Mattiyu 11 – HCB & CCBT

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 11:1-30

Yesu da Yohanna Mai Baftisma

(Luka 7.18-35)

1Bayan Yesu ya gama yi wa almajiransa sha biyun nan umarni, sai ya yi gaba daga can don yă koyar yă kuma yi wa’azi a garuruwan Galili.11.1 Da Girik a cikin garuruwansu

2Sa’ad da Yohanna Mai Baftisma ya ji a kurkuku abin da Kiristi yake yi, sai ya aiki almajiransa 3su tambaye shi, “Kai ne wanda zai zo, ko kuwa mu sa ido ga wani?”

4Yesu ya amsa ya ce, “Ku koma ku gaya wa Yohanna abin da kuka ji, kuka kuma gani. 5Makafi suna gani, guragu suna tafiya, ana warkar da waɗanda suke da kuturta, kurame suna ji, ana tā da matattu, ana kuma yi wa matalauta wa’azin labari mai daɗi. 6Mai albarka ne mutumin da bai yi tuntuɓe ba saboda ni.”

7Sa’ad da almajiran Yohanna suke barin wurin, sai Yesu ya fara yi wa taron magana game da Yohanna. “Me kuka je kallo a hamada? Ciyawar da iska take kaɗawa ne? 8In ba haka ba, to, me kuka je kallo? Mutum mai sanye da riguna masu kyau ne? A’a, masu sa riguna masu kyau, ai, a fadan sarakuna suke. 9To, me kuka je kallo ne? Annabi? I, ina gaya muku, ya ma fi annabi. 10Wannan shi ne wanda aka rubuta game da shi cewa,

“ ‘Zan aiki ɗan saƙona yă sha gabanka,

wanda zai shirya hanyarka a gabanka.’11.10 Mal 3.1

11Gaskiya nake gaya muku. A cikin dukan waɗanda mata suka haifa, ba wani da ya taso da ya fi Yohanna Mai Baftisma girma; duk da haka mafi ƙanƙanta a mulkin sama ya fi shi girma. 12Tun daga kwanakin Yohanna Mai Baftisma har yă zuwa yanzu, mulkin sama yana sha da ƙyar, fitanannu kuma sun kama mulkin sama sun riƙe gam. 13Gama dukan Annabawa da kuma Doka sun yi ta annabci har yă zuwa kan Yohanna. 14In kuna niyya ku yarda da wannan, to, shi ne Iliya da dā ma zai zo. 15Duk mai kunnen ji, yă ji.

16“Da me zan kwatanta wannan zamani? Suna kama da yara da suke zaune a kasuwa, suna kiran juna, suna cewa,

17“ ‘Mun yi muku busa,

ba ku kuwa yi rawa ba,

mun rera waƙar makoki,

ba ku kuwa yi makoki ba.’

18Gama Yohanna Mai Baftisma ya zo ba ya ciye-ciye, ba ya shaye-shaye, sai suka ce, ‘Ai, yana da aljani.’ 19Ɗan Mutum ya zo yana ciye-ciye, yana shaye-shaye, sai suka ce, ‘Ga mai haɗama da kuma mashayi, abokin masu karɓar haraji da masu zunubi.’ Amma akan tabbatar da hikima ta wurin ayyukanta.”

Kaiton biranen da ba su tuba ba

(Luka 7.18-35)

20Sai Yesu ya fara yin tir da biranen da aka yi yawancin ayyukansa na banmamaki, don ba su tuba ba. 21“Kaitonki, Korazin! Kaitonki, Betsaida! Da a ce ayyukan banmamakin da aka yi a cikinki ne aka yi a Taya da Sidon, da tuni sun tuba sanye da rigar makoki da toka. 22Amma ina gaya muku, za a fi jin tausayin Taya da Sidon a ranar shari’a, fiye da ku. 23Ke kuma Kafarnahum, za a ɗaga ki sama ne? A’a, za ki gangara zuwa zurfafa ne. Da a ce ayyukan banmamakin da aka yi a cikinki ne a aka yi a Sodom, da tana nan har yă zuwa yau. 24Amma ina gaya miki, za a fi jin tausayin Sodom fiye da ke a ranar shari’a.”

Hutu domin waɗanda suka gaji

(Luka 10.13-15)

25A wannan lokaci sai Yesu ya ce, “Ina yabonka, Uba, Ubangijin sama da ƙasa, gama ka ɓoye waɗannan abubuwa ga masu hikima da masu ilimi, ka kuma bayyana su ga ƙananan yara. 26I, Uba, gama wannan shi ne abin da ka ji daɗin yi.

27“Dukan kome Ubana ya danƙa mini. Ba wanda ya san Ɗan sai dai Uban, ba kuma wanda ya san Uban, sai dai Ɗan da kuma waɗanda Ɗan ya so yă bayyana musu shi.

28“Ku zo gare ni, dukanku da kuka gaji kuke kuma fama da kaya, zan kuwa ba ku hutu. 29Ku ɗauki karkiyata a kanku, ku kuma yi koyi da ni, gama ni mai tawali’u ne marar girman kai, za ku kuwa sami hutu don rayukanku. 30Gama karkiyata mai sauƙi ce, kayana kuma marasa nauyi ne.”

Chinese Contemporary Bible (Traditional)

馬太福音 11:1-30

耶穌和施洗者約翰

1耶穌囑咐完十二個門徒,就離開那裡,到附近的城鎮傳道和教導人。

2約翰在監獄中聽到基督所做的事,就差兩個門徒去問祂: 3「你就是那位我們所等候的救主嗎?還是我們要等別人呢?」

4耶穌回答說:「你們回去把所見所聞告訴約翰5就是瞎子看見,瘸子走路,痲瘋病人得潔淨,聾子聽見,死人復活,窮人聽到福音。 6凡對我沒有失去信心的人有福了!」

7他們離開後,耶穌對眾人談起約翰,說:「你們從前去曠野要看什麼呢?看隨風搖動的蘆葦嗎? 8如果不是,你們到底想看什麼?是看穿綾羅綢緞的人嗎?那些穿綾羅綢緞的人生活在王宮裡。 9你們究竟想看什麼?看先知嗎?是的,我告訴你們,他不只是先知。 10聖經上說,『看啊,我要差遣我的使者在你前面為你預備道路』,這裡所指的就是約翰11我實在告訴你們,凡婦人所生的,沒有一個興起來比施洗者約翰大,然而天國裡最微不足道的也比他大。

12「從施洗者約翰到現在,天國一直在強勁地擴展著,強勁的人要抓住它。 13因為到約翰為止,所有的先知和律法都在預言天國的事。 14如果你們願意接受,約翰就是那要來的以利亞15有耳可聽的都應該留心聽。

16「這個世代的人好像什麼呢?他們好像一群在街上玩耍的兒童對別的孩子說,

17『我們吹娶親的樂曲,

你們不跳舞;

我們唱送葬的哀歌,

你們不悲傷。』

18約翰來了,也不吃也不喝,他們就說他被鬼附身。 19人子來了,又吃又喝,他們就說祂是貪吃好酒之徒,與稅吏和罪人為友。然而智慧會在她的作為上得到驗證。」

不肯悔改的城

20那時,耶穌開始責備一些城鎮,因為祂在那裡行了許多神蹟,當地的居民仍不肯悔改。 21祂說:「哥拉汛啊,你大禍臨頭了!伯賽大啊,你大禍臨頭了!我在你們當中所行的神蹟,如果行在泰爾西頓,那裡的人早就身披麻衣,頭蒙灰塵,悔改了。 22所以我告訴你們,在審判之日,你們將比泰爾西頓受更重的刑罰!

23迦百農啊,你將被提升到天上嗎?不!你將被打落到陰間。因為若把在你那裡所行的神蹟行在所多瑪,它肯定會存留到今天。 24所以我告訴你們,在審判之日,你們將比所多瑪受更重的刑罰!」

勞苦者得安息

25那時,耶穌說:「父啊,天地的主,我頌讚你,因為你把這些事向聰明、有學問的人隱藏起來,卻啟示給像孩童一般的人。 26父啊,是的,這正是你的美意。 27我父將一切交給了我。除了父,沒有人認識子;除了子和受子啟示的人,沒有人認識父。

28「所有勞苦困乏、背負重擔的人啊,到我這裡來吧!我要賜給你們安息。 29我心柔和謙卑,你們要負我的軛,向我學習,這樣你們的心靈必得享安息。 30因為我的軛容易負,我的擔子很輕省。」