשחזרו האחרות מאוחר יותר, הן עמדו בחוץ וקראו: ’אדוננו, אדוננו, פתח לנו את הדלת!‘

12”אולם הוא השיב להן מבפנים: ’אינני מכיר אתכן!‘

13”משום כך היו ערים ומוכנים, כי אינכם יודעים באיזה יום ובאיזו שעה אחזור.“

14ישוע המשיך: ”אפשר לתאר את מלכות השמים בעזרת הסיפור על אדם שנסע לארץ רחוקה. לפני נסיעתו הוא קרא למשרתיו והפקיד בידם סכומי כסף, כדי שישקיעו אותם למענו בזמן העדרו. 15הוא נתן לאחד 50,000 שקלים, לשני – 20,000 שקלים ולשלישי – 10,000 שקלים. הוא חילק את הכסף בהתאם לכישרונו של כל אחד ויצא לדרכו. 16האיש שקיבל 50,000 שקלים החל מיד לקנות ולמכור, ותוך זמן קצר הרוויח עוד 50,000 שקלים. 17גם האיש שקיבל 20,000 שקלים ניגש מיד לעבודה והרוויח עוד 20,000 שקלים. 18אך האיש שקיבל 10,000 שקלים חפר בור באדמה והטמין בתוכו את הכסף.

19”לאחר זמן רב חזר האדון ממסעו, וביקש ממשרתיו לתת דין וחשבון על הכסף שהפקיד בידם. 20האיש שקיבל 50,000 שקלים החזיר לאדוניו 100,000 שקלים. 21האדון שיבח אותו על עבודתו הטובה ואמר: ’מאחר שהיית נאמן בסכום קטן, אתן לך עכשיו אחריות גדולה יותר. בוא והשתתף בשמחתי‘.

22”אחריו בא האיש שקיבל 20,000 שקלים והצהיר: ’אדוני, נתת לי 20,000 שקלים, ועכשיו אני מחזיר לך סכום כפול‘.

23” ’עבודה טובה‘, אמר לו האדון. ’אתה משרת טוב ונאמן. מאחר שהיית נאמן בסכום קטן, אתן לך עכשיו הרבה יותר!‘ 24‏-25לאחר מכן בא האיש שקיבל 10,000 שקלים ואמר: ’אדוני, ידעתי שאתה איש קשה, שמצליח לקצור במקום שלא זרעת ולאסוף במקום שלא פיזרת. משום כך פחדתי והסתרתי את הכסף באדמה – והנה הוא!‘

26”אך אדוניו השיב לו: ’רשע שכמוך, עבד עצלן! אם ידעת שאדרוש ממך את הרווח, 27מדוע לא הפקדת את הכסף בבנק? כך לפחות הייתי מקבל ריבית! 28קחו ממנו את הכסף, ותנו לאיש שיש לו כבר 100,000 29כי האיש שמנצל היטב את מה שנותנים לו – יינתן לו עוד ויהיה לו שפע רב. ואילו אדם בלתי־אחראי – גם מעט האחריות שניתנה לו תילקח ממנו. 30קחו עתה את המשרת הזה, שאין בו כל תועלת, והשליכוהו החוצה לחושך, שם יש בכי וחריקת שיניים‘.

31”אולם כשאני, המשיח,25‏.31 כה 31 כלשונו: ”בן־האדם“ (דניאל ז 13‏-14) אבוא בתפארתי עם כל המלאכים, אשב על כיסאי בכבוד רב. 32כל אומות העולם יתאספו לפני, ואני אפריד ביניהם כרועה המפריד בין הכבשים ובין העיזים. 33את הכבשים אעמיד לימיני ואת העיזים לשמאלי.

34”לאחר מכן אני, המלך, אומר לעומדים לימיני: ’בואו, ברוכי אבי, אל המלכות שהוכנה למענכם מאז היווסד העולם. 35כשהייתי רעב – האכלתם אותי. כשהייתי צמא – נתתם לי לשתות. כשהייתי אורח זר – הכנסתם אותי לביתכם. 36כשהייתי עירום – הלבשתם אותי. כשהייתי חולה או אסור בכלא – באתם לבקר אותי‘.

37”ואותם צדיקים יענו: ’אדוננו, מתי ראינו אותך רעב והאכלנו אותך, או צמא והשקינו אותך? 38או אורח זר ועזרנו לך? או עירום והלבשנו אותך? 39מתי ראינו אותך חולה או כלוא ובאנו לבקר אותך?‘

40”ואני, המלך, אענה: ’כשעשיתם אחד מן הדברים האלה לאחד מאחי הצעירים – כאילו עשיתם אותו לי‘. 41לאחר מכן אפנה אל העומדים לשמאלי ואומר להם: ’הסתלקו מכאן, ארורים, אל האש הנצחית שהוכנה לשטן והשדים! 42כי כשהייתי רעב לא האכלתם אותי, וכשהייתי צמא לא נתתם לי דבר לשתות. 43הייתי אורח זר, אולם לא הזמנתם אותי לביתכם. הייתי עירום, ולא הלבשתם אותי. הייתי חולה וכלוא, וכלל לא באתם לבקר אותי!‘

44”ואז הם יענו: ’אדון, מתי ראינו אותך רעב או צמא או זר או עירום או חולה או כלוא, ולא עזרנו לך?‘

45”אז יענה להם: אמן, אומר אני לכם! ’כאשר סירבתם לעזור לאחד מן האחים הצעירים האלה סירבתם לעזור לי‘.

46”והם ילכו משם לייסורי נצח, ואילו הצדיקים – לחיי נצח.“