2 Korintiyawa 1 – HCB & NUB

Hausa Contemporary Bible

2 Korintiyawa 1:1-24

1Bulus, manzon Kiristi Yesu ta wurin nufin Allah, da kuma daga Timoti ɗan’uwanmu,

Zuwa ga ikkilisiyar Allah da take a Korint, tare da dukan tsarkaka a ko’ina a Akayya.

2Alheri da salama daga Allah Ubanmu da kuma Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.

Allah na dukan ta’aziyya

3Yabo ya tabbata ga Allah, da Uban Ubangijinmu Yesu Kiristi, Uba mai tausayi, da kuma Allah na dukan ta’aziyya, 4wanda yakan yi mana ta’aziyya a cikin dukan wahalolinmu, domin mu kuma mu iya ta’azantar da waɗanda suke cikin kowace irin wahala, da ta’aziyyar da mu kanmu muka samu daga Allah. 5Gama kamar yadda wahalar Kiristi ta cika har tana zuba a cikin rayuwarmu, haka nan kuma ta wurin Kiristi ta’aziyyarmu ta cika har tana zuba. 6In muna shan wahala, ai, muna shanta domin ta’aziyyarku, da cetonku ne, in mun sami ta’aziyya, ai, mun same ta domin ta’aziyyarku ce, wadda take sa ku jure wa irin wahalan nan, da muke sha. 7Begen da muke da shi dominku kuwa, tabbatacce ne, domin mun san cewa kamar yadda kuke tarayya da mu a cikin wahalolinmu, haka kuma kuke tarayya da mu a cikin ta’aziyyarmu.

8’Yan’uwa, ba ma so ku zama da rashin sani, a kan wahalolin da muka sha a lardin Asiya. Mun sha wahaloli sosai, har abin ya fi ƙarfinmu, ya sa muka fid da tsammanin rayuwa. 9Ba shakka, a zuciyarmu mun ji kamar hukuncin kisa ne aka yi mana. Wannan kuwa ya faru ne domin kada mu dogara da kanmu, sai dai ga Allah, wanda yake tā da matattu. 10Shi ya cece mu daga irin wannan hatsari na mutuwa, zai kuwa cece mu. A kansa muka kafa bege cewa zai ci gaba da cetonmu, 11yayinda kuke taimakonmu ta wurin addu’o’inku. Mutane da yawa kuwa za su yi godiya ta dalilinmu, saboda albarkar da aka yi mana, ta amsa addu’o’i masu yawa.

Canja shirye-shiryen Bulus

12Wannan shi ne taƙamarmu. Lamirinmu yana ba da shaida cewa mun yi zamanmu a duniya, musamman a dangantakarmu da ku cikin tsarki, tsakani da Allah. Mun yi haka ta wurin bishewar alherin Allah, ba bisa ga hikimar duniya ba. 13Gama ba mu rubuta muku abin da ba za ku iya karatu ko ku kāsa fahimta ba. Ina kuma fata cewa, 14kamar yadda kuka ɗan fahimce mu, za ku kai ga cikakkiyar fahimta cewa za ku iya yin taƙama da mu, kamar yadda mu ma za mu yi taƙama da ku a ranar da Ubangiji Yesu zai dawo.

15Saboda na amince da haka, shi ya sa na so zuwa wurinku da fari, domin ku sami albarka riɓi biyu. 16Na yi shiri in ziyarce ku a kan hanyata zuwa Makidoniya, in kuma sāke dawo wurinku a kan hanyata daga Makidoniya, sa’an nan ku yi mini rakiya a hanyata zuwa Yahudiya. 17Kuna gani na yi wannan shirin ba da sanin abin da nake yi ba ne? Ko kuwa, kuna gani na yi shirin nan da halin mutuntaka ne, don in ce, “I” in koma in ce, “A’a”?

18Kamar dai yadda ba shakka Allah yake mai aminci, haka ma maganar da muka yi muku, ba “I” da kuma “A’a” ba ce. 19Gama Ɗan Allah, Yesu Kiristi, wanda ni da Sila da Timoti muka yi muku wa’azinsa, ai, ba “I” da “A’a” ba ne, amma a cikin Kiristi, “I” ne kullum. 20Domin dukan alkawaran Allah cikarsu a gare shi suke, ta wurinsa ne kuma muke faɗar “Amin”, domin a ɗaukaka Allah. 21Allah ne fa yake sa mu da ku mu tsaya daram cikin Kiristi. Shi ne ya shafe mu, 22ya buga mana hatiminsa a kan mu nasa ne, ya kuma sa mana Ruhunsa a cikin zukatanmu, domin yă tabbatar da abin da yake zuwa nan gaba.

23Labudda, Allah shi ne shaidata cewa don kada in ƙara muku wahala ne ya sa ban koma Korint ba. 24Ba nuna muku iko a kan bangaskiyarku muke yi ba, sai dai muna aiki tare da ku ne saboda farin cikinku, domin bisa ga bangaskiya ce kuke tsaye da ƙarfi.

Swedish Contemporary Bible

2 Korintierbrevet 1:1-24

Hälsning

1Från Paulus, som genom Guds vilja är apostel1:1 Eller sändebud. åt Kristus1:1 Se not till Matt 1:1. Jesus, och från vår bror Timotheos.

Till Guds församling i Korinth, och till alla de troende runt om i provinsen Achaia.

2Nåd och frid från Gud, vår Fader, och Herren Jesus Kristus.

Gud tröstar och uppmuntrar

3Välsignad är vår Herre Jesus Kristus Gud och Fader, barmhärtighetens Fader, all trösts Gud. 4Han tröstar oss i alla våra svårigheter, så att vi själva kan ge vidare av hans tröst och uppmuntran till andra som har det svårt. 5Ju mer vi får lida för Kristus skull, desto mer tröst får vi genom Kristus. 6När vi möter svårigheter är det alltså för er tröst och frälsning. Genom den tröst vi själva får kan ni få tröst som ger er kraft när ni får gå igenom samma lidanden som vi. 7Vårt hopp är fast när det gäller er. Vi vet att ni delar lidandena med oss, och likaså delar ni också vår tröst.

8Jag vill att ni ska veta, syskon, vilka enorma svårigheter vi fick gå igenom i provinsen Asien1:8 Provinsen Asien var en romersk provins i nuvarande Turkiet.. Vi var så illa ute att vi inte hade några krafter kvar, och vi trodde faktiskt att vår sista stund var kommen. 9Ja, vi hade inom oss fått en dödsdom. Men detta var för att vi inte skulle lita på oss själva, utan på Gud, han som uppväcker de döda. 10Och Gud räddade oss verkligen ur denna dödsfara, och han ska göra det igen. Till honom har vi satt vårt hopp, och han kommer att rädda oss igen. 11Men ni hjälper oss genom era böner, och så ska många tacka Gud för oss och för den nåd vi fått.

Paulus ändrade resplaner

12Vår stolthet är att vårt samvete kan vittna om att vi här i världen, och särskilt i vår relation mot er, alltid har handlat i helighet och renhet från Gud. Vi har inte styrts av mänsklig vishet utan av Guds nåd. 13Vi skriver ingenting annat till er än det ni kan läsa och förstå. Jag hoppas också att ni helt och fullt ska förstå 14det som ni redan delvis har förstått, att ni på Herren Jesus dag kan vara lika stolta över oss som vi är över er.

15Eftersom jag litade på detta, hade jag tänkt glädja er, med inte bara ett, utan två besök. 16Jag hade tänkt besöka er först på min väg till Makedonien, och sedan på vägen hem igen. Då skulle ni ha fått hjälpa mig med det jag behöver för min resa till Judeen.

17När jag nu tänkte så, hade jag lagt mina planer lite väl lättvindigt? Kanske säger jag, i mänsklig svaghet, en sak och menar en annan? 18Nej, så sant Gud är trofast, så säger vi inte både ja och nej på samma gång. 19Kristus Jesus, Guds Son, som jag och Silvanus och Timotheos har förkunnat bland er, var ju heller aldrig ja och nej, utan i honom finns bara ett ja. 20För allt det som Gud har lovat har fått sitt ja genom Jesus. Därför säger också vi vårt Amen genom honom till Guds ära. 21Det är ju Gud som hjälper både er och mig att hålla fast vid Kristus och har smort oss. 22Han har satt sitt sigill på oss och gett oss Anden som en säkerhet i våra hjärtan.

23Gud själv kan intyga att det var för att skona er som jag inte mer ville komma till Korinth. 24Men vi vill inte styra över er tro. Nej, vi vill bara hjälpa er att vara glada över den tro som ni redan står fasta i.