Mattiyu 14 – HCB & CARST

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 14:1-36

An yanke kan Yohanna Mai Baftisma

(Markus 6.14-29; Luka 9.7-9)

1A lokacin nan sarki Hiridus ya ji labarin Yesu, 2sai ya ce wa fadawansa, “Wannan Yohanna Mai Baftisma ne; ya tashi daga matattu! Shi ya sa abubuwan banmamakin nan suke faruwa ta wurinsa.”

3To, dā Hiridus ya kama Yohanna ya daure, ya kuma sa shi cikin kurkuku saboda Hiridiyas, matar ɗan’uwansa Filibus, 4gama Yohanna ya dinga ce masa, “Ba daidai ba ne ka aure ta.” 5Hiridus ya so yă kashe Yohanna, amma yana jin tsoron mutane, don sun ɗauka shi annabi ne.

6A bikin tuna da ranar haihuwar Hiridus, diyar Hiridiyas ta yi musu rawa ta kuma gamsar da Hiridus ƙwarai, 7har ya yi alkawari da rantsuwa cewa zai ba ta duk abin da ta roƙa. 8Da mahaifiyarta ta zuga ta, sai ta ce, “Ba ni a cikin kwanon nan, kan Yohanna Mai Baftisma.” 9Sarki ya yi baƙin ciki, amma saboda rantsuwarsa da kuma baƙinsa, sai ya ba da umarni a ba ta abin da ta roƙa 10ya kuma sa aka yanke kan Yohanna a kurkuku. 11Aka kawo kansa cikin kwano aka ba yarinyar, ita kuma ta kai wa mahaifiyarta. 12Almajiran Yohanna suka zo suka ɗauki gawarsa suka binne. Sa’an nan suka je suka gaya wa Yesu.

Yesu ya ciyar da dubu biyar

(Markus 6.30-44; Luka 9.10-17; Yohanna 6.1-14)

13Sa’ad da Yesu ya ji abin da ya faru, sai ya shiga jirgin ruwa ya janye shi kaɗai zuwa wani wuri inda ba kowa. Da jin haka, taron mutane suka bi shi da ƙafa daga garuruwa. 14Da Yesu ya sauka ya kuma ga taro mai yawa, sai ya ji tausayinsu ya kuma warkar da marasa lafiyarsu.

15Da yamma ta yi, sai almajiransa suka zo wurinsa suka ce, “Wurin nan fa ba kowa, ga shi kuma rana ta kusa fāɗuwa. Ka sallami taron don su shiga ƙauyuka su nemi wa kansu abinci.”

16Yesu ya amsa, “Ba su bukata su tafi. Ku ku ba su wani abu su ci.”

17Suka ce, “Burodi biyar da kifi biyu ne kawai muke da su a nan.”

18Ya ce, “Ku kawo mini su a nan.” 19Sai ya umarci mutanen su zazzauna a kan ciyawa. Da ya ɗauki burodi biyar da kifin biyun nan ya dubi sama, ya yi godiya ya kuma kakkarya burodin. Sa’an nan ya ba wa almajiransa, almajiran kuwa suka ba wa mutane. 20Duk suka ci suka ƙoshi, almajiran kuwa suka kwashe ragowar gutsattsarin cike da kwanduna goma sha biyu. 21Yawan waɗanda suka ci, sun yi wajen maza dubu biyar, ban da mata da yara.

Yesu ya yi tafiya a kan ruwa

(Markus 6.45-52; Yohanna 6.15-21)

22Nan da nan Yesu ya sa almajiran su shiga jirgin ruwa su sha gabansa, su haye zuwa ɗayan hayin, yayinda shi kuma yă sallami taron. 23Bayan ya sallame su, sai ya haura bisan gefen dutse shi kaɗai don yă yi addu’a. Da yamma ta yi, yana can shi kaɗai, 24jirgin ruwan kuwa ya riga ya yi nesa da gaci, yana fama da raƙuman ruwa domin iska tana gāba da shi.

25Wajen tsaro na huɗu na dare, sai Yesu ya nufe su, yana takawa a kan tafkin. 26Sa’ad da almajiran suka gan shi yana takawa a kan tafkin, sai tsoro ya kama su. Suka yi ihu don tsoro suka ce, “Fatalwa ce.”

27Amma nan da nan Yesu ya ce musu, “Ku yi ƙarfin hali! Ni ne. Kada ku ji tsoro.”

28Sai Bitrus ya amsa ya ce, “Ubangiji in kai ne ka ce mini in zo wurinka a kan ruwan.”

29Ya ce, “Zo.”

Sai Bitrus ya fita daga jirgin ruwan, ya taka a kan ruwan ya nufe wajen Yesu. 30Amma da ya ga haukar iskar, sai ya ji tsoro, ya kuma fara nutsewa, sai ya yi ihu ya ce, “Ubangiji, ka cece ni!”

31Nan da nan Yesu ya miƙa hannu ya kamo shi ya ce, “Kai mai ƙarancin bangaskiya, don me ka yi shakka?”

32Da suka hau jirgin ruwan, sai iskar ta kwanta. 33Waɗanda suke cikin jirgin ruwan kuwa suka yi masa sujada, suna cewa, “Gaskiya kai Ɗan Allah ne.”

(Markus 6.45-52; Yohanna 6.15-21)

34Sa’ad da suka haye, sai suka sauka a Gennesaret. 35Da mutanen wurin suka gane da Yesu, sai suka kai labari a ko’ina a ƙauyukan da suke kewaye. Mutane suka kawo masa dukan marasa lafiyarsu 36suka kuwa roƙe shi yă bar marasa lafiya su taɓa ko da gefen rigarsa kawai, duk waɗanda suka taɓa shi kuwa suka warke.

Священное Писание (Восточный перевод), версия для Таджикистана

Матто 14:1-36

Царь Ирод убивает пророка Яхьё

(Мк. 6:14-29; Лк. 9:7-9)

1В то время об Исо услышал и правитель Ирод14:1 Это Ирод Антипа, сын Ирода Великого от сомарянки Малфаки. Он правил Галилеей и Переей с 4 г. до н. э. по 39 г. н. э.. 2Он говорил своим приближённым:

– Это пророк Яхьё. Он воскрес из мёртвых, и поэтому в Нём такая чудодейственная сила.

3В своё время Ирод арестовал Яхьё, связал его и бросил в темницу из-за Иродиады, жены своего брата Филиппа14:3 Это Ирод Филипп I, сын Ирода Великого от Мариамны., 4потому что Яхьё говорил ему: «Нельзя тебе жить с ней»14:4 Женитьба Ирода на жене брата была нарушением Закона Всевышнего (см. Лев. 18:16; 20:21).. 5Ирод хотел убить Яхьё, но боялся народа, так как все считали его пророком. 6И вот когда Ирод праздновал свой день рождения, дочь Иродиады танцевала перед гостями и так понравилась Ироду, 7что он поклялся дать ей всё, чего бы она ни попросила. 8Наученная своей матерью девушка сказала:

– Подай мне сюда на блюде голову пророка Яхьё.

9Царь опечалился, но так как он поклялся перед возлежавшими за столом гостями, то велел исполнить её желание. 10По его приказу Яхьё отрубили в темнице голову, 11принесли её на блюде и отдали девушке, а та отнесла её матери. 12Ученики Яхьё, забрав тело, похоронили его, а затем пошли и рассказали обо всём Исо.

Насыщение более пяти тысяч человек

(Мк. 6:32-44; Лк. 9:10-17; Ин. 6:1-13)

13Услышав о судьбе Яхьё, Исо переправился на лодке в пустынное место, чтобы побыть одному. Но люди из окрестных городов узнали, куда Он отправился, и пошли туда пешком. 14Когда Исо сошёл на берег и увидел большую толпу, Он сжалился над людьми и исцелил больных, которые были среди них. 15Наступил вечер. Ученики Исо подошли к Нему и сказали:

– Место здесь пустынное, и уже поздно, отпусти людей, чтобы они успели дойти до ближайших посёлков и купить себе еды.

16Исо ответил:

– Им не нужно уходить отсюда. Вы дайте им есть.

17– Но у нас только пять лепёшек и две рыбы, – ответили ученики.

18– Принесите всё это ко Мне, – сказал Исо.

19Он велел народу расположиться на траве, взял эти пять лепёшек и две рыбы и, подняв глаза к небу, благословил пищу. Затем Он стал разламывать лепёшки и давать их Своим ученикам, а те – народу. 20Все ели и насытились, а когда собрали оставшиеся куски, то их набралось двенадцать полных корзин. 21Всего же ело пять тысяч мужчин, не считая женщин и детей.

Хождение Исо Масеха по воде

(Мк. 6:45-51; Ин. 6:16-21)

22Сразу после этого Исо велел ученикам сесть в лодку и переправиться на другую сторону озера, а Сам Он оставался, пока не отпустил народ. 23А когда народ разошёлся, Исо поднялся на гору помолиться. Наступил вечер, и Исо оставался на горе один. 24Тем временем лодка была уже далеко от берега. Её били волны, так как дул встречный ветер. 25Уже перед рассветом Исо пошёл к ученикам, ступая по озеру. 26Но ученики, увидев Его идущим по воде, очень испугались.

– Это призрак! – закричали они от страха.

27Но Исо сразу же заговорил с ними:

– Успокойтесь, это Я, не бойтесь.

28– Повелитель, если это Ты, – сказал тогда Петрус, – то разреши мне прийти к Тебе по воде.

29– Иди, – сказал Исо.

Петрус вышел из лодки и пошёл по воде к Исо. 30Но увидев, как сильно дует ветер, он испугался и, начав тонуть, закричал:

– Повелитель, спаси меня!

31Исо тотчас протянул руку и поддержал его.

– Маловерный, – сказал Он, – зачем же ты стал сомневаться?

32Когда они вошли в лодку, ветер утих. 33Все, кто был в лодке, поклонились Исо.

– Ты действительно (вечный) Сын Всевышнего, – сказали они.

Исцеление больных в Генисарете

(Мк. 6:53-56)

34Переправившись на другую сторону озера, они сошли на берег в Генисарете. 35Местные жители узнали Исо и разнесли весть о Его приходе по всей округе. К Исо принесли всех больных 36и просили Его, чтобы Он позволил им прикоснуться лишь к кисточке на краю Его одежды14:36 См. сноску на 9:20.. И все, кто прикасался, выздоравливали.