Mattiyu 20 – HCB & PCB

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 20:1-34

Misalin ma’aikata a gonar inabi

1“Mulkin sama yana kama da wani mai gona, wanda ya fita da sassafe don yă yi hayar mutane su yi aiki a gonar inabinsa. 2Ya yarda yă biya su dinari guda a yini, sai ya tura su gonar inabinsa.

3“Wajen sa’a ta uku, ya fita sai ya ga waɗansu suna tsattsaye a bakin kasuwa ba sa kome. 4Ya ce musu, ‘Ku ma ku tafi gonar inabina ku yi aiki, zan kuwa biya ku abin da ya dace.’ 5Saboda haka suka tafi.

“Ya sāke fita a sa’a ta shida da kuma sa’a ta tara, ya sāke yin haka. 6Wajen sa’a ta goma sha ɗaya, ya sāke fita, ya tarar da waɗansu har yanzu suna tsattsaye. Ya tambaye su, ‘Don me kuke yini tsattsaye a nan ba kwa kome?’

7“Suka amsa, ‘Don ba wanda ya ɗauke mu aiki.’

“Ya ce musu, ‘Ku ma ku je ku yi aiki a gonar inabina.’

8“Sa’ad da yamma ta yi, sai mai gonar inabin ya ce wa wakilinsa, ‘Kira ma’aikatan, ka biya su hakkin aikinsu, fara daga waɗanda aka ɗauke su a ƙarshe har zuwa na farko.’

9“Ma’aikatan da ka ɗauka wajen sa’a ta goma sha ɗaya suka zo, kowannensu kuwa ya karɓi dinari guda. 10Saboda haka da waɗanda aka ɗauka da fari suka zo, sun zaci za su sami fiye da haka. Amma kowannensu ma ya karɓi dinari guda. 11Sa’ad da suka karɓa, sai suka fara yin gunaguni a kan mai gonar. 12Suna cewa, ‘Waɗannan mutanen da aka ɗauka a ƙarshe sun yi aikin sa’a ɗaya ne kawai, ka kuma mai da su daidai da mu da muka yini muna faman aiki, muka kuma sha zafin rana.’

13“Amma ya amsa wa ɗayansu ya ce, ‘Aboki, ban cuce ka ba. Ba ka yarda ka yi aiki a kan dinari guda ba? 14Ka karɓi hakkinka ka tafi. Ni na ga damar ba waɗannan na ƙarshe daidai da yadda na ba ka. 15Ba ni da ikon yin abin da na ga dama da kuɗina ne? Ko kana kishi saboda ni mai kyauta ne?’

16“Saboda haka fa, na ƙarshe za su zama na farko, na farko kuma su zama na ƙarshe.”

Yesu ya sāke yin zancen mutuwarsa

(Markus 10.32-34; Luka 18.31-34)

17To, da Yesu yana haurawa zuwa Urushalima, sai ya ja almajiran nan goma sha biyu gefe, ya ce musu, 18“Za mu haura zuwa Urushalima, za a kuma bashe Ɗan Mutum ga manyan firistoci da malaman dokoki. Za su yi masa hukuncin kisa 19za su kuma bashe shi ga Al’ummai su yi masa ba’a, su yi masa bulala, su kuma gicciye shi. A rana ta uku kuma a tashe shi!”

Roƙon mahaifiya

(Markus 10.35-45)

20Sai mahaifiyar ’ya’yan Zebedin nan ta zo wurin Yesu tare da ’ya’yanta, da ta durƙusa a ƙasa, sai ta roƙe shi yă yi mata wani abu.

21Ya yi tambaya ya ce, “Mene ne kike so?”

Ta ce, “Ka sa daga cikin ’ya’yan nan nawa biyu, ɗaya yă zauna a damarka, ɗaya kuma a hagunka, a mulkinka.”

22Yesu ya ce musu, “Ba ku san abin da kuke roƙo ba. Za ku iya sha daga kwaf da zan sha?”

Suka amsa, “Za mu iya.”

23Yesu ya ce musu, “Tabbatacce za ku sha daga kwaf na, sai dai zama a damana, ko haguna, ba ni nake da izinin bayarwa ba. Waɗannan wurare na waɗanda Ubana ya shirya wa ne.”

24Da goman suka ji haka, sai suka yi fushi da ’yan’uwan nan biyu. 25Yesu ya kira su wuri ɗaya ya ce, “Kun san cewa masu mulkin Al’ummai sukan nuna musu iko, hakimansu kuma sukan gasa musu iko. 26Ba haka zai kasance da ku ba. Maimakon haka, duk mai son zama babba a cikinku, dole yă zama bawanku, 27kuma duk mai son zama shugaba, dole yă zama bawanku, 28kamar yadda Ɗan Mutum bai zo don a bauta masa ba, sai dai don yă yi bauta, yă kuma ba da ransa fansa saboda mutane da yawa.”

Makafi biyu sun sami ganin gari

(Markus 10.46-52; Luka 18.35-43)

29Sa’ad da Yesu da almajiransa suke barin Yeriko, sai wani babban taro ya bi shi. 30Makafi biyu kuwa suna zaune a bakin hanya, da suka ji cewa Yesu yana wucewa, sai suka ɗaga murya suka ce, “Ubangiji, Ɗan Dawuda, ka ji tausayinmu!”

31Mutane suka tsawata musu, suka ce musu su yi shiru. Sai suka ƙara ɗaga murya suna cewa, “Ubangiji, Ɗan Dawuda, ka ji tausayinmu!”

32Yesu ya tsaya ya kira su. Ya tambaye su, “Me kuke so in yi muku?”

33Suka amsa suka ce, “Ubangiji, muna so mu sami ganin gari.”

34Sai Yesu ya ji tausayinsu, ya taɓa idanunsu. Nan da nan kuwa suka sami ganin gari, suka kuma bi shi.

Persian Contemporary Bible

متی‌ٰ 20:1-34

كارفرمای دلسوز

1«وقايع ملكوت خدا را می‌توان به ماجرای صاحب باغی تشبيه كرد كه صبح زود بيرون رفت تا برای باغ خود چند كارگر بگيرد. 2با كارگرها قرار گذاشت كه به هر يک، مزد يک روز كامل را بپردازد؛ سپس همه را به سر كارشان فرستاد.

3«ساعاتی بعد، بار ديگر بيرون رفت و كارگرانی را در ميدان ديد كه بيكار ايستاده‌اند. 4پس، آنان را نيز به باغ خود فرستاد و گفت كه هر چه حقشان باشد، غروب به ايشان خواهد داد. 5نزديک ظهر، و نيز ساعت سه بعد از ظهر، باز عدهٔ بيشتری را به كار گمارد.

6«ساعت پنج بعد از ظهر، بار ديگر رفت و چند نفر ديگر را پيدا كرد كه بيكار ايستاده بودند و پرسيد:

«چرا تمام روز اينجا بيكار مانده‌ايد؟

7«جواب دادند: هيچكس به ما كار نداد.

«به ايشان گفت: برويد به باغ من و كار كنيد.

8«غروب آن روز، صاحب باغ به سركارگر خود گفت كه كارگرها را فرا بخواند و از آخرين تا اولين نفر، مزدشان را بپردازد. 9به كسانی كه ساعت پنج به كار مشغول شده بودند، مزد يک روز تمام را داد. 10در آخر، نوبت كارگرانی شد كه اول از همه به كار مشغول شده بودند؛ ايشان انتظار داشتند بيشتر از ديگران مزد بگيرند. ولی به آنان نيز همان مقدار داده شد.

11‏-12«پس ايشان به صاحب باغ شكايت كرده، گفتند: به اينها كه فقط يک ساعت كار كرده‌اند، به اندازهٔ ما داده‌ايد كه تمام روز زير آفتاب سوزان جان كنده‌ايم؟

13«مالک باغ رو به يكی از ايشان كرده، گفت: ای رفيق، من كه به تو ظلمی نكردم. مگر تو قبول نكردی با مزد يک روز كار كنی؟ 14پس مزد خود را بگير و برو. دلم می‌خواهد به همه يک اندازه مزد بدهم. 15آيا من حق ندارم هر طور كه دلم می‌خواهد پولم را خرج كنم؟ آيا اين درست است كه تو از سخاوت من دلخور شوی؟

16«بلی، اينچنين است كه آنانی كه اول هستند، آخر می‌شوند و آنانی كه آخرند، اول.»

آخرين سفر عيسی به اورشليم

17در راه اورشليم، عيسی دوازده شاگرد خود را به كناری كشيد 18و به آنها گفت كه در اورشليم چه سرنوشتی در انتظار اوست؛ او فرمود:

«مرا كه مسيحم خواهند گرفت و نزد رئيس كاهنان و علمای مذهبی خواهند برد و به مرگ محكوم خواهند كرد. 19آنان نيز مرا به رومی‌ها تحويل خواهند داد. ايشان مرا مسخره كرده، شلاق خواهند زد و به صليب خواهند كشيد. اما من روز سوم زنده خواهم شد.»

تعليم عيسی درباره خدمت به مردم

20آنگاه مادر يعقوب و يوحنا، پسران زبدی، دو پسر خود را نزد عيسی آورده، او را تعظيم كرد و خواهش نمود كه درخواست او را اجابت كند.

21عيسی پرسيد: «چه درخواستی داری؟»

آن زن جواب داد: «وقتی در ملكوت خود، بر تخت سلطنت نشستيد، اجازه بفرماييد يكی از پسرانم در دست راست و ديگری در دست چپتان بنشينند.»

22عيسی در جواب او فرمود: «تو نمی‌دانی چه می‌خواهی!» سپس رو كرد به يعقوب و يوحنا و از ايشان پرسيد: «آيا می‌توانيد از جام تلخی كه من بايد بزودی بنوشم، شما نيز بنوشيد، آيا می‌توانيد مانند من متحمل رنج و عذاب بشويد؟»

جواب دادند: «بلی، می‌توانيم.»

23عيسی به ايشان فرمود: «درست است، شما از اين جام خواهيد نوشيد و متحمل رنج و عذاب خواهيد شد، اما من اين اختيار را ندارم كه بگويم چه كسی در دست راست يا چپ من بنشيند. اين جای‌ها برای كسانی نگاه داشته شده كه پدرم آنها را قبلاً انتخاب كرده است.»

24ده شاگرد ديگر وقتی فهميدند يعقوب و يوحنا چه درخواستی كرده‌اند، از آن دو برادر سخت رنجيدند.

25ولی عيسی همهٔ شاگردان را فرا خوانده، گفت: «در اين دنيا، حكمرانان بر مردم آقايی می‌كنند و رؤسا به زيردستان خود دستور می‌دهند. 26ولی شما چنين نباشيد. اگر كسی از شما می‌خواهد در ميان شما از همه بزرگتر باشد، بايد خدمتگزار همه باشد؛ 27و اگر می‌خواهد مقامش از همه بالاتر باشد، بايد غلام همه باشد. 28چون من كه مسيحم، نيامدم تا به من خدمت كنند؛ من آمدم تا به مردم خدمت كنم و جانم را در راه نجات بسياری فدا سازم.»

عيسی به دو كور، بينايی می‌بخشد

29وقتی عيسی و شاگردانش از شهر اريحا خارج می‌شدند، جمعيت انبوهی به دنبال ايشان به راه افتاد.

30در همين هنگام، دو كور كه كنار جاده نشسته بودند، چون شنيدند كه عيسی از آنجا می‌گذرد، صدای خود را بلند كرده، فرياد زدند: «ای سَروَر ما، ای پسر داوود پادشاه، بر ما رحم كنيد.»

31مردم كوشيدند ايشان را ساكت سازند، اما آنان صدای خود را بلندتر و بلندتر می‌كردند.

32‏-33سرانجام وقتی عيسی به آنجا رسيد، ايستاد و از ايشان پرسيد: «چه می‌خواهيد برايتان انجام دهم؟»

جواب دادند: «سَروَر ما، می‌خواهيم چشمانمان باز شود!»

34عيسی دلش به حال ايشان سوخت و دست بر چشمانشان گذاشت. چشمان ايشان فوری باز شد و توانستند ببينند. پس به دنبال عيسی رفتند.