Mattiyu 15 – HCB & NIRV

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 15:1-39

Mai tsabta da marar tsabta

(Markus 7.1-13)

1Sa’an nan waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki suka zo wurin Yesu daga Urushalima suka yi tambaya suka ce, 2“Me ya sa almajiranka suke karya al’adun dattawa? Ba sa wanke hannuwansu kafin su ci abinci!”

3Yesu ya amsa ya ce, “Ku ma me ya sa kuke karya dokar Allah saboda al’adarku? 4Gama Allah ya ce, ‘Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka,15.4 Fit 20.12; M Sh 5.16 kuma duk wanda ya zagi mahaifinsa ko mahaifiyarsa dole a kashe shi.’15.4 Fit 21.17; Fir 20.9 5Amma ku kukan ce, in wani ya ce wa mahaifinsa ko mahaifiyarsa, ‘Duk taimakon da dā ya kamata za ku samu daga gare ni an ba wa Allah,’ 6ba zai ‘girmama mahaifinsa’ da shi ba. Ta haka kun yi banza da maganar Allah saboda al’adarku. 7Ku munafukai! Daidai ne Ishaya ya yi annabci a kanku da ya ce,

8“ ‘Waɗannan mutane da baki kawai suke girmama ni,

amma zukatansu suna nesa da ni.

9A banza suke mini sujada,

koyarwarsu, dokoki ne kawai da mutane suke koyarwa.’ ”15.9 Ish 29.13

(Markus 7.14-23)

10Sai Yesu ya kira taron wurinsa ya ce, “Ku saurara ku kuma gane. 11Abin da yake shiga bakin mutum ba ya ƙazantar da shi, sai dai abin da yake fitowa daga bakinsa, shi ne yake ƙazantar da shi.”

12Sai almajiran suka zo wurinsa suka ce, “Ka san cewa Farisiyawa ba su ji daɗi sa’ad da suka ji wannan ba?”

13Ya amsa ya ce, “Duk tsiron da Ubana na sama bai shuka ba, za a tumɓuke shi daga saiwoyi. 14Ku ƙyale su, ai, makafin jagorai ne.15.14 Waɗansu rubuce-rubucen hannu na dā suna da jagorai ne na makafi In makaho ya yi wa makaho jagora, dukansu za su fāɗa a rami.”

15Bitrus ya ce, “Ka bayyana mana wannan misali.”

16Yesu ya tambaye su ya ce, “Har yanzu ba ku gane ba ne? 17Ba ku gane cewa duk abin da ya shiga baki yakan wuce ciki ne daga nan kuma yă fita daga jiki ba? 18Amma abubuwan da suke fitowa ta baki suna fitowa ne daga zuciya, su ne kuma suke ƙazantar da mutum. 19Gama daga zuciya ne mugayen tunani, kisankai, zina, fasikanci, sata, shaidar ƙarya, ɓatan suna, suka fitowa. 20Waɗannan su ne suke ƙazantar da mutum; amma cin abinci ba tare da wanke hannuwa ba, ba ya ƙazantar da mutum.”

Bangaskiyar mutuniyar Kan’ana

(Markus 7.24-30)

21Barin wurin ke nan, sai Yesu ya janye zuwa yankin Taya da Sidon. 22Wata mutuniyar Kan’ana daga wajajen ta zo wurinsa, tana ihu tana cewa, “Ubangiji, Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai! ’Yata tana shan wahala ƙwarai daga aljanin da yake cikinta.”

23Yesu bai ce mata uffam ba. Saboda haka almajiransa suka zo wurinsa suka roƙe shi suka ce, “Ka kore ta tă tafi, tana ta binmu tana damunmu da ihu.”

24Ya amsa ya ce, “An aiko ni wurin ɓatattun tumakin Isra’ila ne kaɗai.”

25Sai macen ta zo ta durƙusa a gabansa ta ce, “Ubangiji, ka taimake ni!”

26Ya amsa ya ce, “Ba daidai ba ne a ɗauki abincin yara a jefa wa karnukansu.”

27Ta amsa, ta ce, “I, Ubangiji, amma karnuka ma sukan ci gutsattsarin da sukan fāɗi daga teburin maigidansu.”

28Sa’an nan Yesu ya amsa ya ce, “Mace, kina da bangaskiya mai yawa! An biya miki bukatarki.” ’Yarta kuwa ta warke nan take.

Yesu ya ciyar da dubu huɗu

29Yesu ya tashi daga nan ya bi ta gefen Tekun Galili. Sa’an nan ya haura gefen wani dutse ya zauna. 30Taron mutane mai girma kuwa suka zo wurinsa, suna kawo masa guragu, makafi, shanyayyu, kurame da dai waɗansu da yawa, suka kuwa kwantar da su a gabansa; ya kuma warkar da su. 31Mutanen kuwa suka yi mamaki sa’ad da suka ga kurame suna magana, shanyayyu suna samun lafiya, guragu suna takawa, makafi kuma suna ganin gari. Sai suka yabi Allah na Isra’ila.

(Markus 8.1-10)

32Yesu ya kira almajiransa wurinsa ya ce, “Ina jin tausayin mutanen nan; gama kwana uku ke nan suke tare da ni ba abin da za su ci. Ba na so in sallame su da yunwa, don kada su kāsa a hanya.”

33Sai almajiransa suka amsa suka ce, “Ina za mu sami isashen burodi a wannan wurin da babu kowa mu ciyar da irin taron nan?”

34Yesu ya tambaye su, “Burodi guda nawa kuke da shi?”

Suka amsa suka ce, “Guda bakwai da ’yan ƙananan kifaye.”

35Ya sa taron su zazzauna a ƙasa. 36Sa’an nan ya ɗauki burodi guda bakwai da kuma kifayen nan, da ya yi godiya, sai ya kakkarya su ya ba wa almajiran, su kuma suka ba wa mutane. 37Duk kuwa suka ci, suka ƙoshi. Daga baya almajiran suka kwashe ragowar gutsattsarin cike da kwanduna bakwai. 38Yawan waɗanda suka ci kuwa, maza dubu huɗu ne, ban da mata da yara. 39Bayan Yesu ya sallami taron, sai ya shiga jirgin ruwa ya tafi wajajen Magadan.

New International Reader’s Version

Matthew 15:1-39

What Makes People “Unclean”?

1Some Pharisees and some teachers of the law came from Jerusalem to see Jesus. They asked, 2“Why don’t your disciples obey what the elders teach? Your disciples don’t wash their hands before they eat!”

3Jesus replied, “And why don’t you obey God’s command? You would rather follow your own teachings! 4God said, ‘Honor your father and mother.’ (Exodus 20:12; Deuteronomy 5:16) He also said, ‘Anyone who asks for bad things to happen to their father or mother must be put to death.’ (Exodus 21:17; Leviticus 20:9) 5But suppose people have something that might be used to help their parents. You allow them to say it is instead ‘a gift set apart for God.’ 6So they do not need to honor their father or mother with their gift. You make the word of God useless in order to follow your own teachings. 7You pretenders! Isaiah was right when he prophesied about you. He said,

8“ ‘These people honor me by what they say.

But their hearts are far away from me.

9Their worship doesn’t mean anything to me.

They teach nothing but human rules.’ ” (Isaiah 29:13)

10Jesus called the crowd to him. He said, “Listen and understand. 11What goes into someone’s mouth does not make them ‘unclean.’ It’s what comes out of their mouth that makes them ‘unclean.’ ”

12Then the disciples came to him. They asked, “Do you know that the Pharisees were angry when they heard this?”

13Jesus replied, “They are plants that my Father in heaven has not planted. They will be pulled up by the roots. 14Leave the Pharisees. They are blind guides. If one blind person leads another blind person, both of them will fall into a pit.”

15Peter said, “Explain this to us.”

16“Don’t you understand yet?” Jesus asked them. 17“Don’t you see? Everything that enters the mouth goes into the stomach. Then it goes out of the body. 18But the things that come out of a person’s mouth come from the heart. Those are the things that make someone ‘unclean.’ 19Evil thoughts come out of a person’s heart. So do murder, adultery, and other sexual sins. And so do stealing, false witness, and telling lies about others. 20Those are the things that make you ‘unclean.’ But eating without washing your hands does not make you ‘unclean.’ ”

The Faith of a Woman From Canaan

21Jesus left Galilee and went to the area of Tyre and Sidon. 22A woman from Canaan lived near Tyre and Sidon. She came to him and cried out, “Lord! Son of David! Have mercy on me! A demon controls my daughter. She is suffering terribly.”

23Jesus did not say a word. So his disciples came to him. They begged him, “Send her away. She keeps crying out after us.”

24Jesus answered, “I was sent only to the people of Israel. They are like lost sheep.”

25Then the woman fell to her knees in front of him. “Lord! Help me!” she said.

26He replied, “It is not right to take the children’s bread and throw it to the dogs.”

27“Yes it is, Lord,” she said. “Even the dogs eat the crumbs that fall from their owner’s table.”

28Then Jesus said to her, “Woman, you have great faith! You will be given what you are asking for.” And her daughter was healed at that moment.

Jesus Feeds Four Thousand

29Jesus left there. He walked along the Sea of Galilee. Then he went up on a mountainside and sat down. 30Large crowds came to him. They brought blind people and those who could not walk. They also brought disabled people, those who could not speak, and many others. They laid them at his feet, and he healed them. 31The people were amazed. Those who could not speak were speaking. The disabled were made well. Those not able to walk were walking. Those who were blind could see. So the people praised the God of Israel.

32Then Jesus called for his disciples to come to him. He said, “I feel deep concern for these people. They have already been with me three days. They don’t have anything to eat. I don’t want to send them away hungry. If I do, they will become too weak on their way home.”

33His disciples answered him. “There is nothing here,” they said. “Where could we get enough bread to feed this large crowd?”

34“How many loaves do you have?” Jesus asked.

“Seven,” they replied, “and a few small fish.”

35Jesus told the crowd to sit down on the ground. 36He took the seven loaves and the fish and gave thanks. Then he broke them and gave them to the disciples. And the disciples passed them out to the people. 37All of them ate and were satisfied. After that, the disciples picked up seven baskets of leftover pieces. 38The number of men who ate was 4,000. Women and children also ate. 39After Jesus had sent the crowd away, he got into the boat. He went to the area near Magadan.