Mattiyu 22 – HCB & NEN

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 22:1-46

Misalin bikin aure

(Luka 14.15-24)

1Yesu ya sāke yin musu magana da misalai, yana cewa, 2“Mulkin sama yana kama da wani sarki wanda ya shirya bikin auren ɗansa. 3Sai ya aiki bayinsa su kira waɗanda aka gayyata zuwa bikin, amma waɗanda aka ce su zo bikin, suka ƙi zuwa.

4“Sai ya sāke aiken waɗansu bayi ya ce, ‘Ku ce wa waɗanda aka gayyata cewa na shirya abinci. An yanka bijimai da shanun da aka yi kiwo, kome a shirye yake. Ku zo bikin auren mana.’

5“Amma ba su kula ba, suka kama gabansu, ɗaya ya tafi gonarsa, ɗaya kuma ya tafi kasuwancinsa. 6Sauran suka kama bayinsa suka wulaƙanta su, suka kuma kashe su. 7Sai sarkin ya yi fushi. Ya aiki mayaƙansa suka karkashe masu kisankan nan, aka kuma ƙone birninsu.

8“Sa’an nan ya ce wa bayinsa, ‘Bikin aure fa ya shiryu, sai dai mutanen da na gayyata ba su dace ba. 9Ku bi titi-titi ku gayyato duk waɗanda kuka gani, su zo bikin.’ 10Saboda haka bayin suka bi titi-titi, suka tattaro duk mutanen da suka samu, masu kirki da marasa kirki, zauren bikin ya cika makil da baƙi.

11“Amma da sarkin ya shigo don yă ga baƙin, sai ya ga wani can da ba ya sanye da kayan auren. 12Ya yi tambaya ya ce, ‘Aboki, yaya ka shigo nan ba tare da rigar aure ba?’ Mutumin ya rasa ta cewa.

13“Sai sarkin ya ce wa fadawa, ‘Ku daure shi hannu da ƙafa, ku jefar da shi waje, cikin duhu, inda za a yi kuka da cizon haƙora.’

14“Gama kirayayu da yawa, amma zaɓaɓɓu kaɗan ne zaɓaɓɓu.”

Biyan haraji ga Kaisar

(Markus 12.13-17; Luka 20.20-26)

15Sai Farisiyawa suka yi waje, suka ƙulla yadda za su yi masa tarko cikin maganarsa. 16Suka aiki almajiransu tare da mutanen Hiridus wurinsa. Suka ce, “Malam, mun san kai mutum ne mai mutunci, kuma kana koyar da maganar Allah bisa gaskiya. Mutane ba sa ɗaukan hankalinka, domin ba ka kula ko su wane ne ba. 17To, ka gaya mana, a ra’ayinka? Ya dace a biya Kaisar haraji ko a’a?”

18Amma Yesu da yake ya san mugun nufinsu, sai ya ce, “Ku munafukai, don me kuke ƙoƙarin sa mini tarko? 19Ku nuna mini kuɗin da ake biyan haraji da shi.” Sai suka kawo masa dinari, 20sai ya tambaye su ya ce, “Hoton wane ne wannan? Kuma rubutun wane ne?”

21Suka amsa, “Na Kaisar ne.”

Sai ya ce musu, “Ku ba wa Kaisar abin da yake na Kaisar, ku kuma ba wa Allah abin da yake na Allah.”

22Da suka ji haka, sai suka yi mamaki. Saboda haka suka ƙyale shi, suka yi tafiyarsu.

Aure a tashin matattu

(Markus 12.18-27; Luka 20.27-40)

23A ranan nan Sadukiyawa, waɗanda suke cewa babu tashin matattu, suka zo wurinsa da tambaya. 24Suka ce “Malam, Musa ya faɗa mana cewa in mutum ya mutu ba shi da ’ya’ya, dole ɗan’uwansa yă auri gwauruwar yă kuma haifar wa ɗan’uwan ’ya’ya. 25A cikinmu an yi ’yan’uwa guda bakwai. Na fari ya yi aure, ya mutu, da yake bai sami ’ya’ya ba, sai ya bar matarsa wa ɗan’uwansa. 26Haka ya faru da ɗan’uwa na biyu da na uku, har zuwa na bakwai. 27A ƙarshe, macen ta mutu. 28To, a tashin matattu, matar wa a cikinsu bakwai ɗin nan za tă zama, da yake dukansu sun aure ta?”

29Yesu ya amsa ya ce, “Kun ɓata, domin ba ku san Nassi ko ikon Allah ba. 30Ai, a tashin matattu, mutane ba za su yi aure ko su ba da aure ba; za su zama kamar mala’iku a sama. 31Amma game da tashi daga matattu na waɗanda suka mutu ba ku karanta abin da Allah ya ce muku ba ne, 32‘Ni ne Allah na Ibrahim, Allah na Ishaku da kuma Allah na Yaƙub’22.32 Fit 3.6? Ai, shi ba Allah na matattu ba ne, shi Allah na masu rai ne.”

33Da taro suka ji haka, sai suka yi mamakin koyarwarsa.

Doka mafi girma

(Markus 12.28-34; Luka 10.25-28)

34Da jin Yesu ya ƙure Sadukiyawa, sai Farisiyawa suka tattaru. 35Ɗaya daga cikinsu, wani masanin Doka, ya gwada shi da wannan tambaya. 36“Malam, wace doka ce mafi girma a cikin dokoki?”

37Yesu ya amsa ya ce, “ ‘Ka ƙaunaci Ubangiji Allahnka da dukan zuciyarka da dukan ranka da kuma dukan hankalinka.’22.37 M Sh 6.5 38Wannan, ita ce doka ta fari da kuma mafi girma. 39Ta biye kuma kamar ta farkon take. ‘Ka ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka.’22.39 Fir 19.18 40Dukan Doka da Annabawa suna rataya ne a kan waɗannan dokoki biyu.”

Kiristi, ɗan wane ne?

(Markus 12.35-37; Luka 20.41-44)

41Yayinda Farisiyawa suke a tattare wuri ɗaya, sai Yesu ya tambaye su, 42“Me kuke tsammani game da Kiristi? Ɗan wane ne shi?”

Suka amsa suka ce, “Ɗan Dawuda.”

43Ya ce musu, “To, ta yaya Dawuda ya yi magana ta wurin Ruhu Mai Tsarki, ya kira shi ‘Ubangiji’? Gama ya ce,

44“ ‘Ubangiji ya ce wa Ubangijina,

“Zauna a hannun damana,

sai na sa abokan gābanka

su zama matashin sawunka.” ’22.44 Zab 110.1

45To, in Dawuda ya kira shi ‘Ubangiji,’ yaya zai zama ɗansa?” 46Ba wanda ya iya tanka masa, daga wannan rana kuwa ba wanda ya sāke yin karambanin yin masa wata tambaya.

Kiswahili Contemporary Version (Neno: Bibilia Takatifu)

Mathayo 22:1-46

Mfano Wa Karamu Ya Arusi

(Luka 14:15-24)

122:1 Lk 14:16; Ufu 19:7-9Yesu akasema nao tena kwa mifano, akawaambia, 222:2 Mt 13:24; Yn 3:29“Ufalme wa Mbinguni unaweza kufananishwa na mfalme mmoja aliyemwandalia mwanawe karamu ya arusi. 322:3 Mt 21:34Akawatuma watumishi wake kuwaita wale waliokuwa wamealikwa karamuni, lakini wakakataa kuja.

422:4 Mt 21:36“Kisha akawatuma watumishi wengine akisema, ‘Waambieni wale walioalikwa kwamba nimeandaa chakula. Nimekwisha kuchinja mafahali wangu na vinono, karamu iko tayari. Karibuni kwa karamu ya arusi.’

5“Lakini hawakuzingatia, wakaenda zao: huyu shambani mwake na mwingine kwenye biashara zake. 6Wengine wao wakawakamata wale watumishi wake, wakawatesa na kuwaua. 722:7 Lk 19:27Yule mfalme akakasirika sana, akapeleka jeshi lake likawaangamiza wale wauaji na kuuteketeza mji wao kwa moto.

822:8 Mt 10:11-13“Kisha akawaambia watumishi wake, ‘Karamu ya arusi imeshakuwa tayari, lakini wale niliowaalika hawakustahili kuja. 922:9 Eze 21:21; Mt 13:47; 21:43Kwa hiyo nendeni katika njia panda mkamwalike karamuni yeyote mtakayemwona.’ 1022:10 Mt 13:47-48Wale watumishi wakaenda barabarani, wakawakusanya watu wote waliowaona, wema na wabaya. Ukumbi wa arusi ukajaa wageni.

1122:11 2Kor 5:3; Efe 4:24; Kol 3:10, 12; Ufu 3:4; 16:15; 19:8“Lakini mfalme alipoingia ndani ili kuwaona wageni, akamwona mle mtu mmoja ambaye hakuwa amevaa vazi la arusi. 1222:12 Mt 20:12; 26:50Mfalme akamuuliza, ‘Rafiki, uliingiaje humu bila vazi la arusi?’ Yule mtu hakuwa na la kusema.

1322:13 Mt 8:12“Ndipo mfalme akawaambia watumishi wake, ‘Mfungeni mikono na miguu mkamtupe nje, kwenye giza. Huko kutakuwa na kilio na kusaga meno.’

1422:14 Ufu 17:14; Mt 20:16“Kwa maana walioitwa ni wengi, lakini walioteuliwa ni wachache.”

Kulipa Kodi Kwa Kaisari

(Marko 12:13-17; Luka 20:20-26)

1522:15 Mk 12:13; Lk 20:20Ndipo Mafarisayo wakatoka nje wakaandaa mpango wa kumtega Yesu katika maneno yake. 1622:16 Mk 3:6Wakatuma wanafunzi wao kwake pamoja na Maherode. Nao wakasema, “Mwalimu, tunajua kwamba wewe ni mtu mwadilifu na unafundisha njia ya Mungu katika kweli bila kuyumbishwa na mtu wala kuonyesha upendeleo. 1722:17 Mt 17:25Tuambie basi, wewe unaonaje? Je, ni halali kulipa kodi kwa Kaisari, au la?”

18Lakini Yesu, akijua makusudi yao mabaya, akawaambia, “Enyi wanafiki, kwa nini mnajaribu kunitega? 19Nionyesheni hiyo sarafu inayotumika kwa kulipia kodi.” Wakamletea dinari. 20Naye akawauliza, “Sura hii ni ya nani? Na maandishi haya ni ya nani?”

2122:21 Rum 13:7Wakamjibu, “Ni vya Kaisari.”

Basi Yesu akawaambia, “Mpeni Kaisari kilicho cha Kaisari, naye Mungu mpeni kilicho cha Mungu.”

2222:22 Mk 12:12Waliposikia hili, wakashangaa. Hivyo wakamwacha, wakaenda zao.

Ndoa Na Ufufuo

(Marko 12:18-27; Luka 20:27-40)

2322:23 Mdo 4:1; 23:8; 1Kor 15:12Siku hiyo hiyo Masadukayo, wale wasemao kwamba hakuna ufufuo wa wafu, wakamjia Yesu na kumuuliza swali, wakisema, 2422:24 Kum 25:5-6“Mwalimu, Mose alisema, ‘Kama mtu akifa bila kuwa na watoto, ndugu yake inampasa amwoe huyo mjane ili ampatie watoto huyo nduguye aliyekufa.’ 25Basi palikuwa na ndugu saba miongoni mwetu. Yule wa kwanza akaoa mke, naye akafa, na kwa kuwa hakuwa na watoto, akamwachia nduguye yule mjane. 26Ikatokea vivyo hivyo kwa yule ndugu wa pili, na wa tatu, hadi wote saba. 27Hatimaye, yule mwanamke naye akafa. 28Sasa basi, siku ya ufufuo, yeye atakuwa mke wa nani miongoni mwa wale ndugu saba, kwa kuwa wote walikuwa wamemwoa huyo mwanamke?”

2922:29 Yn 20:9Yesu akawajibu, “Mwapotoka kwa sababu hamjui Maandiko wala uweza wa Mungu. 3022:30 Mt 24:38Wakati wa ufufuo, watu hawataoa wala kuolewa, bali watakuwa kama malaika wa mbinguni. 31Lakini kuhusu ufufuo wa wafu, hamjasoma kile Mungu alichowaambia, kwamba, 3222:32 Kut 3:6; Mdo 7:32‘Mimi ni Mungu wa Abrahamu, Mungu wa Isaki, na Mungu wa Yakobo’? Yeye si Mungu wa wafu, bali ni Mungu wa walio hai.”

3322:33 Mt 7:28Ule umati wa watu uliposikia hayo, ulishangaa sana kwa mafundisho yake.

Amri Kuu Kuliko Zote

(Marko 12:28-34; Luka 10:25-28)

3422:34 Mdo 4:1Mafarisayo waliposikia kwamba Yesu alikuwa amewanyamazisha Masadukayo, Mafarisayo wakakusanyika pamoja. 3522:35 Lk 11:45; 14:3Mmoja wao, mtaalamu wa sheria, akamuuliza swali ili kumjaribu, akisema, 36“Mwalimu, ni amri ipi katika Sheria iliyo kuu kuliko zote?”

3722:37 Kum 6:5Yesu akamjibu, “ ‘Mpende Bwana Mungu wako kwa moyo wako wote na kwa roho yako yote na kwa akili zako zote.’ 38Hii ndiyo amri iliyo kuu, tena ni ya kwanza. 3922:39 Law 19:18; Gal 5:14Nayo ya pili ni kama hiyo, nayo ni hii: ‘Mpende jirani yako kama nafsi yako.’ 4022:40 Mt 7:12; Lk 10:25-28Amri hizi mbili ndizo msingi wa Sheria na Manabii.”

Swali Kuhusu Mwana Wa Daudi

(Marko 12:35-37; Luka 20:41-44)

4122:41 Mk 12:35; Lk 20:41Wakati Mafarisayo walikuwa wamekusanyika pamoja, Yesu akawauliza, 4222:42 Mt 9:27“Mnaonaje kuhusu Kristo?22:42 Kristo maana yake ni Masiya, yaani Aliyetiwa mafuta. Yeye ni mwana wa nani?”

Wakamjibu, “Yeye ni mwana wa Daudi.”

43Akawaambia, “Inakuwaje basi kwamba Daudi, akinena kwa kuongozwa na Roho, anamwita Kristo ‘Bwana’? Kwa maana asema,

4422:44 1Fal 5:3; Ebr 1:13“ ‘Bwana alimwambia Bwana wangu:

“Keti mkono wangu wa kuume,

hadi nitakapowaweka adui zako

chini ya miguu yako.” ’

45Kama basi Daudi anamwita yeye ‘Bwana,’ awezaje kuwa mwanawe?” 4622:46 Mk 12:34; Lk 20:40Hakuna mtu aliyeweza kumjibu Yesu neno. Tena tangu siku hiyo hakuna aliyethubutu kumuuliza tena maswali.