Otkrivenje 5 – CRO & HCB

Knijga O Kristu

Otkrivenje 5:1-14

Jaganjac otvara svitak

1U desnici Onoga na prijestolju ugledam svitak ispisan s obiju strana i zapečaćen sa sedam pečata. 2Ugledam zatim snažnog anđela kako glasno viče: “Tko je dostojan razlomiti pečate i otvoriti svitak?” 3Ali nitko u nebu, ni na zemlji, ni ispod zemlje nije mogao otvoriti svitak i pogledati u njega.

4Gorko sam zaplakao jer nije bilo nikoga dostojnoga da otvori knjigu i pročita što u njoj piše. 5Ali jedan od četvorice starješina mi reče: “Ne plači! Pobijedio je, evo, Lav iz Judina plemena, nasljednik Davidova prijestolja.5:5 U grčkome: korijen Davidov. On je dostojan otvoriti svitak i razlomiti sedam pečata.”

6Ugledam zatim zaklanog Jaganjca kako stoji između prijestolja i četiriju bića te između starješina. Imao je sedam rogova i sedam očiju koje su sedam Božjih duhova poslanih po svoj zemlji. 7Jaganjac pristupi pa iz desnice Onoga na prijestolju uzme svitak. 8Kad to učini, četiri bića i dvadeset četvorica starješina padnu ničice pred njega. Svaki je imao citru i zlatne posude pune kada—molitve Božjega naroda!

9Zapjevaju mu novu pjesmu:

“Dostojan si uzeti svitak

i razlomiti pečate

jer si bio zaklan

i svojom si krvlju za Boga otkupio

iz svakoga plemena, jezika i naroda.

10Učinio si ih kraljevstvom i svećenstvom našega Boga.

Oni će kraljevati na zemlji.”

11Pogledam opet i začujem glas anđela oko prijestolja, bića i starješina. Bilo ih je tisuće milijuna. 12Jakim glasom pjevali su:

“Dostojan je zaklani Jaganjac

primiti moć i bogatstvo,

mudrost i snagu,

čast i slavu i blagoslov!”

13Začujem tada kako sve stvorenje na nebu, na zemlji i pod zemljom te u moru govori:

“Blagoslov, čast i slava pripadaju

Onomu koji sjedi na prijestolju

i Jaganjcu, u vijeke vjekova.”

14Četiri bića ponavljala su: “Amen!” A starješine padnu ničice i poklone mu se.

Hausa Contemporary Bible

Ruʼuya ta Yohanna 5:1-14

Naɗaɗɗen littafi da kuma Ɗan Ragon

1Sa’an nan na ga a hannun damar wannan wanda yake zaune a kursiyin naɗaɗɗen littafi da rubutu a ciki da wajensa an kuma hatimce shi da hatimai bakwai. 2Na kuma ga wani babban mala’ika yana shela da babbar murya cewa, “Wa ya cancanta yă ɓalle hatiman nan yă kuma buɗe naɗaɗɗen littafin?” 3Amma ba wani a sama ko a ƙasa ko a ƙarƙashin ƙasan da ya iya buɗe naɗaɗɗen littafin ko ma yă duba cikinsa. 4Na yi ta kuka domin ba a iya samun wanda ya cancanta yă buɗe naɗaɗɗen littafin ko yă duba cikinsa ba. 5Sai ɗaya daga cikin dattawan ya ce mini, “Kada ka yi kuka! Duba, Zakin kabilar Yahuda, da kuma Tushen Dawuda ya ci nasara. Ya iya buɗe naɗaɗɗen littafin da hatimansa bakwai.”

6Sa’an nan na ga Ɗan Rago, yana kamar an yanka, tsaye a tsakiyar kursiyin, halittu huɗun nan masu rai da kuma dattawan an sun kewaye shi. Yana da ƙahoni bakwai da idanu bakwai, waɗanda suke ruhohi bakwai na Allah da aka aika cikin dukan duniya. 7Ya zo ya karɓi naɗaɗɗen littafin daga hannun dama na wannan wanda yake zaune a kursiyin. 8Bayan ya karɓa, sai halittu huɗun nan masu rai da kuma dattawan nan ashirin da huɗu suka fāɗi ƙasa a gaban Ɗan Ragon. Kowannensu yana da garaya kuma suna riƙe da kaskon zinariya cike da turare, waɗanda suke addu’o’in tsarkaka. 9Suka rera sabuwar waƙa,

“Ka cancanci ka karɓi naɗaɗɗen littafin

ka kuma buɗe hatimansa,

domin an kashe ka,

da jininka kuma ka sayi mutane wa Allah,

daga kowace kabila da harshe da mutane da kuma al’umma.

10Ka mai da su masarauta da kuma firistoci, don su yi wa Allahnmu hidima,

kuma za su yi mulki a duniya.”

11Sai na duba na kuma ji muryar mala’iku masu yawa, yawansu kuwa ya kai dubu dubbai, da kuma dubu goma sau dubu goma. Suka kewaye kursiyin da halittu huɗun nan masu rai da kuma dattawan nan. 12Da babbar murya suka rera,

“Macancanci ne Ɗan Ragon nan da aka kashe,

don yă sami iko da wadata da hikima da ƙarfi

da girma da ɗaukaka da kuma yabo!”

13Sa’an nan na ji kowace halitta a sama da ƙasa da ƙarƙashin ƙasa da kuma bisan teku, da kome da yake cikinsu yana rerawa,

“Gare shi mai zama a kan kursiyin da kuma ga Ɗan Ragon

yabo da girma da ɗaukaka da iko,

sun tabbata har abada abadin!”

14Sai halittu huɗun nan masu rai suka ce, “Amin”, dattawan kuma suka fāɗi suka yi sujada.