Mattiyu 11 – HCB & NVI-PT

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 11:1-30

Yesu da Yohanna Mai Baftisma

(Luka 7.18-35)

1Bayan Yesu ya gama yi wa almajiransa sha biyun nan umarni, sai ya yi gaba daga can don yă koyar yă kuma yi wa’azi a garuruwan Galili.11.1 Da Girik a cikin garuruwansu

2Sa’ad da Yohanna Mai Baftisma ya ji a kurkuku abin da Kiristi yake yi, sai ya aiki almajiransa 3su tambaye shi, “Kai ne wanda zai zo, ko kuwa mu sa ido ga wani?”

4Yesu ya amsa ya ce, “Ku koma ku gaya wa Yohanna abin da kuka ji, kuka kuma gani. 5Makafi suna gani, guragu suna tafiya, ana warkar da waɗanda suke da kuturta, kurame suna ji, ana tā da matattu, ana kuma yi wa matalauta wa’azin labari mai daɗi. 6Mai albarka ne mutumin da bai yi tuntuɓe ba saboda ni.”

7Sa’ad da almajiran Yohanna suke barin wurin, sai Yesu ya fara yi wa taron magana game da Yohanna. “Me kuka je kallo a hamada? Ciyawar da iska take kaɗawa ne? 8In ba haka ba, to, me kuka je kallo? Mutum mai sanye da riguna masu kyau ne? A’a, masu sa riguna masu kyau, ai, a fadan sarakuna suke. 9To, me kuka je kallo ne? Annabi? I, ina gaya muku, ya ma fi annabi. 10Wannan shi ne wanda aka rubuta game da shi cewa,

“ ‘Zan aiki ɗan saƙona yă sha gabanka,

wanda zai shirya hanyarka a gabanka.’11.10 Mal 3.1

11Gaskiya nake gaya muku. A cikin dukan waɗanda mata suka haifa, ba wani da ya taso da ya fi Yohanna Mai Baftisma girma; duk da haka mafi ƙanƙanta a mulkin sama ya fi shi girma. 12Tun daga kwanakin Yohanna Mai Baftisma har yă zuwa yanzu, mulkin sama yana sha da ƙyar, fitanannu kuma sun kama mulkin sama sun riƙe gam. 13Gama dukan Annabawa da kuma Doka sun yi ta annabci har yă zuwa kan Yohanna. 14In kuna niyya ku yarda da wannan, to, shi ne Iliya da dā ma zai zo. 15Duk mai kunnen ji, yă ji.

16“Da me zan kwatanta wannan zamani? Suna kama da yara da suke zaune a kasuwa, suna kiran juna, suna cewa,

17“ ‘Mun yi muku busa,

ba ku kuwa yi rawa ba,

mun rera waƙar makoki,

ba ku kuwa yi makoki ba.’

18Gama Yohanna Mai Baftisma ya zo ba ya ciye-ciye, ba ya shaye-shaye, sai suka ce, ‘Ai, yana da aljani.’ 19Ɗan Mutum ya zo yana ciye-ciye, yana shaye-shaye, sai suka ce, ‘Ga mai haɗama da kuma mashayi, abokin masu karɓar haraji da masu zunubi.’ Amma akan tabbatar da hikima ta wurin ayyukanta.”

Kaiton biranen da ba su tuba ba

(Luka 7.18-35)

20Sai Yesu ya fara yin tir da biranen da aka yi yawancin ayyukansa na banmamaki, don ba su tuba ba. 21“Kaitonki, Korazin! Kaitonki, Betsaida! Da a ce ayyukan banmamakin da aka yi a cikinki ne aka yi a Taya da Sidon, da tuni sun tuba sanye da rigar makoki da toka. 22Amma ina gaya muku, za a fi jin tausayin Taya da Sidon a ranar shari’a, fiye da ku. 23Ke kuma Kafarnahum, za a ɗaga ki sama ne? A’a, za ki gangara zuwa zurfafa ne. Da a ce ayyukan banmamakin da aka yi a cikinki ne a aka yi a Sodom, da tana nan har yă zuwa yau. 24Amma ina gaya miki, za a fi jin tausayin Sodom fiye da ke a ranar shari’a.”

Hutu domin waɗanda suka gaji

(Luka 10.13-15)

25A wannan lokaci sai Yesu ya ce, “Ina yabonka, Uba, Ubangijin sama da ƙasa, gama ka ɓoye waɗannan abubuwa ga masu hikima da masu ilimi, ka kuma bayyana su ga ƙananan yara. 26I, Uba, gama wannan shi ne abin da ka ji daɗin yi.

27“Dukan kome Ubana ya danƙa mini. Ba wanda ya san Ɗan sai dai Uban, ba kuma wanda ya san Uban, sai dai Ɗan da kuma waɗanda Ɗan ya so yă bayyana musu shi.

28“Ku zo gare ni, dukanku da kuka gaji kuke kuma fama da kaya, zan kuwa ba ku hutu. 29Ku ɗauki karkiyata a kanku, ku kuma yi koyi da ni, gama ni mai tawali’u ne marar girman kai, za ku kuwa sami hutu don rayukanku. 30Gama karkiyata mai sauƙi ce, kayana kuma marasa nauyi ne.”

Nova Versão Internacional

Mateus 11:1-30

Jesus e João Batista

(Lc 7.18-35)

1Quando acabou de instruir seus doze discípulos, Jesus saiu para ensinar e pregar nas cidades da Galileia11.1 Grego: cidades deles..

2João, ao ouvir na prisão o que Cristo estava fazendo, enviou seus discípulos para lhe perguntarem: 3“És tu aquele que haveria de vir ou devemos esperar algum outro?”

4Jesus respondeu: “Voltem e anunciem a João o que vocês estão ouvindo e vendo: 5os cegos veem, os aleijados andam, os leprosos11.5 O termo grego não se refere somente à lepra, mas também a diversas doenças da pele. são purificados, os surdos ouvem, os mortos são ressuscitados, e as boas-novas são pregadas aos pobres; 6e feliz é aquele que não se escandaliza por minha causa”.

7Enquanto saíam os discípulos de João, Jesus começou a falar à multidão a respeito de João: “O que vocês foram ver no deserto? Um caniço agitado pelo vento? 8Ou, o que foram ver? Um homem vestido de roupas finas? Ora, os que usam roupas finas estão nos palácios reais. 9Afinal, o que foram ver? Um profeta? Sim, eu digo a vocês, e mais que profeta. 10Este é aquele a respeito de quem está escrito:

“ ‘Enviarei o meu mensageiro à tua frente;

ele preparará o teu caminho diante de ti’11.10 Ml 3.1.

11Digo a verdade a vocês: Do meio dos nascidos de mulher não surgiu ninguém maior do que João Batista; todavia, o menor no Reino dos céus é maior do que ele. 12Desde os dias de João Batista até agora, o Reino dos céus é tomado à força, e os que usam de força se apoderam dele. 13Pois todos os Profetas e a Lei profetizaram até João. 14E se vocês quiserem aceitar, este é o Elias que havia de vir. 15Aquele que tem ouvidos, ouça!

16“A que posso comparar esta geração? São como crianças que ficam sentadas nas praças e gritam umas às outras:

17“ ‘Nós tocamos flauta,

mas vocês não dançaram;

cantamos um lamento,

mas vocês não se entristeceram’.

18Pois veio João, que jejua e não bebe vinho11.18 Grego: não comendo, nem bebendo., e dizem: ‘Ele tem demônio’. 19Veio o Filho do homem comendo e bebendo, e dizem: ‘Aí está um comilão e beberrão, amigo de publicanos e pecadores’. Mas a sabedoria é comprovada pelas obras que a acompanham”.

Ai das Cidades que Não se Arrependem

(Lc 10.13-15)

20Então Jesus começou a denunciar as cidades em que havia sido realizada a maioria dos seus milagres, porque não se arrependeram. 21“Ai de você, Corazim! Ai de você, Betsaida! Porque se os milagres que foram realizados entre vocês tivessem sido realizados em Tiro e Sidom, há muito tempo elas se teriam arrependido, vestindo roupas de saco e cobrindo-se de cinzas. 22Mas eu afirmo que no dia do juízo haverá menor rigor para Tiro e Sidom do que para vocês. 23E você, Cafarnaum, será elevada até ao céu? Não, você descerá até o Hades11.23 Essa palavra pode ser traduzida por inferno, sepulcro, morte ou profundezas.! Se os milagres que em você foram realizados tivessem sido realizados em Sodoma, ela teria permanecido até hoje. 24Mas eu afirmo que no dia do juízo haverá menor rigor para Sodoma do que para você”.

Repouso para os Cansados

(Lc 10.21,22)

25Naquela ocasião, Jesus disse: “Eu te louvo, Pai, Senhor dos céus e da terra, porque escondeste estas coisas dos sábios e cultos, e as revelaste aos pequeninos. 26Sim, Pai, pois assim foi do teu agrado.

27“Todas as coisas me foram entregues por meu Pai. Ninguém conhece o Filho a não ser o Pai, e ninguém conhece o Pai a não ser o Filho e aqueles a quem o Filho o quiser revelar.

28“Venham a mim, todos os que estão cansados e sobrecarregados, e eu darei descanso a vocês. 29Tomem sobre vocês o meu jugo e aprendam de mim, pois sou manso e humilde de coração, e vocês encontrarão descanso para as suas almas. 30Pois o meu jugo é suave e o meu fardo é leve”.