Hebrejima 11 – CRO & HCB

Knijga O Kristu

Hebrejima 11:1-40

Veliki primjeri vjere

1Vjera je čvrsto pouzdanje da će se dogoditi ono čemu se nadamo; ona je dokaz stvarnosti koju ne vidimo. 2Vjerom su naši praoci postignuli da ih Bog pohvali.

3Vjerom znamo da je sve što postoji stvoreno Božjom zapovijedi, da je stvoreno iz nevidljivoga.

4Vjerom je Abel prinio Bogu bolju žrtvu nego Kain. Bog je prihvatio Abelovu žrtvu kako bi pokazao da je on pravedan čovjek. Tako nam Abel, iako odavno mrtav, još govori zbog svoje vjere.

5Zbog svoje vjere Henok je prenesen u nebo a da nije iskusio smrti; “nestao je jer ga je Bog uzeo”.11:5 Postanak 5:24. Ali prije nego što je prenesen primio je svjedočanstvo da je ugodio Bogu. 6Bogu ne možete nikada udovoljiti bez vjere. Tko želi doći k Bogu, mora vjerovati da Bog postoji i da nagrađuje one koji ga iskreno traže.

7Vjerom je Noa izgradio korablju da svoju obitelj spasi od potopa. Poslušao je Boga koji ga je upozorio da će se zbiti ono što se nikada prije nije dogodilo. Vjerom je osudio ostali svijet i stekao pravednost pred Bogom.

8Vjerom je Abraham poslušao Boga kad ga je pozvao da ostavi dom i ode u drugu zemlju koju mu je Bog dao u baštinu. Otišao je ne znajući kamo ide. 9Čak i kad je stigao u zemlju koju mu je Bog obećao, i ondje je živio po vjeri—jer bio je poput tuđinca i živio je pod šatorom, skupa s Izakom i Jakovom kojima je Bog dao isto obećanje. 10Jer iščekivao je grad s vječnim temeljima, kojega je Bog graditelj i tvorac. 11Vjerom je i Sara s Abrahamom mogla začeti dijete unatoč svojoj poodmakloj dobi i unatoč tomu što nije mogla imati djece. Abraham je vjerovao da će Bog održati obećanje.11:11 U nekim rukopisima: Sara je vjerovala da će Bog održati obećanje. 12Tako je od jednog Abrahama, prestara da ima djecu, nastao narod brojan poput zvijezda na nebu i neizbrojiva pijeska na morskoj obali.

13Svi su ti ljudi u vjeri umrli a da nisu primili što im je Bog obećao, već su to vidjeli samo izdaleka i prihvatili priznajući da su na zemlji tuđinci i pridošlice. 14A tko za sebe tako kaže, očito čezne za domovinom. 15Da su mislili na zemlju iz koje su došli, mogli su se u nju vratiti. 16Ali oni su se radovali boljemu mjestu, nebeskoj domovini. Zato se Bog ne srami nazvati njihovim Bogom. Pripravio im je nebeski grad.

17Vjerom je Abraham prinio Izaka kao žrtvu kad ga je Bog kušao. Taj Abraham, koji je već imao Božja obećanja, bio je spreman žrtvovati vlastitog sina, Izaka. 18Bog mu je obećao: “Po Izaku će ti se nazivati potomstvo.”11:18 Postanak 21:12. 19Vjerovao je da Bog može Izaka, ako i umre, oživjeti. To se donekle i dogodilo jer je Izak za Abrahama bio osuđen na smrt, ali je oživio.

20Vjerom je Izak blagoslovio dvojicu svojih sinova, Jakova i Ezava, pouzdajući se u Boga glede budućnosti.

21Vjerom je i Jakov, već star i na umoru, blagoslovio obojicu Josipovih sinova te se poklonio Bogu oslanjajući se na štap.

22Vjerom je i Josip na samrti s pouzdanjem govorio o tomu kako će Bog izvesti izraelski narod iz Egipta te zapovjedio da ponesu sa sobom i njegove kosti.

23Vjerom su Mojsija roditelji, kad se rodio, skrivali tri mjeseca. Vidjeli su da im je Bog dao lijepo djetešce i nisu se bojali kraljeve naredbe.

24Vjerom je Mojsije, kad je već odrastao, odbio zvati se sinom faraonove kćeri. 25Radije je odabrao da bude zlostavljan skupa s Božjim narodom nego da uživa u prolaznim zadovoljstvima grijeha. 26Vrednijim od egipatskog blaga smatrao je trpjeti sramotu zbog obećanoga Krista jer je gledao na nagradu koju će dobiti od Boga. 27Vjerom je Mojsije otišao iz Egipta ne bojeći se kraljeva bijesa, postojano kao da pred sobom gleda nevidljivoga Boga. 28Vjerom je zapovjedio izraelskome narodu da svetkuje pashalnu večeru i da poprska dovratke janjećom krvlju kako im Zatornik ne bi poubijao prvorođenu djecu.

29Vjerom je izraelski narod prošao kroz Crveno more kao po suhu tlu, a Egipćani su se utopili kad su to pokušali.

30Vjerom izraelskog naroda koji je sedam dana ophodio Jerihon pale su njegove zidine.

31Vjerom je bludnica Rahaba preživjela u tome gradu i nije poginula s nevjernicima jer je lijepo primila uhode.

32Što još reći? Predugo bi trajalo da vam potanko pričam o Gideonu, Baraku, Samsonu, Jefti, Davidu, Samuelu i prorocima. 33Ti su ljudi vjerom u Boga osvajali kraljevstva, pravedno vladali i primili što im je Bog obećao. Zatvorili su lavovima ralje, 34ugasili žestinu ognja, izbjegli smrtonosnoj oštrici mača. Oporavili su se od slabosti, ojačali u boju i nagnali u bijeg tuđinske vojske. 35Neke su žene zbog uskrsnuća ponovno zadobile svoje pokojne.

Druge su pak vjernike mučili, ali su oni radije umrli nego da se odreknu Boga pa da ih oslobode. Pouzdavali su se da će uskrsnuti u bolji život. 36Nekima su se izrugivali i bičevali ih, okivali ih i bacali u tamnice. 37Neke su kamenovali, neke prepilili napola, neke ubili mačem. Neki su hodali obučeni u ovčje i kozje kožuhe. Bili su gladni, potlačeni i zlostavljani. 38Svijet ih nije bio dostojan. Lutali su pustinjom i planinama, skrivali se u špiljama i jamama.

39Svi su ti ljudi stekli Božju naklonost zbog svoje vjere, a nitko od njih nije primio ono što im je Bog obećao. 40Jer Bog nam je svima namijenio bolje. Oni će postignuti savršenstvo, ali tek skupa s nama.

Hausa Contemporary Bible

Ibraniyawa 11:1-40

Ta wurin bangaskiya

1Bangaskiya ita ce kasance tabbacin abin da muke bege a kai da kuma tabbatar da abin da ba mu gani ba. 2Abin da aka yabi kakanni na dā a kai ke nan.

3Ta wurin bangaskiya ne muka fahimci cewa an halicci duniya bisa ga umarnin Allah, saboda an halicce abin da ake gani daga abin da ba a gani.

4Ta wurin bangaskiya Habila ya miƙa wa Allah hadayar da ta fi wadda Kayinu ya miƙa. Ta wurin bangaskiya aka yabe shi cewa shi mai adalci ne, sa’ad da Allah ya yi magana mai kyau game da bayarwarsa. Ta wurin bangaskiya kuma har yanzu yana magana, ko da yake ya riga ya mutu.

5Ta wurin bangaskiya ne aka ɗauki Enok daga wannan rayuwa, ta haka bai ɗanɗana mutuwa ba; ba a kuwa same shi ba, domin Allah ya ɗauke shi. Gama kafin a ɗauke shi, an yabe shi a kan ya gamshi Allah. 6In ba tare da bangaskiya ba kuwa, ba ya yiwuwa a gamshi Allah, domin duk mai zuwa wurin Allah dole yă gaskata cewa yana nan, kuma shi ne yakan sāka wa waɗanda suke nemansa da gaske.

7Ta wurin bangaskiya Nuhu, sa’ad da aka yi masa gargaɗi a kan abubuwan da ba a gani ba tukuna, a cikin tsoro mai tsarki ya sassaƙa jirgi don ceton iyalinsa. Ta wurin bangaskiyarsa ya hukunta duniya ya kuma zama magājin adalcin da ake samu ta wurin bangaskiya.

8Ta wurin bangaskiya ne Ibrahim, sa’ad da aka kira shi ya fita zuwa wata ƙasar da zai karɓi gādo daga baya, ya kuwa yi biyayya ya tafi, ko da yake bai san inda za shi ba. 9Ta wurin bangaskiya ya yi zama a ƙasar da aka yi masa alkawari kamar baƙo a baƙuwar ƙasa; ya zauna a tentuna, haka ma Ishaku da Yaƙub, waɗanda su ma magādan alkawarin nan ne tare da shi. 10Gama yana zuba ido ga birnin nan mai tushe, wanda mai zānen gininsa da kuma mai gininsa Allah ne. 11Ta wurin bangaskiya Ibrahim, ko da yake shekarunsa sun wuce, Saratu kanta kuma bakararriya ce ya iya zama mahaifi domin ya11.11 Ko kuwa Ta wurin bangaskiya Saratu ma, wadda shekarunta sun wuce, ta iya haifi ’ya’ya domin ta amince cewa shi wanda ya yi alkawarin mai aminci ne. 12Saboda haka, daga mutum ɗaya, wanda dā shi ma da matacce kusan ɗaya ne, zuriya masu yawa suka fito kamar taurari a sararin sama da kuma kamar yashin da ba a iya ƙirgawa a bakin teku.

13Duk mutanen nan suna cikin bangaskiya sa’ad da suka mutu. Ba su kuwa karɓi abubuwan da aka yi alkawari ba; sun dai hango su suka kuma marabce su daga nesa. Suka kuma amince cewa su baƙi ne, bare kuma a duniya. 14Mutane masu faɗin irin abubuwan nan sun nuna cewa suna neman ƙasar da take tasu. 15Da a ce suna tunanin ƙasar da suka bari a baya, da sun riga sun sami damar komawa. 16A maimako, suna marmarin wata ƙasa mafi kyau, ta sama. Saboda haka Allah ba ya kunya a kira shi Allahnsu, domin ya riga ya shirya musu birni.

17Ta wurin bangaskiya Ibrahim, sa’ad da Allah ya gwada shi, sai ya miƙa Ishaku hadaya. Shi da ya karɓi alkawaran ya yi shirin miƙa makaɗaicin ɗansa, 18ko da yake Allah ya ce masa, “Ta wurin Ishaku ne za a lissafta zuriyarka.”11.18 Far 21.12 19Ibrahim ya yi tunani cewa Allah yana iya tā da matattu, a misalce kuwa, ya sāke karɓan Ishaku daga matattu.

20Ta wurin bangaskiya ne Ishaku ya albarkaci Yaƙub da Isuwa game da nan gabansu.

21Ta wurin bangaskiya ne Yaƙub, sa’ad da yake bakin mutuwa, ya albarkaci kowane ɗan Yusuf, ya kuma yi sujada yayinda yake jingine a kan sandansa.

22Ta wurin bangaskiya ne Yusuf, sa’ad da kwanakinsa suka yi kusan ƙarewa, ya yi magana game da fitowar Isra’ilawa daga Masar ya kuma ba da umarni game da ƙasusuwansa.

23Ta wurin bangaskiya ne iyayen Musa suka ɓoye shi har wata uku bayan haihuwarsa, domin sun ga cewa shi ba kamar sauran yara ba ne, ba su kuwa ji tsoron umarnin sarki ba.

24Ta wurin bangaskiya ne Musa, sa’ad da ya yi girma, ya ƙi a kira shi ɗan diyar Fir’auna. 25Ya zaɓa yă sha wahala tare da mutanen Allah, maimakon yă ji daɗin sha’awace-sha’awacen zunubi na ɗan lokaci. 26Ya ɗauki wulaƙancin da yake sha saboda Kiristi ya fi dukiyar Masar daraja, domin ya sa ido ga ladansa. 27Ta wurin bangaskiya ya bar Masar, ba tare da jin tsoron fushin sarki ba; ya kuwa jure domin ya ga wannan wanda ba a iya gani. 28Ta wurin bangaskiya ya kiyaye Bikin Ƙetarewa ya kuma yayyafa jini, domin kada mai hallakar ’ya’yan fari yă taɓa ’ya’yan fari na Isra’ila.

29Ta wurin bangaskiya ne mutane suka bi ta cikin Jan Teku, sai ka ce a kan busasshiyar ƙasa; amma da Masarawa suka yi ƙoƙari su yi haka, sai aka nutsar da su.

30Ta wurin bangaskiya ne katangar Yeriko ta rushe, bayan mutane suka yi ta kewaye ta har kwana bakwai.

31Ta wurin bangaskiya ne ba a kashe Rahab karuwan nan, ta tare da marasa biyayya ba don ta marabci ’yan leƙan asiri.

32Me kuma zan faɗa? Ba ni da lokacin da zan ba da labari a kan Gideyon, Barak, Samson, Yefta, Dawuda, Sama’ila, da kuma annabawa, 33waɗanda ta wurin bangaskiya ne suka ci nasara a kan mulkoki, suka aikata adalci, suka kuma sami abin da aka yi alkawari; waɗanda suka rurrufe bakunan zakoki, 34suka kashe harshen wuta, suka kuma tsere wa kaifin takobi; waɗanda aka mai da rashin ƙarfinsu ya zama ƙarfi; waɗanda suka yi jaruntaka wajen yaƙi suka kuma fatattaki mayaƙan waɗansu ƙasashe. 35Mata suka karɓi ƙaunatattunsu da aka sāke tasar daga matattu. Aka azabtar da yawancin mutanen nan, amma suka ƙi a sake su, domin sun tabbata za su sami lada mafi kyau sa’ad da aka tā da matattu. 36Waɗansu suka sha ba’a da bulala, har da dauri da sarƙa, da kuma jefa su cikin kurkuku. 37Aka jajjefe su da duwatsu; aka raba su biyu da zarto; aka kashe su da takobi. Suka yi ta yawo saye da fatun tumaki da na awaki, suka yi zaman rashi, suka sha tsanani da kuma wulaƙanci 38duniya ba tă ma cancanci su zauna a cikinta ba. Suka yi ta yawo a cikin hamada da a kan duwatsu, da cikin kogwanni da kuma cikin ramummuka.

39Waɗannan duka an yabe su saboda bangaskiyarsu, duk da haka babu waninsu da ya sami abin da aka yi alkawari. 40Allah ya shirya mana wani abu mafi kyau. Kuma bai so su kai ga maƙasudin bangaskiyarsu ba sai tare da mu.