Mattiyu 2 – HCB & PCB

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 2:1-23

Ziyarar Masana

1Bayan an haifi Yesu a Betlehem, a Yahudiya, a zamanin Sarki Hiridus, sai waɗansu Masana,2.1 A al’adance Masu Hikima daga gabas suka zo Urushalima 2suka yi tambaya suka ce, “Ina shi wanda aka haifa sarkin Yahudawa? Gama mun ga tauraronsa a gabas2.2 Ko kuwa a tauraro sa’ad da ya taso mun kuwa zo ne domin mu yi masa sujada.”

3Da Sarki Hiridus ya ji wannan, sai hankalinsa ya tashi haka ma na dukan Urushalima. 4Bayan ya kira dukan manyan firistoci da malaman dokoki na mutane wuri ɗaya, sai ya tambaye su inda za a haifi Kiristi. 5Suka amsa suka ce, “A Betlehem ne, cikin Yahudiya, gama haka annabin ya rubuta.

6“ ‘Amma ke Betlehem, a cikin ƙasar Yahuda,

ba ke ce mafi ƙanƙanta a cikin masu mulki a Yahuda ba,

gama daga cikinki mai mulki zai zo,

wanda zai zama makiyayin mutanena Isra’ila.’2.6 Mik 5.2

7Sai Hiridus ya kira Masanan nan a ɓoye, yă gano daga wurinsu daidai lokacin da tauraron ya bayyana. 8Sai ya aike su Betlehem ya ce, “Ku je ku binciko a hankali game da yaron nan. Da kun same shi, sai ku kawo mini labari nan da nan, domin ni ma in je in yi masa sujada.”

9Bayan sun saurari sarki, sai suka kama hanyarsu, tauraron da suka gani a gabas kuwa yana tafe a gabansu, sai da ya kai inda yaron yake. 10Da suka ga tauraron, sai suka yi farin ciki ƙwarai. 11Suka shiga gidan, suka kuwa ga yaron tare da mahaifiyarsa Maryamu. Suka durƙusa har ƙasa, suka yi masa sujada. Sa’an nan suka kunce dukiyarsu, suka miƙa masa kyautai na zinariya da na turare da na mur. 12Bayan an gargaɗe su cikin mafarki kada su koma wurin Hiridus, sai suka koma ƙasarsu ta wata hanya dabam.

Tserewa zuwa Masar

13Bayan sun tafi, sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusuf a mafarki ya ce, “Tashi, ka ɗauki yaron da mahaifiyarsa, ku gudu zuwa Masar. Ku zauna a can sai na gaya muku, gama Hiridus zai nemi yaron don yă kashe.”

14Sai Yusuf ya tashi, ya ɗauki yaron da mahaifiyarsa da dad dare suka tafi Masar, 15inda ya zauna har sai da Hiridus ya mutu. Ta haka kuwa aka cika abin da Ubangiji ya faɗa ta bakin annabin cewa, “Daga Masar na kira ɗana.”2.15 Hos 11.1

16Da Hiridus ya gane cewa Masanan nan sun yi masa wayo, sai ya husata ƙwarai, ya yi umarni cewa a karkashe dukan ’yan yara maza da suke a Betlehem da kewayenta, daga masu shekara biyu zuwa ƙasa, bisa ga lokacin da ya sami labarin daga Masanan nan. 17Sai abin da aka faɗa ta bakin annabi Irmiya ya cika, cewa,

18“An ji murya a Rama,

tana kuka da makoki mai tsanani,

Rahila ce take kuka domin ’ya’yanta,

an kāsa ta’azantar da ita,

don ba su.”2.18 Irm 31.15

Komowa zuwa Nazaret

19Bayan Hiridus ya mutu, sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana ga Yusuf a mafarki a Masar, 20ya ce, “Tashi, ka ɗauki yaron da mahaifiyarsa ku tafi ƙasar Isra’ila, domin waɗanda suke neman ran yaron sun mutu.”

21Sai ya tashi, ya ɗauki yaron da mahaifiyarsa suka tafi ƙasar Isra’ila. 22Amma da ya ji Arkelawus ne yake mulki a Yahudiya a matsayin wanda ya gāji mahaifinsa Hiridus, sai ya ji tsoron zuwa can. Bayan an gargaɗe shi a mafarki, sai ya ratse zuwa gundumar Galili, 23ya je ya zauna a wani garin da ake kira Nazaret. Ta haka aka cika abin da aka faɗa ta bakin annabawa cewa, “Za a ce da shi Banazare.”

Persian Contemporary Bible

متی‌ٰ 2:1-23

ستاره‌شناسان در جستجوی عيسی

1عيسی در زمان سلطنت «هيروديس»، در شهر «بيت‌لحم» يهوديه به دنیا آمد.

در آن هنگام چند مجوسِ ستاره‌شناس از مشرق زمين به اورشليم آمده، پرسيدند: 2«كجاست آن كودكی كه بايد پادشاه يهود گردد؟ ما ستارهٔ او را در سرزمينهای دور دست شرق ديده‌ايم و آمده‌ايم تا او را بپرستيم.»

3وقتی اين مطلب به گوش هيروديس پادشاه رسيد، سخت پريشان شد. تمام مردم اورشليم نيز از ماجرا آگاهی يافتند. 4او تمام علمای مذهبی قوم يهود را فرا خواند و از ايشان پرسيد: «طبق پيشگويی پيامبران، مسيح در كجا بايد به دنیا آيد؟»

5ايشان پاسخ دادند: «بايد در بيت‌لحم متولد شود زيرا ميكای نبی چنين پيشگويی كرده است: 6ای بيت‌لحم، ای شهر كوچک، تو در يهوديه، دهكده‌ای بی‌ارزش نيستی، زيرا از تو پيشوايی ظهور خواهد كرد كه قوم بنی‌اسرائيل را رهبری خواهد نمود.»

7آنگاه هيروديس پيام محرمانه‌ای برای مجوسيان ستاره‌شناس فرستاد و از ايشان خواست تا به ملاقات او بيايند و به او اطلاع دهند كه اولين بار ستاره را در چه زمانی ديده‌اند. 8پس به ايشان گفت: «به بيت‌لحم برويد و به دقت به جستجوی آن طفل بپردازيد. آنگاه نزد من بازگشته، به من خبر دهيد تا من نيز بروم و او را بپرستم.»

9پس از اين گفتگو، ستاره‌شناسان به راه خود ادامه دادند. ناگهان ستاره را ديدند كه در پيشاپيش آنان حركت می‌كند، تا به بيت‌لحم رسيده، بالای جايی كه كودک در آنجا بود ايستاد. 10ستاره‌شناسان از شادی در پوست نمی‌گنجيدند.

11وقتی وارد خانه‌ای شدند كه كودک و مادرش مريم در آن بودند، پيشانی بر خاک نهاده، كودک را پرستش كردند. سپس هدايای خود را گشودند و طلا و عطر و مواد خوشبو به او تقديم كردند. 12اما در راه بازگشت به وطن، از راه اورشليم مراجعت نكردند تا به هيروديس گزارش بدهند، زيرا خداوند در خواب به آنها فرموده بود كه از راه ديگری به وطن بازگردند.

فرار به مصر

13پس از رفتن ستاره‌شناسان، فرشتهٔ خداوند در خواب بر يوسف ظاهر شد و گفت: «برخيز و كودک و مادرش را برداشته، به مصر فرار كن، و همانجا بمان تا تو را خبر دهم؛ زيرا هيروديس پادشاه می‌خواهد كودک را به قتل برساند.» 14يوسف همان شب مريم و كودک را برداشت و به سوی مصر رفت، 15و تا زمان مرگ هيروديس در آنجا ماند. يكی از انبیا قرنها پيش دربارهٔ اين موضوع پيشگويی كرده و گفته بود: «پسر خود را از مصر فرا خواندم.»

16اما وقتی هيروديس متوجه شد كه ستاره‌شناسان از دستور او سرپيچی كرده‌اند، بسيار خشمگين شد و سربازانی به بيت‌لحم فرستاد تا تمام كودكان دو ساله و كمتر را كه در آن شهر و در تمام حومهٔ آن بودند قتل عام كنند، زيرا طبق گفتهٔ ستاره‌شناسان، ستاره دو سال پيش از آن ظاهر شده بود. 17اين رفتار بی‌رحمانهٔ هيروديس را قبلاً ارميای نبی چنين پيشگويی كرده بود:

18«صدای گريه و ماتم از رامه به گوش می‌رسد. راحيل برای فرزندانش می‌گريد و آرام نمی‌گيرد، چون فرزندانش مرده‌اند.»

بازگشت از مصر

19پس از مرگ هيروديس، در مصر فرشتهٔ خداوند در خواب بر يوسف ظاهر شد و به او گفت: 20«برخيز و كودک و مادرش را بردار و به سرزمين اسرائيل بازگرد، چون كسی كه قصد قتل كودک را داشت، خودش مرده است.»

21پس يوسف بی‌درنگ با كودک و مادرش به اسرائيل بازگشت. 22اما در راه، وقتی شنيد كه پسر هيروديس، «آركلائوس»، جانشين پدرش شده و در يهوديه سلطنت می‌كند، ترسيد. باز در عالم خواب به او وحی رسيد كه به يهوديه نرود. پس او به ايالت جليل رفت و 23در شهر ناصره ساكن شد. باز در اينجا پيشگويی انبيا جامهٔ عمل پوشيد كه: «او ناصری خوانده خواهد شد.»