Mattiyu 1 – HCB & OL

Hausa Contemporary Bible

Mattiyu 1:1-25

Asalin Yesu Kiristi

(Luka 3.23-38)

1Tarihin da aka rubuta game da asalin Yesu Kiristi ɗan Dawuda, ɗan Ibrahim.

2Ibrahim ya haifi Ishaku,

Ishaku ya haifi Yaƙub,

Yaƙub ya haifi Yahuda da ’yan’uwansa,

3Yahuda ya haifi Ferez da Zera, waɗanda Tamar ce mahaifiyarsu;

Ferez ya haifi Hezron,

Hezron ya haifi Ram,

4Ram ya haifi Amminadab,

Amminadab ya haifi Nashon,

Nashon ya haifi Salmon,

5Salmon ya haifi Bowaz, wanda Rahab ce mahaifiyarsa,

Bowaz ya haifi Obed, wanda Rut ce mahaifiyarsa,

Obed ya haifi Yesse,

6Yesse kuwa ya haifi Sarki Dawuda.

Dawuda ya haifi Solomon, wanda matar Uriya ce mahaifiyarsa.

7Solomon ya haifi Rehobowam,

Rehobowam ya haifi Abiya,

Abiya ya haifi Asa,

8Asa ya haifi Yehoshafat,

Yehoshafat ya haifi Yehoram,

Yehoram ya haifi Azariya,

9Azariya ya haifi Yotam,

Yotam ya haifi Ahaz,

Ahaz ya haifi Hezekiya,

10Hezekiya ya haifi Manasse,

Manasse ya haifi Amon,

Amon ya haifi Yosiya,

11Yosiya kuma ya haifi Yekoniya1.11 Wato, Jehohiyachin; haka ma a aya 12 da ’yan’uwansa a lokacin da aka kwashe su zuwa bauta a Babilon.

12Bayan an kwashe su zuwa bauta a Babilon.

Yekoniya ya haifi Sheyaltiyel,

Sheyaltiyel ya haifi Zerubbabel,

13Zerubbabel ya haifi Abiyud,

Abiyud ya haifi Eliyakim,

Eliyakim ya haifi Azor,

14Azor ya haifi Zadok,

Zadok ya haifi Akim,

Akim kuma ya haifi Eliyud,

15Eliyud ya haifi Eleyazar,

Eleyazar ya haifi Mattan,

Mattan ya haifi Yaƙub,

16Yaƙub ya haifi Yusuf, mijin Maryamu, wadda ta haifi Yesu, wanda ake kira Kiristi.

17Ta haka akwai zuriya goma sha huɗu ke nan duka-duka daga lokacin Ibrahim zuwa lokacin Dawuda, goma sha huɗu kuma daga Dawuda zuwa bauta a Babilon, goma sha huɗu kuma daga bauta a Babilon zuwa Kiristi.1.17 Ko kuwa Kiristi. Kiristi (Da Girik) Almasihu (Da Ibraniyanci) duk suna nufin “Shafaffe.”

Haihuwar Yesu Kiristi

(Luka 2.1-7)

18Ga yadda haihuwar Yesu Kiristi ta kasance. An yi alkawarin auren mahaifiyarsa Maryamu, ga Yusuf. Amma tun kafin su zama miji da mata, sai aka tarar Maryamu tana da ciki, ta wurin Ruhu Mai Tsarki. 19Yusuf mijinta, da yake shi mai adalci ne, bai so yă ba ta kunya, yă tone mata asiri a fili ba, sai ya yi tunani yă sake ta a ɓoye.

20Amma yana cikin wannan tunani, sai wani mala’ikan Ubangiji ya bayyana masa cikin mafarki ya ce, “Yusuf ɗan Dawuda, kada ka ji tsoron ɗaukan Maryamu zuwa gidanka a matsayin matarka, gama cikin nan nata, daga wurin Ruhu Mai Tsarki ne. 21Za tă haifi ɗa, za ka kuma sa masa suna Yesu,1.21 Yesu da Girik shi ne Yoshuwa da Ibraniyanci, wanda yake nufin Ubangiji yana ceto. gama shi ne zai ceci mutanensa daga zunubansu.”

22Duk wannan ya faru ne, don a cika abin da Ubangiji ya faɗi ta bakin annabin cewa, 23“Ga shi budurwa za tă yi ciki, za tă haifi ɗa, kuma za a kira shi Immanuwel”1.23 Ish 7.14 (wanda yake nufin “Allah tare da mu”).

24Da Yusuf ya farka daga barci, sai ya bi umarnin mala’ikan Ubangiji, ya ɗauki Maryamu zuwa gida a matsayin matarsa. 25Amma bai kwana da ita ba, sai bayan da ta haifi ɗan. Ya kuwa sa masa suna Yesu.

O Livro

Mateus 1:1-25

A genealogia de Jesus Cristo

(Lc 3.23-38)

1São estes os antepassados de Jesus Cristo, descendente do rei David e de Abraão.

2Os descendentes de Abraão foram sucessivamente Isaque, Jacob, Judá e os seus irmãos. 3Judá foi pai de Perez e de Zera. Tamar foi a mãe de ambos. Depois de Perez vieram Hezrom, Rão, 4Aminadabe, Nassom, Salmom, 5Boaz, cuja mãe foi Raabe, Obede, que teve por mãe Rute, 6Jessé e o rei David.

Os descendentes de David foram Salomão, cuja mãe tinha sido mulher de Urias, 7Roboão, Abias, Asa, 8Jeosafá, Jorão, Uzias, 9Jotão, Acaz, Ezequias, 10Manassés, Amom, Josias, 11Jeconias e seus irmãos, que nasceram quando os judeus foram deportados para a Babilónia.

12Depois desse exílio, a linha de descendência continuou sucessivamente com Jeconias, Sealtiel, Zorobabel, 13Abiude, Eliaquim, Azor, 14Zadoque, Aquim, Eliude, 15Eleazar, Matã, Jacob 16e por fim José, marido de Maria, mãe de Jesus, chamado Cristo.

17São catorze gerações desde Abraão até ao rei David; catorze desde o tempo do rei David até ao exílio na Babilónia; e catorze do exílio até Cristo.

O nascimento de Jesus

18Eis o que se passou antes do nascimento de Jesus Cristo. Maria, sua mãe, estava noiva de José mas, embora fosse virgem, ficou grávida pelo Espírito Santo. 19José, o seu noivo, homem justo, decidiu pôr termo à promessa de casamento, querendo porém fazê-lo de modo que ela não ficasse com má fama entre o povo.

20Estando ele a pensar no caso, teve um sonho em que viu um anjo de pé, ao seu lado, que lhe dizia: “José, filho de David, não tenhas medo de aceitar Maria como tua mulher! A criança que ela traz no ventre foi gerada pelo Espírito Santo. 21Ela terá um filho a quem porás o nome de Jesus, porque ele salvará o seu povo dos seus pecados.” 22Assim se cumpriu a mensagem de Deus através dos seus profetas:

23“A virgem ficará grávida e dará à luz um filho,

e pôr-lhe-ão o nome de Emanuel.”1.23 Is 7.14.

Emanuel quer dizer: Deus está connosco.

24Quando acordou, José fez o que o anjo lhe mandara e levou Maria para casa como sua mulher. 25Mas ela continuou virgem até nascer o seu filho. José pôs-lhe o nome de Jesus.