Mattiyu 15 – HCB & HHH

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 15:1-39

Mai tsabta da marar tsabta

(Markus 7.1-13)

1Sa’an nan waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki suka zo wurin Yesu daga Urushalima suka yi tambaya suka ce, 2“Me ya sa almajiranka suke karya al’adun dattawa? Ba sa wanke hannuwansu kafin su ci abinci!”

3Yesu ya amsa ya ce, “Ku ma me ya sa kuke karya dokar Allah saboda al’adarku? 4Gama Allah ya ce, ‘Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka,15.4 Fit 20.12; M Sh 5.16 kuma duk wanda ya zagi mahaifinsa ko mahaifiyarsa dole a kashe shi.’15.4 Fit 21.17; Fir 20.9 5Amma ku kukan ce, in wani ya ce wa mahaifinsa ko mahaifiyarsa, ‘Duk taimakon da dā ya kamata za ku samu daga gare ni an ba wa Allah,’ 6ba zai ‘girmama mahaifinsa’ da shi ba. Ta haka kun yi banza da maganar Allah saboda al’adarku. 7Ku munafukai! Daidai ne Ishaya ya yi annabci a kanku da ya ce,

8“ ‘Waɗannan mutane da baki kawai suke girmama ni,

amma zukatansu suna nesa da ni.

9A banza suke mini sujada,

koyarwarsu, dokoki ne kawai da mutane suke koyarwa.’ ”15.9 Ish 29.13

(Markus 7.14-23)

10Sai Yesu ya kira taron wurinsa ya ce, “Ku saurara ku kuma gane. 11Abin da yake shiga bakin mutum ba ya ƙazantar da shi, sai dai abin da yake fitowa daga bakinsa, shi ne yake ƙazantar da shi.”

12Sai almajiran suka zo wurinsa suka ce, “Ka san cewa Farisiyawa ba su ji daɗi sa’ad da suka ji wannan ba?”

13Ya amsa ya ce, “Duk tsiron da Ubana na sama bai shuka ba, za a tumɓuke shi daga saiwoyi. 14Ku ƙyale su, ai, makafin jagorai ne.15.14 Waɗansu rubuce-rubucen hannu na dā suna da jagorai ne na makafi In makaho ya yi wa makaho jagora, dukansu za su fāɗa a rami.”

15Bitrus ya ce, “Ka bayyana mana wannan misali.”

16Yesu ya tambaye su ya ce, “Har yanzu ba ku gane ba ne? 17Ba ku gane cewa duk abin da ya shiga baki yakan wuce ciki ne daga nan kuma yă fita daga jiki ba? 18Amma abubuwan da suke fitowa ta baki suna fitowa ne daga zuciya, su ne kuma suke ƙazantar da mutum. 19Gama daga zuciya ne mugayen tunani, kisankai, zina, fasikanci, sata, shaidar ƙarya, ɓatan suna, suka fitowa. 20Waɗannan su ne suke ƙazantar da mutum; amma cin abinci ba tare da wanke hannuwa ba, ba ya ƙazantar da mutum.”

Bangaskiyar mutuniyar Kan’ana

(Markus 7.24-30)

21Barin wurin ke nan, sai Yesu ya janye zuwa yankin Taya da Sidon. 22Wata mutuniyar Kan’ana daga wajajen ta zo wurinsa, tana ihu tana cewa, “Ubangiji, Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai! ’Yata tana shan wahala ƙwarai daga aljanin da yake cikinta.”

23Yesu bai ce mata uffam ba. Saboda haka almajiransa suka zo wurinsa suka roƙe shi suka ce, “Ka kore ta tă tafi, tana ta binmu tana damunmu da ihu.”

24Ya amsa ya ce, “An aiko ni wurin ɓatattun tumakin Isra’ila ne kaɗai.”

25Sai macen ta zo ta durƙusa a gabansa ta ce, “Ubangiji, ka taimake ni!”

26Ya amsa ya ce, “Ba daidai ba ne a ɗauki abincin yara a jefa wa karnukansu.”

27Ta amsa, ta ce, “I, Ubangiji, amma karnuka ma sukan ci gutsattsarin da sukan fāɗi daga teburin maigidansu.”

28Sa’an nan Yesu ya amsa ya ce, “Mace, kina da bangaskiya mai yawa! An biya miki bukatarki.” ’Yarta kuwa ta warke nan take.

Yesu ya ciyar da dubu huɗu

29Yesu ya tashi daga nan ya bi ta gefen Tekun Galili. Sa’an nan ya haura gefen wani dutse ya zauna. 30Taron mutane mai girma kuwa suka zo wurinsa, suna kawo masa guragu, makafi, shanyayyu, kurame da dai waɗansu da yawa, suka kuwa kwantar da su a gabansa; ya kuma warkar da su. 31Mutanen kuwa suka yi mamaki sa’ad da suka ga kurame suna magana, shanyayyu suna samun lafiya, guragu suna takawa, makafi kuma suna ganin gari. Sai suka yabi Allah na Isra’ila.

(Markus 8.1-10)

32Yesu ya kira almajiransa wurinsa ya ce, “Ina jin tausayin mutanen nan; gama kwana uku ke nan suke tare da ni ba abin da za su ci. Ba na so in sallame su da yunwa, don kada su kāsa a hanya.”

33Sai almajiransa suka amsa suka ce, “Ina za mu sami isashen burodi a wannan wurin da babu kowa mu ciyar da irin taron nan?”

34Yesu ya tambaye su, “Burodi guda nawa kuke da shi?”

Suka amsa suka ce, “Guda bakwai da ’yan ƙananan kifaye.”

35Ya sa taron su zazzauna a ƙasa. 36Sa’an nan ya ɗauki burodi guda bakwai da kuma kifayen nan, da ya yi godiya, sai ya kakkarya su ya ba wa almajiran, su kuma suka ba wa mutane. 37Duk kuwa suka ci, suka ƙoshi. Daga baya almajiran suka kwashe ragowar gutsattsarin cike da kwanduna bakwai. 38Yawan waɗanda suka ci kuwa, maza dubu huɗu ne, ban da mata da yara. 39Bayan Yesu ya sallami taron, sai ya shiga jirgin ruwa ya tafi wajajen Magadan.

Habrit Hakhadasha/Haderekh

הבשורה על-פי מתי 15:1-39

1יום אחד הגיעו מירושלים מספר פרושים וסופרים כדי לחקור את ישוע.

2”מדוע תלמידיך אינם מקיימים את המסורת היהודית העתיקה?“ דרשו לדעת. ”מדוע תלמידיך אינם נוטלים את ידיהם לפני האוכל?“

3השיב להם ישוע: ”ומדוע עוברת המסורת שלכם על מצוותיו של אלוהים? 4למשל, כתוב בתורה:15‏.4 טו 4 שמות כ 12, כא 17 ’כבד את אביך ואת אמך… ומקלל אביו ואמו מות יומת!‘ 5‏-6אולם אתם אומרים שמותר לאדם להתעלם מצרכי הוריו העניים, אם ייתן ’לעבודת האלוהים‘ את מה שיכול היה לתת להם. וכך אתם מפרים את מצוותו של אלוהים, כדי לקיים מסורת וחוקים שהומצאו על־ידי בני־אדם. 7צבועים שכמוכם! הנביא ישעיהו תיאר אתכם נכונה כשאמר:15‏.7 טו 7 ישעיהו כט 13

8’ניגש העם הזה בפיו,

ובשפתיו כבדוני ולבו רחק ממני;

9ותהי יראתם אותי מצות אנשים מלומדה‘. “

10ישוע אסף סביבו את הקהל ואמר: ”הקשיבו לדבריי והשתדלו להבינם: 11מה שמטמא את האדם זה לא מה שנכנס לפה אלא מה שיוצא מהפה – זה מטמא את האדם!“

12תלמידיו באו אליו ואמרו: ”בדבריך אלה העלבת את הפרושים!“

13ישוע השיב להם: ”כל צמח שלא נשתל על־ידי אבי – ייעקר. 14התעלמו מהם; הפרושים אינם אלא מורי־דרך עיוורים המדריכים עיוורים אחרים, ובסופו של דבר יפלו כולם יחד לתוך בור!“

15שמעון פטרוס ביקש מישוע שיסביר למה התכוון באמרו שאנשים מטמאים את עצמם ממה שיוצא מן הפה.

16”האם אינך מבין?“ שאל אותו ישוע. 17”האם אינך רואה שכל מה שאתה אוכל עובר דרך מערכת העיכול ויוצא שוב החוצה? 18אולם מילים רעות יוצאות מתוך לב רע ומטמאות את האומר אותן. 19כי מתוך הלב יוצאות מחשבות רעות, מעשי רצח, ניאוף, זנות, גניבה, שקר ורכילות. 20דברים אלה הם המטמאים את האדם. אכילה ללא נטילת ידיים אינה מטמאת את האדם.“

21ישוע עזב את האזור ההוא והלך אל אזור צור וצידון.

22אישה כנענית שגרה שם באה אל ישוע והתחננה: ”אדוני, בן־דוד, רחם עלי! שד אחז בבתי והוא מענה אותה ללא הרף.“ 23אולם ישוע לא ענה לה – אף לא מילה אחת. תלמידיו ביקשו ממנו לגרש אותה: ”אמור לה ללכת מכאן, כי היא מציקה לנו כל היום בתחינותיה.“

24”נשלחתי אל צאן האובדות של בית ישראל בלבד“, אמר ישוע לאישה. 25אולם האישה נפלה לרגליו ושוב ביקשה: ”אדוני, עזור לי!“

26”אין זה צודק לקחת את לחמם של הילדים ולהשליכו לכלבים“, ענה לה ישוע.

27”נכון, אדוני,“ השיבה האישה, ”אבל גם לגורי הכלבים מותר לאכול את הפירורים שנופלים מעל שולחן אדוניהם.“

28”אישה,“ אמר לה ישוע, ”יש בך אמונה רבה, ולכן תתמלא בקשתך.“ באותו רגע בתה נרפאה.

29ישוע חזר לכינרת, עלה על גבעה והתיישב שם. 30ההמונים הביאו אליו פיסחים, עיוורים, בעלי־מום, אילמים וחולים אחרים, הניחו אותם לפניו, והוא ריפא את כולם. 31כאשר העם ראה את האילמים מפטפטים בהתרגשות, קטועי האיברים מקבלים איברים חדשים, נכים קופצים ורוקדים והעיוורים מביטים סביבם, נדהמו ושבחו את אלוהי ישראל.

32לאחר מכן קרא ישוע לתלמידיו ואמר: ”אני מרחם על אנשים אלה; הם נמצאים אתי כאן שלושה ימים, ולא נשאר להם מה לאכול. אינני רוצה לשלוח אותם רעבים, כי הם עלולים להתעלף בדרך.“

33”מאין נשיג במדבר הזה מספיק אוכל לכל ההמון?“ שאלו התלמידים.

34”כמה ככרות לחם יש לכם?“ שאל אותם ישוע. ”שבע,“ ענו, ”וכמה דגים קטנים.“

35ישוע ציווה על העם לשבת על הארץ, 36לקח את שבע ככרות הלחם ואת הדגים, הודה לאלוהים עליהם, חילק אותם למנות ונתן לתלמידים, כדי שיגישו ליושבים. 37‏-38אכלו לשובע (כארבעת־אלפים איש לא כולל נשים וילדים), כאשר אספו את השאריות הם מילאו שבעה סלים!

39לאחר מכן שלח ישוע את האנשים לביתם, והוא עצמו עלה לסירה ושט למגדל.