Mattiyu 10 – HCB & SNC

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 10:1-42

Yesu ya aiki sha biyun

(Markus 3.13-19; Luka 6.12-16)

1Sai ya kira almajiransa goma sha biyu wurinsa ya kuma ba su iko su fitar aljanu, su kuma warkar da kowace irin cuta da rashin lafiya.

2Ga sunayen manzannin nan goma sha biyu,

da fari, Siman (wanda ake kira Bitrus) da ɗan’uwansa Andarawus;

Yaƙub ɗan Zebedi da ɗan’uwansa Yohanna;

3Filibus da Bartolomeyu;

Toma da Mattiyu mai karɓar haraji;

Yaƙub ɗan Alfayus da Taddayus;

4Siman Zilot da kuma Yahuda Iskariyot wanda ya bashe Yesu.

(Markus 3.13-19; Luka 6.12-16)

5Waɗannan sha biyun ne Yesu ya aika da umarni cewa, “Kada ku je cikin Al’ummai, ko kuwa ku shiga wani garin Samariyawa. 6A maimakon haka ku je wajen ɓatattun tumakin Isra’ila. 7Sa’ad da kuke tafiya, ku yi wa’azi, kuna cewa, ‘Mulkin sama ya kusato.’ 8Ku warkar da marasa lafiya, ku tā da matattu, ku tsabtacce kutare, ku kuma fitar da aljanu. A kyauta kuka samu, ku kuma bayar a kyauta.

9“Kada ku riƙe wata zinariya ko azurfa ko jan ƙarfe a aljihunanku, 10kada ku ɗauki jaka don tafiya, ko ƙarin riga, ko takalma ko sanda; domin ma’aikaci ya cancanci hakkinsa. 11Kowane gari ko ƙauyen da kuka shiga, ku nemi mai mutunci a wurin, ku kuma zauna a gidansa har sai kun tashi. 12Da shigarku gidan, ku yi gaisuwa. 13In gidan na kirki ne, bari salamarku ta zauna a kansa; in kuwa ba mai kirki ba, salamarku ta komo muku. 14Duk wanda ya ƙi marabtarku ko ya ƙi sauraron kalmominku, sai ku karkaɗe ƙurar ƙafafunku sa’ad da kuka fita gidan ko garin. 15Gaskiya nake gaya muku, za a fi jin tausayin Sodom da Gomorra a ranar shari’a fiye da wannan gari.

(Markus 3.13-19; Luka 6.12-16)

16“Ina aikan ku kamar tumaki a cikin kyarketai. Saboda haka ku zama masu wayo kamar macizai, kuma marasa ɓarna kamar kurciyoyi. 17Ku yi hankali da mutane; za su miƙa ku ga majalisa su kuma yi muku bulala a majami’unsu. 18Saboda ni, za a ja ku zuwa gaban gwamnoni da gaban sarakuna domin ku ba da shaida a gabansu, da kuma ga Al’ummai. 19Amma sa’ad da suka kama ku, kada ku damu game da abin da za ku faɗa ko kuwa yadda za ku faɗe shi. A lokacin za a ba ku abin da za ku faɗa, 20gama ba ku ba ne kuke magana, amma Ruhun Ubanku ne yake magana ta wurinku.

21“Ɗan’uwa zai ci amanar ɗan’uwansa, a kuma kashe shi, Uba ma zai yi haka da ɗansa; ’ya’ya za su tayar wa iyayensu, su kuma sa a kashe su. 22Dukan mutane za su ƙi ku saboda ni, amma wanda ya jure har ƙarshe zai sami ceto. 23Sa’ad da aka tsananta muku a wannan wuri, ku gudu zuwa wancan. Gaskiya nake gaya muku, kafin ku gama zazzaga dukan biranen Isra’ila, Ɗan Mutum zai zo.

24“Ɗalibi ba ya fin malaminsa, haka ma, bawa ba ya fin maigidansa. 25Ya isa wa ɗalibi yă zama kamar malaminsa, haka ma bawa kamar maigidansa. In har an kira wanda yake kan gida Be’elzebub,10.25 Da Girik Be’ezebowul ko kuwa Be’elzebowul me za su ce game da mutanen gidansa?

(Luka 12.2-7)

26“Saboda haka kada ku ji tsoronsu. Ba abin da yake a rufe da ba za a tone ba, ko kuwa a ɓoye da ba za a bayyana ba. 27Abin da na faɗa muku a asirce, ku faɗe shi a sarari; abin da aka faɗa muku a kunne, ku yi shelarsa daga kan rufin ɗaki. 28Kada ku ji tsoron masu kashe jiki amma ba sa iya kashe rai. A maimakon haka, ku ji tsoron Wannan wanda yake da iko yă hallaka rai duk da jiki a jahannama ta wuta. 29Ba akan sayar da kanari biyu kobo ɗaya ba? Duk da haka ba ɗayansu da zai fāɗi ƙasa ba da yardar Ubanku. 30Kai, ko gashin kanku ma duk an ƙidaya su. 31Saboda haka kada ku ji tsoro; kun fi kanari masu yawa, daraja nesa.

(Luka 12.8,9)

32“Duk wanda ya bayyana yarda a gare ni a gaban mutane, ni ma zan bayyana yarda a gare shi a gaban Ubana da yake cikin sama. 33Amma duk wanda ya yi mūsun sani na a gaban mutane, ni ma zan yi mūsun saninsa a gaban Ubana da yake cikin sama.

(Luka 12.51-53; 14.26,27)

34“Kada fa ku ɗauka na zo ne don in kawo salama a duniya. A’a, ban zo don in kawo salama ba, sai dai takobi. 35Gama na zo ne in sa,

“ ‘gāba tsakanin mutum da mahaifinsa,

’ya da mahaifiyarta,

matar ɗa da surukarta,

36abokan gāban mutum, za su zama mutanen gidansa ne.’10.36 Mik 7.6

37“Duk wanda ya fi ƙaunar mahaifinsa ko mahaifiyarsa fiye da ni, bai dace yă zama nawa ba; duk kuwa wanda yake ƙaunar ɗansa ko diyarsa fiye da ni, bai dace yă zama nawa ba; 38duk wanda kuma bai ɗauki gicciyensa ya bi ni ba, bai dace yă zama nawa ba. 39Duk mai son adana ransa zai rasa shi, duk wanda kuwa ya rasa ransa saboda ni zai same shi.

(Markus 9.41)

40“Wanda ya karɓe ku, ya karɓe ni ne, wanda kuma ya karɓe ni, ya karɓi wanda ya aiko ni ne. 41Duk wanda ya karɓi annabi don shi annabi ne, zai sami ladar annabi, duk kuwa wanda ya karɓi mutum mai adalci don shi mai adalci ne, zai sami ladar mai adalci. 42In kuma wani ya ba wa ɗaya daga cikin ƙananan nan ko da kwaf ruwan sanyi ne kan shi almajirina ne, gaskiya nake gaya muku, ba shakka ba zai rasa ladarsa ba.”

Slovo na cestu

Matouš 10:1-42

Ježíš vysílá dvanáct učedníků

1Potom Ježíš svolal svých dvanáct žáků a dal jim moc nad temnými silami, aby je vyháněli a uzdravovali všechny nemoci těla i ducha. 2Jména těch dvanácti, které nazval svými vyslanci – apoštoly, jsou:

Šimon, zvaný Petr,

Ondřej – Petrův bratr,

Jakub – syn Zebedeův

a jeho bratr Jan,

3Filip,

Bartoloměj,

Tomáš,

Matouš – bývalý celník,

Jakub – syn Alfeův,

Tadeáš,

4Šimon Kenaanský

a Jidáš Iškariotský,

jenž ho nakonec zradil.

5Těchto dvanáct Ježíš vyslal a na cestu jim dal pokyny: „Nechoďte nyní mezi pohany a nevcházejte do samařských měst. 6-7Raději jděte k těm Izraelcům, kteří se Bohu odcizili, a rozhlašujte, že Boží království je již blízko. 8Uzdravujte nemocné, mrtvé probouzejte k životu, očišťujte malomocné, vyhánějte démony. Co jste zdarma dostali, zdarma rozdávejte.

9Neshánějte žádné peníze, 10neberte si na cestu zavazadlo s náhradními šaty či obuví, ani hůl na obranu. Jako dělník dostává mzdu, tak i ti, kterým sloužíte, by se měli o vás postarat. 11Kdykoliv vstoupíte do města nebo vesnice, ptejte se po bohabojném člověku a v jeho domě pak zůstaňte, dokud se nevydáte na další cestu.

12Když vstoupíte do domu, pozdravte přáním pokoje. 13Jestliže vaše poselství vděčně přijmou, naplní je pokoj, který přinášíte. 14Odmítnou-li, jejich škoda, vám pokoj zůstane. Opusťte každé město nebo dům, kde by vás ani vaše svědectví nepřijali, a nezdržujte se s nimi. 15Říkám vám, že takové město na tom bude v den soudu hůře než Sodoma a Gomora.

Ježíš připravuje učedníky na pronásledování

16Posílám vás jako ovce mezi vlky. Buďte tedy obezřetní jako hadi a bezelstní jako holubice.

17Mějte se na pozoru před lidmi, protože vás budou vydávat soudům a budou vás bičovat v synagogách, 18vláčet vás před vládce a panovníky kvůli mně. To všechno bude příležitost, abyste jim i celému světu vydali svědectví. 19Až vás postaví před soud, nedělejte si starosti s tím, jak a co budete mluvit, protože vám budou dána pravá slova v pravý čas. 20To nebudete mluvit vy, ale Duch vašeho Otce promluví skrze vás.

21Bratr vydá bratra na smrt, otec syna, děti se vzbouří proti rodičům a zabijí je. 22Všichni vás budou nenávidět, protože jste moji. Ale ten, kdo vytrvá až do konce, bude zachráněn pro věčnost. 23Budou-li vás v některém městě pronásledovat, utečte do jiného. Říkám vám, že nestačíte projít všechna izraelská města dříve, než se prokáže, kdo vlastně jsem.

24Žák nemůže očekávat víc než učitel, ani služebník Boží víc než jeho pán. 25Ať je spokojen s údělem svého učitele a pána. Když mne obvinili, že jsem ve spojení s ďáblem, co si asi vymyslí na vás!

26Ale nebojte se jich. Přijde čas, že pravda vyjde najevo a všechno skryté bude odhaleno. 27Co vám říkám ve tmě, povězte na světle, a co vám šeptám do ucha, rozhlašujte veřejně!

28A nebojte se těch, kteří zabíjejí tělo; věčný život vzít nemohou. Spíše mějte strach z toho, který vás může navěky zahubit. 29-30Jakoupak cenu má vrabec? A přece ani jeden nespadne na zem bez vědomí vašeho Otce. 31Tak nemějte strach – jste daleko cennější než celé hejno vrabců. Otci záleží na každém vašem vlásku.

32Kdo se ke mně přizná před lidmi, k tomu se i já budu hlásit před svým Otcem v nebi. 33Kdo mne však před lidmi zapře, toho se zřeknu před svým nebeským Otcem.

34Nemyslete si, že můj příchod přinese světu bezprostřední pokoj; můj příchod způsobí i boj a násilí. 35Víra ve mne může rozdělit syna a otce, dceru a matku, snachu a tchyni. 36Nepochopení a zloba vlastní rodiny bývají nejhlubší. 37Kdo má ve svém srdci na prvním místě otce nebo matku, syna nebo dceru, a ne mne, není mne hoden. 38Kdo by chtěl za mnou jít a nevzal by na sebe tyto těžkosti jako kříž, není mne hoden. 39Kdo lpí na svém životě, ztratí ho, kdo však je ochoten pro mne všechno obětovat, ten teprve pravý život získá.

40Kdo přijímá vás, přijímá mne, a kdo přijímá mne, ten přijímá toho, který mne poslal. 41Přijme-li někdo mého svědka s vědomím, že Bůh ho posílá, dostane stejnou odměnu jako on. Kdo se ujme věřícího pro jeho víru ve mne, dostane stejnou odměnu jako ten věřící. 42A kdo by podal třeba jen sklenici studené vody jednomu z nepatrných, protože je můj učedník, ten bude určitě odměněn.“