Kolossiyawa 1 – HCB & NVI-PT

Hausa Contemporary Bible

Kolossiyawa 1:1-29

1Bulus, wanda Allah ya zaɓa don yă zama manzon Kiristi Yesu, da kuma daga Timoti ɗan’uwanmu,

2Zuwa ga tsarkaka da kuma amintattun ’yan’uwa cikin Kiristi da suke a Kolossi.

Alheri da salama daga Allah Ubanmu, su kasance tare da ku.1.2 Waɗansu rubuce-rubucen hannu na dā suna da Uba da Ubangiji Yesu Kiristi

Godiya da addu’a

3Kullum muna gode wa Allah, Uban Ubangijinmu Yesu Kiristi, sa’ad da muke addu’a dominku. 4Gama mun ji labarin bangaskiyarku a cikin Yesu Kiristi da kuma ƙaunar da kuke yi saboda dukan tsarkaka. 5Kuna yin haka ne kuwa domin abin da kuke bege yana a ajiye a sama. Kun riga kun ji game da wannan bege sa’ad da kuka gaskata saƙon nan na gaskiya wanda shi ne bisharar 6da ta zo muku. Ko’ina a duniya wannan bishara tana yi ta haihuwa tana kuma girma, kamar yadda take yi a cikinku tun daga ranar da kuka ji ta kuka kuma fahimci alherin Allah cikin dukan gaskiyarta. 7Kun koyi wannan gaskiya daga wurin Efafaras, ƙaunataccen abokin hidimarmu, wanda yake amintacce mai hidimar Kiristi a madadinmu, 8wanda kuma ya faɗa mana ƙaunar da kuke yi cikin Ruhu.

9Shi ya sa tun daga ranar da muka sami labarin, ba mu fasa yin addu’a dominku ba. Kullum muna roƙon Allah yă sa ku san kome da yake so ku yi, domin ku sami hikima ta Ruhu, ku kuma sami ganewar kome duka. 10Ta haka za ku yi rayuwa wadda ta dace da Ubangiji, ku kuma gamshe shi a ta kowace hanya, kuna yin aiki mai kyau ta kowace hanya, kuna kuma yin girma cikin sanin Allah. 11Allah yă ƙarfafa ku da dukan iko bisa ga ɗaukakar ƙarfinsa domin ku kasance da jimrewa sosai da kuma haƙuri, cikin farin ciki 12kuna gode wa Uba, wanda ya sa kuka cancanci ku sami rabo a gādon tsarkaka a cikin mulkin haske. 13Gama ya riga ya cece mu daga mulkin duhu ya kuma kawo mu cikin mulkin Ɗan da yake ƙauna, 14wanda ta wurinsa muka sami fansa da kuma gafarar zunubai.

Fifikon Kiristi

15Kiristi shi ne surar da ake gani na Allah wanda ba a iya gani, ɗan fari a kan dukan halitta. 16Ta wurinsa aka halicci dukan abu, abubuwan da suke cikin sama da abubuwan da suke a duniya, waɗanda ake gani, da waɗanda ba a gani, ko kursiyoyi ko ikoki ko masu mulki ko hukumomi; an halicci dukan abu ta wurinsa da kuma dominsa ne. 17Ya kasance kafin dukan abu, kuma a cikinsa ne dukan abubuwa suke a harhaɗe. 18Shi ne kuma kan ikkilisiya, wadda take jikinsa. Shi ne mafari da kuma na farko da ya tashi daga matattu, domin a cikin kowane abu yă zama mafifici. 19Gama Allah ya ji daɗi yă sa dukan cikarsa ta kasance a cikin Kiristi, 20ta wurin Kiristi ne ya komar da kome zuwa ga kansa. Ya kawo salama ga abubuwan da suke ƙasa da abubuwan da suke sama, ta wurin jinin Kiristi da ya zubar a kan gicciye.

21A dā kuna a ware da Allah, kuka kuma zama abokan gāba a cikin tunaninku saboda mugun halinku. 22Amma Ɗansa ya zama mutum ya kuma mutu. Saboda haka Allah ya yi sulhu da ku, yanzu kuwa ya bar ku ku tsaya a gabansa da tsarki, marasa aibi, da kuma marasa abin zargi. 23Sai ku ci gaba cikin bangaskiyarku, kuna tsaye a kafe kuma tsayayyu, ba tare da gusawa daga begen da kuka ji daga bishara ba. Wannan ita ce bisharar da kuka ji wadda aka yi shelarta ga kowace halittar da take ƙarƙashin sama, wadda kuma ni Bulus, na zama mai hidimarta.

Hidimar Bulus ga ikkilisiya

24Yanzu, ina farin ciki saboda wuyar da nake sha dominku, don ta wurin wuyan nan zan cika abin da ya rage na wuyar da Kiristi ya sha saboda jikinsa, wato, ikkilisiya. 25Na zama mai hidimar ikkilisiya bisa ga aikin nan da Allah ya ba ni amana saboda ku, domin in sanar da maganar Allah sosai. 26Wannan magana da nake gaya muku asiri ne da yake a ɓoye tun zamanai masu yawa, wanda yanzu aka bayyana ga tsarkaka. 27Su ne Allah ya so yă sanar da yadda irin yalwar ɗaukakar asirin nan take a cikin al’ummai, asirin nan kuwa shi ne Kiristi a cikinku, begen ɗaukakar da za a bayyana.

28Saboda haka ko’ina muka tafi, muna shela, muna gargaɗi, muna kuma koyar da kowa da dukan hikima, don mu miƙa kowa cikakke a cikin Kiristi. 29Don haka ne ina fama, ina kuma ƙoƙari da duk ƙarfin nan da Kiristi ya ba ni.

Nova Versão Internacional

Colossenses 1:1-29

1Paulo, apóstolo de Cristo Jesus pela vontade de Deus, e o irmão Timóteo,

2aos santos e fiéis1.2 Ou crentes irmãos em Cristo que estão em Colossos:

A vocês, graça e paz da parte de Deus nosso Pai e do Senhor Jesus Cristo1.2 Vários manuscritos não trazem e do Senhor Jesus Cristo..

Ação de Graças

3Sempre agradecemos a Deus, o Pai de nosso Senhor Jesus Cristo, quando oramos por vocês, 4pois temos ouvido falar da fé que vocês têm em Cristo Jesus e do amor que têm por todos os santos, 5por causa da esperança que está reservada a vocês nos céus, a respeito da qual ouviram por meio da palavra da verdade, o evangelho 6que chegou até vocês. Por todo o mundo este evangelho vai frutificando e crescendo, como também ocorre entre vocês, desde o dia em que o ouviram e entenderam a graça de Deus em toda a sua verdade. 7Vocês o aprenderam de Epafras, nosso amado cooperador, fiel ministro de Cristo para conosco1.7 Vários manuscritos dizem para com vocês., 8que também nos falou do amor que vocês têm no Espírito.

9Por essa razão, desde o dia em que o ouvimos, não deixamos de orar por vocês e de pedir que sejam cheios do pleno conhecimento da vontade de Deus, com toda a sabedoria e entendimento espiritual. 10E isso para que vocês vivam de maneira digna do Senhor e em tudo possam agradá-lo, frutificando em toda boa obra, crescendo no conhecimento de Deus e 11sendo fortalecidos com todo o poder, de acordo com a força da sua glória, para que tenham toda a perseverança e paciência com alegria, 12dando graças ao Pai, que nos1.12 Alguns manuscritos dizem os. tornou dignos de participar da herança dos santos no reino da luz. 13Pois ele nos resgatou do domínio das trevas e nos transportou para o Reino do seu Filho amado, 14em quem temos a redenção1.14 Alguns manuscritos dizem redenção por meio do seu sangue., a saber, o perdão dos pecados.

A Supremacia de Cristo

15Ele é a imagem do Deus invisível,

o primogênito sobre toda a criação,

16pois nele foram criadas todas as coisas nos céus e na terra,

as visíveis e as invisíveis,

sejam tronos sejam soberanias, poderes ou autoridades;

todas as coisas foram criadas por ele e para ele.

17Ele é antes de todas as coisas,

e nele tudo subsiste.

18Ele é a cabeça do corpo, que é a igreja;

é o princípio e o primogênito dentre os mortos,

para que em tudo tenha a supremacia.

19Pois foi do agrado de Deus

que nele habitasse toda a plenitude1.19 Ou Pois toda a plenitude agradou-se em habitar nele,

20e por meio dele reconciliasse consigo todas as coisas,

tanto as que estão na terra

quanto as que estão nos céus,

estabelecendo a paz pelo seu sangue derramado na cruz.

21Antes vocês estavam separados de Deus e, na mente de vocês, eram inimigos por causa do mau1.21 Ou conforme demonstrado pelo mau procedimento de vocês. 22Mas agora ele os reconciliou pelo corpo físico de Cristo1.22 Grego: corpo da sua carne., mediante a morte, para apresentá-los diante dele santos, inculpáveis e livres de qualquer acusação, 23desde que continuem alicerçados e firmes na fé, sem se afastarem da esperança do evangelho, que vocês ouviram e que tem sido proclamado a todos os que estão debaixo do céu. Esse é o evangelho do qual eu, Paulo, me tornei ministro.

O Trabalho de Paulo pela Igreja

24Agora me alegro em meus sofrimentos por vocês e completo no meu corpo1.24 Grego: na minha carne. o que resta das aflições de Cristo, em favor do seu corpo, que é a igreja. 25Dela me tornei ministro de acordo com a responsabilidade, por Deus a mim atribuída, de apresentar a vocês plenamente a palavra de Deus, 26o mistério que esteve oculto durante épocas e gerações, mas que agora foi manifestado a seus santos. 27A ele quis Deus dar a conhecer entre os gentios1.27 Isto é, os que não são judeus. a gloriosa riqueza deste mistério, que é Cristo em vocês, a esperança da glória.

28Nós o proclamamos, advertindo e ensinando a cada um com toda a sabedoria, para que apresentemos todo homem perfeito em Cristo. 29Para isso eu me esforço, lutando conforme a sua força, que atua poderosamente em mim.