Mattiyu 15 – HCB & BDS

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 15:1-39

Mai tsabta da marar tsabta

(Markus 7.1-13)

1Sa’an nan waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki suka zo wurin Yesu daga Urushalima suka yi tambaya suka ce, 2“Me ya sa almajiranka suke karya al’adun dattawa? Ba sa wanke hannuwansu kafin su ci abinci!”

3Yesu ya amsa ya ce, “Ku ma me ya sa kuke karya dokar Allah saboda al’adarku? 4Gama Allah ya ce, ‘Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka,15.4 Fit 20.12; M Sh 5.16 kuma duk wanda ya zagi mahaifinsa ko mahaifiyarsa dole a kashe shi.’15.4 Fit 21.17; Fir 20.9 5Amma ku kukan ce, in wani ya ce wa mahaifinsa ko mahaifiyarsa, ‘Duk taimakon da dā ya kamata za ku samu daga gare ni an ba wa Allah,’ 6ba zai ‘girmama mahaifinsa’ da shi ba. Ta haka kun yi banza da maganar Allah saboda al’adarku. 7Ku munafukai! Daidai ne Ishaya ya yi annabci a kanku da ya ce,

8“ ‘Waɗannan mutane da baki kawai suke girmama ni,

amma zukatansu suna nesa da ni.

9A banza suke mini sujada,

koyarwarsu, dokoki ne kawai da mutane suke koyarwa.’ ”15.9 Ish 29.13

(Markus 7.14-23)

10Sai Yesu ya kira taron wurinsa ya ce, “Ku saurara ku kuma gane. 11Abin da yake shiga bakin mutum ba ya ƙazantar da shi, sai dai abin da yake fitowa daga bakinsa, shi ne yake ƙazantar da shi.”

12Sai almajiran suka zo wurinsa suka ce, “Ka san cewa Farisiyawa ba su ji daɗi sa’ad da suka ji wannan ba?”

13Ya amsa ya ce, “Duk tsiron da Ubana na sama bai shuka ba, za a tumɓuke shi daga saiwoyi. 14Ku ƙyale su, ai, makafin jagorai ne.15.14 Waɗansu rubuce-rubucen hannu na dā suna da jagorai ne na makafi In makaho ya yi wa makaho jagora, dukansu za su fāɗa a rami.”

15Bitrus ya ce, “Ka bayyana mana wannan misali.”

16Yesu ya tambaye su ya ce, “Har yanzu ba ku gane ba ne? 17Ba ku gane cewa duk abin da ya shiga baki yakan wuce ciki ne daga nan kuma yă fita daga jiki ba? 18Amma abubuwan da suke fitowa ta baki suna fitowa ne daga zuciya, su ne kuma suke ƙazantar da mutum. 19Gama daga zuciya ne mugayen tunani, kisankai, zina, fasikanci, sata, shaidar ƙarya, ɓatan suna, suka fitowa. 20Waɗannan su ne suke ƙazantar da mutum; amma cin abinci ba tare da wanke hannuwa ba, ba ya ƙazantar da mutum.”

Bangaskiyar mutuniyar Kan’ana

(Markus 7.24-30)

21Barin wurin ke nan, sai Yesu ya janye zuwa yankin Taya da Sidon. 22Wata mutuniyar Kan’ana daga wajajen ta zo wurinsa, tana ihu tana cewa, “Ubangiji, Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai! ’Yata tana shan wahala ƙwarai daga aljanin da yake cikinta.”

23Yesu bai ce mata uffam ba. Saboda haka almajiransa suka zo wurinsa suka roƙe shi suka ce, “Ka kore ta tă tafi, tana ta binmu tana damunmu da ihu.”

24Ya amsa ya ce, “An aiko ni wurin ɓatattun tumakin Isra’ila ne kaɗai.”

25Sai macen ta zo ta durƙusa a gabansa ta ce, “Ubangiji, ka taimake ni!”

26Ya amsa ya ce, “Ba daidai ba ne a ɗauki abincin yara a jefa wa karnukansu.”

27Ta amsa, ta ce, “I, Ubangiji, amma karnuka ma sukan ci gutsattsarin da sukan fāɗi daga teburin maigidansu.”

28Sa’an nan Yesu ya amsa ya ce, “Mace, kina da bangaskiya mai yawa! An biya miki bukatarki.” ’Yarta kuwa ta warke nan take.

Yesu ya ciyar da dubu huɗu

29Yesu ya tashi daga nan ya bi ta gefen Tekun Galili. Sa’an nan ya haura gefen wani dutse ya zauna. 30Taron mutane mai girma kuwa suka zo wurinsa, suna kawo masa guragu, makafi, shanyayyu, kurame da dai waɗansu da yawa, suka kuwa kwantar da su a gabansa; ya kuma warkar da su. 31Mutanen kuwa suka yi mamaki sa’ad da suka ga kurame suna magana, shanyayyu suna samun lafiya, guragu suna takawa, makafi kuma suna ganin gari. Sai suka yabi Allah na Isra’ila.

(Markus 8.1-10)

32Yesu ya kira almajiransa wurinsa ya ce, “Ina jin tausayin mutanen nan; gama kwana uku ke nan suke tare da ni ba abin da za su ci. Ba na so in sallame su da yunwa, don kada su kāsa a hanya.”

33Sai almajiransa suka amsa suka ce, “Ina za mu sami isashen burodi a wannan wurin da babu kowa mu ciyar da irin taron nan?”

34Yesu ya tambaye su, “Burodi guda nawa kuke da shi?”

Suka amsa suka ce, “Guda bakwai da ’yan ƙananan kifaye.”

35Ya sa taron su zazzauna a ƙasa. 36Sa’an nan ya ɗauki burodi guda bakwai da kuma kifayen nan, da ya yi godiya, sai ya kakkarya su ya ba wa almajiran, su kuma suka ba wa mutane. 37Duk kuwa suka ci, suka ƙoshi. Daga baya almajiran suka kwashe ragowar gutsattsarin cike da kwanduna bakwai. 38Yawan waɗanda suka ci kuwa, maza dubu huɗu ne, ban da mata da yara. 39Bayan Yesu ya sallami taron, sai ya shiga jirgin ruwa ya tafi wajajen Magadan.

La Bible du Semeur

Matthieu 15:1-39

Jésus et la tradition religieuse juive

(Mc 7.1-23)

1A cette époque, des pharisiens et des spécialistes de la Loi vinrent de Jérusalem ; ils abordèrent Jésus pour lui demander : 2Pourquoi tes disciples ne respectent-ils pas la tradition des ancêtres ? Car ils ne se lavent pas les mains selon le rite usuel avant chaque repas.

3– Et vous, répliqua-t-il, pourquoi désobéissez-vous au commandement de Dieu pour suivre votre tradition ? 4En effet, Dieu a dit : Honore ton père et ta mère15.4 Ex 20.12 ; Dt 5.16. et Que celui qui maudit son père ou sa mère soit puni de mort15.4 Ex 21.17.. 5Mais vous, qu’enseignez-vous ? Qu’il suffit de dire à son père ou à sa mère : « Je fais offrande à Dieu d’une part de mes biens avec laquelle j’aurais pu t’assister », 6pour ne plus rien devoir à son père ou à sa mère. Ainsi vous annulez la Parole de Dieu par votre tradition. 7Hypocrites ! Esaïe a fort bien prophétisé à votre sujet :

8Ce peuple m’honore des lèvres,

mais, au fond de son cœur, il est bien loin de moi !

9Le culte qu’il me rend n’a aucune valeur,

car les enseignements qu’il donne

ne sont que des règles inventées par les hommes15.9 Es 29.13 cité selon l’ancienne version grecque..

10Alors Jésus appela la foule et lui dit : Ecoutez-moi et comprenez-moi bien : 11Ce qui rend un homme impur, ce n’est pas ce qui entre dans sa bouche, mais c’est ce qui en sort.

12Alors les disciples s’approchèrent de lui pour lui dire : Sais-tu que les pharisiens ont été très choqués par tes paroles ?

13Il leur répondit : Toute plante que mon Père céleste n’a pas lui-même plantée sera arrachée. 14Laissez-les : ce sont des aveugles qui conduisent d’autres aveugles ! Or, si un aveugle en conduit un autre, ils tomberont tous deux dans le fossé.

15Pierre intervint en disant : Explique-nous cette parabole.

16– Eh quoi ! répondit Jésus, vous ne comprenez toujours pas, vous aussi ? 17Ne saisissez-vous pas que tout ce qui entre par la bouche va dans le ventre, puis est évacué par voie naturelle ? 18Mais ce qui sort de la bouche vient du cœur, et c’est cela qui rend l’homme impur. 19Car, c’est du cœur que proviennent les mauvaises pensées, les meurtres, les adultères, l’immoralité, le vol, les faux témoignages, les blasphèmes15.19 Autre traduction : injures. . 20Voilà ce qui rend l’homme impur. Mais manger sans s’être lavé les mains ne rend pas l’homme impur.

La foi d’une non-Juive

(Mc 7.24-30)

21En quittant cet endroit, Jésus se rendit dans la région de Tyr et de Sidon.

22Et voilà qu’une femme cananéenne15.22 Cette femme, appelée cananéenne, faisait partie de la population non juive qui vivait dans cette partie de la Phénicie., qui habitait là, vint vers lui et se mit à crier : Seigneur, Fils de David, aie pitié de moi ! Ma fille est sous l’emprise d’un démon qui la tourmente cruellement.

23Mais Jésus ne lui répondit pas un mot.

Ses disciples s’approchèrent de lui et lui dirent : Renvoie-la15.23 Autre traduction : délivre-la, c’est-à-dire donne-lui ce qu’elle demande., car elle ne cesse de nous suivre en criant.

24Ce à quoi il répondit : Je n’ai été envoyé qu’aux brebis perdues du peuple d’Israël.

25Mais la femme vint se prosterner devant lui en disant : Seigneur, viens à mon secours !

26Il lui répondit : Il n’est pas bien de prendre le pain des enfants pour le jeter aux petits chiens.

27– C’est vrai, Seigneur, reprit-elle, et pourtant les petits chiens mangent les miettes qui tombent de la table de leurs maîtres.

28Alors Jésus dit : O femme, ta foi est grande ! Qu’il en soit donc comme tu le veux !

Et, sur l’heure, sa fille fut guérie.

Nombreuses guérisons

(Mc 7.31)

29Jésus partit de cette région et retourna au bord du lac de Galilée. Il monta sur une colline où il s’assit. 30Des foules nombreuses vinrent auprès de lui et, avec elles, des paralysés, des aveugles, des sourds-muets, des estropiés et beaucoup d’autres malades. On les amena aux pieds de Jésus, et il les guérit. 31La foule s’émerveillait de voir les sourds-muets parler, les estropiés reprendre l’usage de leurs membres, les paralysés marcher, les aveugles recouvrer la vue, et tous se mirent à chanter la gloire du Dieu d’Israël.

Avec sept pains et des poissons

(Mc 8.1-10)

32Jésus appela ses disciples et leur dit : J’ai pitié de cette foule. Voilà déjà trois jours qu’ils sont restés là, avec moi, et ils n’ont rien à manger. Je ne veux pas les renvoyer à jeun, de peur que les forces leur manquent sur le chemin du retour.

33Ses disciples lui dirent : Où pourrions-nous trouver, dans ce lieu désert, assez de pains pour nourrir une telle foule ?

34– Combien de pains avez-vous ?

– Sept, répondirent-ils, et quelques petits poissons.

35Alors il invita tout le monde à s’asseoir par terre. 36Il prit ensuite les sept pains et les poissons et, après avoir remercié Dieu, il les partagea et les donna aux disciples, qui les distribuèrent à la foule. 37Tous mangèrent à satiété. On ramassa sept corbeilles pleines des morceaux qui restaient. 38Ceux qui furent ainsi nourris étaient au nombre de quatre mille hommes, sans compter les femmes et les enfants.

39Après avoir congédié la foule, Jésus monta dans un bateau et se rendit dans la région de Magadan.