Mattiyu 24 – HCB & CCBT

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 24:1-51

Alamun ƙarshen zamani

(Markus 13.1,2; Luka 21.5,6)

1Yesu ya bar haikali ke nan, yana cikin tafiya sai almajiransa suka zo wurinsa don su ja hankalinsa ga gine-ginen haikali. 2Sai Yesu ya ce, “Kun ga duk waɗannan abubuwa? Gaskiya nake gaya muku, ba wani dutse a nan da za a bari a kan wani; duk za a rushe.”

(Markus 13.3-13; Luka 21.7-19)

3Da Yesu yana zaune a Dutsen Zaitun, almajiran suka zo wurinsa a ɓoye. Suka ce, “Gaya mana, yaushe ne wannan zai faru, mece ce alamar zuwanka da kuma ta ƙarshen zamani?”

4Yesu ya amsa, “Ku lura fa, kada wani yă ruɗe ku. 5Gama mutane da yawa za su zo cikin sunana, suna cewa, ‘Ni ne Kiristi,’ za su kuwa ruɗi mutane da yawa. 6Za ku ji labarin yaƙe-yaƙe da kuma jita-jitarsu, sai dai ku lura kada hankalinku yă tashi. Dole irin waɗannan abubuwa su faru, amma ƙarshen tukuna. 7Al’umma za tă tasar wa al’umma, mulki yă tasar wa mulki. Za a yi yunwa da girgizar ƙasa a wurare dabam-dabam. 8Dukan waɗannan fa, mafarin azabar naƙudar haihuwa ne.

9“Sa’an nan za a bashe ku don a tsananta muku a kuma kashe ku, dukan al’ummai za su ƙi ku saboda ni. 10A wannan lokaci, da yawa za su juya daga bangaskiya, su ci amana su kuma ƙi juna, 11annabawan ƙarya da yawa za su firfito su kuma ruɗi mutane da yawa. 12Saboda ƙaruwar mugunta, ƙaunar yawanci za tă yi sanyi, 13amma duk wanda ya tsaya da ƙarfi har ƙarshe, zai sami ceto. 14Za a kuma yi wa’azin wannan bisharar mulki a cikin dukan duniya, yă zama shaida ga dukan al’ummai, sa’an nan ƙarshen yă zo.

(Markus 13.14-23; Luka 21.20-24)

15“Saboda haka sa’ad da kuka ga ‘abin ƙyama mai kawo hallaka,’24.15 Dan 9.27; Dan 11.31; Dan 12.11 wanda annabi Daniyel ya yi magana a kai, yana tsaye a tsattsarkan wuri (mai karatu yă gane), 16to, sai waɗanda suke cikin Yahudiya, su gudu zuwa cikin duwatsu. 17Kada wani da yake a kan rufin gidansa, yă sauko don ɗaukar wani abu a gida. 18Kada wani da yake gona kuma yă komo don ɗaukar rigarsa. 19Kaiton mata masu ciki da mata masu renon ’ya’ya a waɗancan kwanakin! 20Ku yi addu’a, kada gudunku yă zama a lokacin sanyi ko a ranar Asabbaci. 21Gama a lokacin za a yi wata matsananciyar wahala, wadda ba a taɓa yi ba tun farkon duniya har ya zuwa yanzu ba kuwa za a ƙara yi ba.

22“Da ba don an taƙaita kwanakin nan ba, da babu wani da zai tsira, amma saboda zaɓaɓɓun nan, za a taƙaita kwanakin. 23A lokacin in wani ya ce muku, ‘Duba, ga Kiristi nan!’ Ko, ‘Ga shi can!’ Kada ku gaskata. 24Gama Kiristi masu yawa na ƙarya, da annabawan ƙarya za su firfito, su kuma aikata manyan alamu da ayyukan banmamaki don su ruɗi har da zaɓaɓɓu ma in zai yiwu. 25Ga shi, na faɗa muku tun da wuri.

26“Saboda haka in wani ya ce muku, ‘Ga shi can a hamada,’ kada ku fita; ko, ‘Ga shi nan a ɗakunan ciki,’ kada ku gaskata. 27Gama kamar yadda walƙiya take wulgawa walai daga gabas zuwa yamma, haka dawowar Ɗan Mutum zai kasance. 28Duk inda mushe yake, can ungulai za su taru.

(Markus 13.24-27; Luka 21.25-28)

29“Nan da nan bayan tsabar wahalan nan

“ ‘sai a duhunta rana,

wata kuma ba zai ba da haskensa ba;

taurari kuma za su fāffāɗi daga sararin sama,

za a kuma girgiza abubuwan sararin sama.’24.29 Ish 13.10; Ish 34.4

30“A sa’an nan ne alamar dawowar Ɗan Mutum zai bayyana a sararin sama, dukan al’umman duniya kuwa za su yi kuka. Za su ga Ɗan Mutum yana zuwa kan gizagizan sararin sama, da iko da kuma ɗaukaka mai girma. 31Zai kuwa aiki mala’ikunsa su busa ƙaho mai ƙara sosai, za su kuwa tattaro zaɓaɓɓunsa daga kusurwoyi huɗun nan, daga wannan bangon duniya zuwa wancan.

(Markus 13.28-31; Luka 21.29-33)

32“Yanzu fa, sai ku koyi wannan darasi daga itacen ɓaure. Da zarar rassansa suka yi taushi ganyayensa kuma suka toho, kun san damina ta kusa. 33Haka kuma, sa’ad da kun ga dukan waɗannan abubuwa, ku sani ya yi kusan zuwa, yana ma dab da bakin ƙofa. 34Gaskiya nake gaya muku, wannan zamani ba zai shuɗe ba sai dukan abubuwan nan sun faru. 35Sama da ƙasa za su shuɗe, amma maganata ba za tă taɓa shuɗe ba.

Rana ko sa’a ba a sani ba

(Markus 13.32-37; Luka 17.26-30,34-35)

36“Babu wanda ya san wannan rana ko sa’a, ko mala’ikun da suke sama ma, ko Ɗan, sai dai Uban kaɗai. 37Kamar yadda ya faru a zamanin Nuhu, haka zai zama a dawowar Ɗan Mutum. 38Gama a kwanaki kafin ruwan tsufana, mutane sun yi ta ci, sun kuma yi ta sha, suna aure, suna kuma aurarwa, har zuwa ranar da Nuhu ya shiga jirgi; 39ba su kuwa san abin da yake faruwa ba sai da ruwan tsufana ya zo ya share su tas. Haka zai zama a dawowar Ɗan Mutum. 40Maza biyu za su kasance a gona; za a ɗau ɗaya a bar ɗaya. 41Mata biyu za su kasance suna niƙa; za a ɗau ɗaya a bar ɗaya.

42“Saboda haka sai ku zauna a faɗake, gama ba ku san a wace rana ce Ubangijinku zai zo ba. 43Ku dai gane wannan, da maigida ya san ko a wane lokaci ne da dare, ɓarawo zai zo, da sai yă zauna a faɗake yă kuma hana a shiga masa gida. 44Saboda haka ku ma, sai ku zauna a faɗake, domin Ɗan Mutum zai zo a sa’ar da ba ku za tă ba.

(Luka 12.35-48)

45“Wane ne bawan nan mai aminci da kuma mai hikima, wanda maigida ya sa yă lura da bayi a cikin gidansa, yă riƙa ba su abinci a daidai lokaci? 46Zai zama wa bawan nan da kyau in maigidan ya dawo ya same shi yana yin haka. 47Gaskiya nake gaya muku, zai sa shi yă lura da dukan dukiyarsa. 48Amma in wannan bawa mugu ne, ya kuma ce a ransa, ‘Maigidana ba zai dawo da wuri ba.’ 49Sa’an nan yă fara dūkan ’yan’uwansa bayi, yana ci yana kuma sha tare da mashaya. 50Maigidan wannan bawa zai dawo a ranar da bai yi tsammani ba, a sa’ar kuma da bai sani ba. 51Maigidan zai farfasa masa jiki da bulala, yă kuma ba shi wuri tare da munafukai, inda za a yi kuka da cizon haƙora.

Chinese Contemporary Bible (Traditional)

馬太福音 24:1-51

預言聖殿被毀

1耶穌離開聖殿時,門徒上前把宏偉的聖殿指給祂看。 2耶穌對他們說:「你們看見這殿宇了嗎?我實在告訴你們,將來它要被完全拆毀,在這裡找不到兩塊疊在一起的石頭。」

世界末日的預兆

3耶穌正坐在橄欖山上,門徒私下來問祂:「請告訴我們,這事什麼時候會發生?你再來和世界末日的時候會有什麼預兆?」

4耶穌回答說:「你們要小心,免得被人迷惑。 5因為將來會有許多人冒我的名而來,說『我是基督』,欺騙許多人。 6你們聽見戰爭爆發、戰訊頻傳時,不要驚慌,因為這些事必然發生,只是末日還沒有到。 7民族將與民族互鬥,國家將與國家相爭,各處將有饑荒和地震。 8這些只是災難24·8 災難」希臘文是「生產之痛」。的開始。

9「那時,你們將遭人迫害、殺害,並因我的名而被萬民憎恨。 10那時,許多人會放棄信仰,互相出賣,彼此憎恨。 11許多假先知也會出現,迷惑許多人。 12由於罪惡氾濫,許多人的愛逐漸冷淡。 13但堅忍到底的必定得救。 14這天國的福音將傳遍天下,讓萬民都聽見,然後末日才會來臨。

15「當你們看見但以理先知所說的『那帶來毀滅的可憎之物』站立在聖地的時候(讀者須會意), 16住在猶太地區的人要趕快逃到山上去, 17在屋頂上的人不要下來進屋收拾行李, 18在田間工作的人也不要回家取外衣。 19那時,孕婦和哺育嬰兒的母親們可就遭殃了! 20你們要祈求上帝,不要讓你們在冬天或安息日逃難, 21因為那時世上將有空前絕後的大災難。 22如果不縮短災期,恐怕沒有人能活命。但為了選民的緣故,災期必被縮短。

23「那時,如果有人對你們說,『看啊!基督在這裡』,或說,『基督在那裡』,你們不要相信。 24因為假基督和假先知將出現,行很大的神蹟奇事來迷惑人,如果可能,甚至要迷惑上帝揀選的子民。 25你們要記住,我已經預先告訴你們了。

26「因此,如果有人對你們說,『看啊!基督在曠野』,你們不要出去;或者說,『看啊!基督在屋裡』,你們也不要相信。 27人子降臨時的情形就像閃電從東方發出一直照到西方。 28屍體在哪裡,禿鷹就會聚集在哪裡。

29「當災難的日子一過,

『太陽變黑,

月亮無光,

眾星隕落,

天體震動。』

30「那時,天上會出現人子降臨的預兆,地上的萬族都要哀哭,他們將看見人子帶著能力和極大的榮耀駕著天上的雲降臨。 31在響亮的號聲中,祂將差遣天使從四面八方、天涯海角招聚祂揀選的人。

無花果樹的比喻

32「你們可以從無花果樹學個道理。當無花果樹發芽長葉的時候,你們就知道夏天快來了。 33同樣,當你們看見這一切事發生時,就知道人子快來了,就在門口。 34我實在告訴你們,這個世代還沒有過去,這一切都要發生。 35天地都要過去,但我的話永遠長存。

警醒準備

36「但沒有人知道那日子和時辰何時來到,連天上的天使也不知道,人子24·36 人子」希臘文是「子」。也不知道,只有天父知道。 37人子降臨時的情形就像挪亞的時代。 38洪水來臨之前,人們吃吃喝喝,男婚女嫁,一直到挪亞進方舟那天; 39他們懵然不知,直到洪水來把他們全沖走了。人子降臨時的情形也是這樣。 40那時,兩個人在田裡,一個將被接去,一個將被撇下; 41兩個婦人推磨,一個將被接去,一個將被撇下。 42所以,你們要警醒,因為你們不知道你們的主會在哪一天來。 43你們都知道,如果一家的主人知道賊會在半夜幾點來,就必警醒,不讓賊入屋偷竊。 44同樣,你們也要做好準備,因為在你們意想不到的時候,人子就來了。

兩種奴僕

45「誰是那個受主人委託管理家中大小僕役、按時分糧食給他們、又忠心又精明的奴僕呢? 46主人回家時,看見他盡忠職守,他就有福了。 47我實在告訴你們,主人一定會把所有產業都交給他管理。 48但如果奴僕邪惡,以為主人不會那麼快回來, 49就毆打同伴,跟醉漢一起吃喝玩樂, 50主人會在他想不到的日子、不知道的時辰回來, 51嚴厲地懲罰24·51 嚴厲地懲罰」或作「腰斬」。他,判他和偽君子同樣的罪。他必在那裡哀哭切齒。