Mattiyu 19 – HCB & SNC

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 19:1-30

Kashen aure

(Markus 10.1-12)

1Sa’ad da Yesu ya gama faɗin waɗannan abubuwa, sai ya bar Galili, ya tafi yankin Yahudiya a ɗaya gefen Urdun. 2Taron mutane mai yawa suka bi shi, ya kuwa warkar da su a can.

3Waɗansu Farisiyawa suka zo wurinsa don su gwada shi. Suka yi tambaya suka ce, “Daidai ne mutum yă saki matarsa saboda wani dalili da kuma a kan kowane dalili?”

4Ya amsa ya ce, “Ba ku taɓa karantawa ba ne cewa, a farkon halitta, Mahalicci ‘ya yi su namiji da ta mace,’19.4 Far 1.27 5ya kuma ce, ‘Saboda wannan dalili, namiji zai bar mahaifinsa da mahaifiyarsa yă manne wa matarsa, biyun kuwa su zama jiki guda’?19.5 Far 2.24 6Ta haka, ba sa ƙara zama biyu, sai dai ɗaya. Saboda haka abin da Allah ya haɗa fa, kada mutum yă raba.”

7Suka yi tambaya, suka ce, “To, me ya sa Musa ya umarta cewa mutum yă ba wa matarsa takardar saki, yă kuma kore ta?”

8Yesu ya amsa ya ce, “Musa ya ba ku izini ku saki matanku saboda taurin zuciyarku ne. Amma ba haka yake ba daga farko. 9Ina faɗa muku cewa duk wanda ya saki matarsa, sai dai a kan rashin aminci a cikin aure, ya kuwa auri wata, ya yi zina ke nan.”

10Almajiran suka ce masa, “In haka yake tsakanin miji da mata, ashe, ya ma fi kyau kada a yi aure.”

11Yesu ya ce, “Ba kowa ba ne zai yarda da wannan magana, sai dai waɗanda aka yarda musu. 12Gama waɗansu bābānni ne domin haka aka haife su; waɗansu kuwa mutane ne suka mai da su haka; waɗansu kuma sun ƙi aure ne saboda mulkin sama. Duk mai iya ɗaukar wannan yă ɗauka.”

Yesu da ƙananan yara

(Markus 10.13-16; Luka 18.15-17)

13Sa’an nan aka kawo yara ƙanana wurin Yesu don yă ɗibiya musu hannuwansa, yă kuma yi musu addu’a. Amma almajirai suka tsawata wa waɗanda suka kawo su.

14Yesu ya ce, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina, kada ku hana su, gama mulkin sama na irin waɗannan ne.” 15Sa’ad da ya ɗibiya musu hannuwansa, sai ya tafi abinsa.

Saurayi mai arziki

(Markus 10.17-31; Luka 18.18-30)

16To, fa, sai ga wani ya zo wurin Yesu ya tambaye shi ya ce, “Malam, wane abu mai kyau ne ya zama mini dole in yi don in sami rai madawwami?”

17Yesu ya amsa ya ce, “Don me kake tambayata game da abin da yake mai kyau? Akwai Mai kyau Ɗaya kaɗai. In kana so ka sami rai madawwami, ka kiyaye dokokin nan.”

18Mutumin ya yi tambaya ya ce, “Waɗanne?”

Yesu ya amsa ya ce, “ ‘Kada ka yi kisankai, kada ka yi zina, kada ka yi sata, kada ka yi shaidar ƙarya, 19ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka,’19.19 Fit 20.12-16; M Sh 5.16-20 ka kuma ‘ƙaunaci maƙwabcinka kamar kanka.’19.19 Fir 19.18

20Saurayin ya ce, “Duk waɗannan na kiyaye. Me kuma ya rage mini?”

21Yesu ya amsa ya ce, “In kana so ka zama cikakke, ka je, ka sayar da dukan dukiyarka ka kuma ba matalauta, za ka kuwa sami dukiya a sama. Sa’an nan ka zo, ka bi ni.”

22Da saurayin ya ji haka, sai ya tafi rai a ɓace, don yana da arziki sosai.

23Sa’an nan Yesu ya ce wa almajiransa, “Gaskiya nake gaya muku, yana da wuya mai arziki yă shiga mulkin sama. 24Har wa yau ina gaya muku, zai fi sauƙi raƙumi yă shiga ta kafar allura, da mai arziki yă shiga mulkin Allah.”

25Sa’ad da almajiran suka ji wannan, sai suka yi mamaki ƙwarai. Suka yi tambaya suka ce, “To, wa zai sami ceto ke nan?”

26Yesu ya kalle su ya ce, “Ga mutum kam, wannan ba ya yiwuwa, amma ga Allah kuwa, dukan abubuwa masu yiwuwa ne.”

27Sai Bitrus ya amsa masa, “Ga shi mun bar kome don mu bi ka! Me za mu samu ke nan?”

28Yesu ya ce musu, “Gaskiya nake gaya muku, a lokacin sabunta dukan kome, sa’ad da Ɗan Mutum ya zauna a kan kursiyinsa mai daraja, ku da kuka bi ni, ku ma za ku zauna a kan kursiyoyi goma sha biyu, kuna yi wa kabilu goma sha biyu na Isra’ila shari’a. 29Duk kuma wanda ya bar gidaje ko ’yan’uwa maza ko ’yan’uwa mata ko mahaifi ko mahaifiya ko yara ko gonaki, saboda ni, zai sami abin da ya fi haka riɓi ɗari, yă kuma gāji rai madawwami. 30Amma da yawa da suke na farko, za su zama na ƙarshe, da yawa kuma da suke na ƙarshe, za su zama na farko.

Slovo na cestu

Matouš 19:1-30

Ježíš učí o manželství a rozvodu

1Po tomto hovoru Ježíš odešel do Judska za Jordánem.

2Mnoho lidí šlo za ním a on uzdravoval nemocné. 3Přišli za ním i farizejové a chtěli ho vyprovokovat k nějakému výroku, který by mohli použít proti němu. „Může se člověk rozvést z jakéhokoliv důvodu?“ zeptali se.

4-6On odpověděl: „Nečetli jste v Písmu, že když na počátku Bůh stvořil muže a ženu, ustanovil: Muž opustí své rodiče, připojí se ke své ženě a stanou se jednou bytostí? Nikdo nemá právo rozdělit to, co Bůh spojil.“

7Oni však namítali: „Proč tedy Mojžíš řekl, že muž může propustit manželku jednoduše tím, že jí dá rozlukový lístek?“

8Ježíš odpověděl: „Toto ustanovení Mojžíšova zákona je ústupkem vaší tvrdosti a nesnášenlivosti. Původní Boží úmysl to však nikdy nebyl. 9Já vám říkám, že kdo se rozvádí z jiného důvodu, než je cizoložství jeho partnera, a uzavírá nový sňatek, dopouští se sám cizoložství.“

10Učedníci mu řekli: „Když mohou nastat takové těžkosti mezi mužem a ženou, pak je lepší se neženit.“ 11On odpověděl: „Tak jednoduché to není. Je zde nutné porozumět Boží vůli. 12Jsou tři důvody proto, aby člověk zůstal svobodný: když je k manželství od narození nezpůsobilý, když mu v uzavření sňatku zabránili lidé, nebo když se manželství zřekne dobrovolně pro plnou službu Boží věci. Rozumíte tomu?“

Ježíš žehná malým dětem

13Potom k Ježíšovi nosili malé děti, aby jim žehnal a modlil se za ně. Učedníci však domlouvali těm, kteří děti přivedli, aby Ježíše neobtěžovali. 14On jim ale řekl: „Nechte je, ať jdou ke mně, a nebraňte jim. Jejich místo je u mne.“ 15Kladl na ně ruce a žehnal jim. Pak odtud odešel.

Ježíš mluví s bohatým mužem

16Za Ježíšem přišel jeden mladý člověk a ptal se ho: „Mistře, jakými dobrými skutky mohu získat věčný život?“

17Ježíš mu na to řekl: „Snažíš se být dobrý? To se chceš vyrovnat Bohu, který jediný je skutečně dobrý! Plň jeho přikázání a budeš věčně živ.“

18„Která to jsou?“ zeptal se mladý muž.

Ježíš odpověděl: „Nezabiješ, nezcizoložíš, nebudeš krást, lhát, 19budeš ctít svoje rodiče, své bližní budeš milovat jako sebe!“

20Mladík na to řekl: „To všechno jsem vždycky dodržoval. Co mi ještě chybí?“

21Ježíš odpověděl: „Chceš-li být dokonalý, jdi a prodej celý svůj majetek a peníze rozdej chudým, a tak budeš mít poklad v nebi. Pak se vrať a staň se mým učedníkem.“

22Mladík zesmutněl a zklamaně odešel. Měl totiž velký majetek. 23Ježíš pak řekl svým učedníkům: „Pro zámožného člověka je velmi nesnadné postavit se na Boží stranu. 24Kdybych to měl k něčemu přirovnat, pak snáze projde velbloud uchem jehly, nežli bohatý branou Božího království.“ 25Učedníky to překvapilo a ptali se: „Kdo tedy vůbec může být spasen?“

26Ježíš se na ně zadíval a řekl: „V lidských silách to není, ale Bůh dokáže všechno.“

27Petr se ozval a řekl: „My jsme se vzdali všeho a jdeme za tebou. Co nás čeká?“

28Ježíš odpověděl: „Ujišťuji vás, že až přijdu, abych stvořil nový svět, nad kterým budu panovat v plné slávě, pak vás dvanáct, kteří mne následujete, posadím po svém boku jako soudce celého Izraele. 29A každému, kdo se vzdá domova, bratrů, sester, otce, matky, manželky, dětí nebo majetku proto, aby šel za mnou, všechno mu mnohokrát vynahradím a bude mít podíl na věčném životě. 30Mnozí první budou poslední a poslední budou první.