Djela Apostolska 27 – CRO & HCB

Knijga O Kristu

Djela Apostolska 27:1-44

Pavao plovi u Rim

1Odlučeno je da odjedrimo u Italiju. Pavla i nekolicinu drugih zatvorenika predali su stotniku carske čete Juliju. 2Ukrcali smo se na neku adramitsku lađu koja je plovila u azijska mjesta te otplovili. S nama je bio i neki Makedonac, Aristarh iz Soluna.

3Sutradan smo doplovili u Sidon. Julije je s Pavlom vrlo ljubazno postupao. Dopustio mu je posjetiti prijatelje, da se pobrinu za njegove potrebe. 4Otplovili smo dalje jedreći sjeverno uz Cipar između otoka i kopna jer su puhali suprotni vjetrovi. 5Prošli smo uz cilicijsku i pamfilijsku obalu te stigli u grad Miru u Liciji. 6Ondje stotnik pronađe neku lađu što je iz Aleksandrije plovila u Italiju, pa nas ukrca na nju.

7Nekoliko smo dana sporo plovili i jedva došli do Knida. Kako od vjetra nismo mogli pristati, otplovili smo pod Kretu, do Salmone, 8pa na jedvite jade uz nju do nekoga mjesta zvanog Dobra pristaništa, blizu grada Laseje. 9Mnogo smo vremena izgubili. Plovidba je postala vrlo opasnom jer je već bila jesen,27:9 U grčkome: jer je post (obično koncem rujna ili početkom listopada) već prošao. a Pavao upozori:

10“Ljudi, vidim da će plovidba biti pogibeljna i da ćemo pretrpjeti veliku štetu—ne samo u teretu nego i u našim životima.” 11Ali stotnik je više vjerovao kormilaru i vlasniku broda nego Pavlu. 12Kako luka nije bila prikladna za zimovanje, većina je ljudi predlagala da otplove i pokušaju doći do luke Feniks na Kreti, otvorenoj prema jugozapadu i sjeverozapadu, te da ondje prezimimo.

Oluja na moru

13Tada puhne blagi južnjak te oni, misleći da bi mogli uspjeti u toj nakani, dignu sidro i zaplove uz samu obalu Krete. 14Ali ubrzo zatim silovito zapuše žestok vjetar zvani sjeveroistočnjak. 15Zahvati lađu tako da mu se nije mogla oteti, pa smo se prepustili da nas nosi.

16Kad smo prolazili uz neki otočić zvan Kauda, jedva smo na brod podignuli čamac za spašavanje koji smo vukli za sobom. 17Podignuli su ga da uporabe opremu za spašavanje i da konopcima potpašu lađu. Bojeći se da se ne nasuču na Sirtu uz afričku obalu, spuste plivajuće sidro te smo tako plovili dalje nošeni vjetrom.

18Kako nas je oluja silovito bacala, sutradan izbace s broda teret, 19a treći dan brodsku opremu i sve čega su se domogli. 20Strašna je oluja bjesnjela mnogo dana te se nisu mogli vidjeti ni sunce ni zvijezde. Gubili smo svaku nadu da ćemo se spasiti.

21Dugo već nismo ništa jeli. Pavao stane pred posadu i reče: “Trebali ste me, ljudi, poslušati i ne odlaziti s Krete pa biste izbjegli svu ovu nevolju i štetu. 22Ali sada vam kažem: budite odvažni jer nitko od nas neće stradati iako će lađa potonuti. 23Noćas mi se ukazao anđeo Boga kojemu pripadam i služim 24te mi rekao: ‘Ne boj se, Pavle, jer ćeš sigurno stići pred cara! A Bog ti daruje i da svi tvoji suputnici sigurno doputuju.’ 25Zato se, ljudi, razvedrite! Vjerujem Bogu. Bit će kako mi je rekao. 26Ali nasukat ćemo se na neki otok.”

Brodolom

27Četrnaeste noći oluje, oko ponoći, vjetar nas je gonio amo-tamo po Jadranu. Mornari naslute da se približava nekakvo kopno. 28Bace olovnicu i izmjere dvadeset hvati dubine. Malo zatim opet ju bace i izmjere petnaest hvati. 29Prestraše se da ne nalete na grebene pa bace s krme četiri sidra i počnu se moliti da se brzo razdani. 30Mornari su kanili pobjeći s lađe pa počnu spuštati čamac u more pod izlikom da kane spustiti sidra s pramca. 31Ali Pavao reče stotniku i vojnicima: “Ne ostanu li oni na lađi, nećete se spasiti!” 32Vojnici prerežu užad i puste da čamac padne u more.

33Sve do svanuća Pavao je molio ljude da jedu. “Četrnaest dana niste ni taknuli jelo”, reče. 34“Molim vas, pojedite što za vlastito dobro. Jer neće vam pasti ni vlas s glave.” 35Kad je to rekao, uzme kruh te pred svima zahvali Bogu, razlomi ga i počne jesti. 36Svi se razvedre i uzmu hranu. 37U lađi nas je bilo dvjesto sedamdeset šest duša. 38Kad su se najeli, počnu rasterećivati lađu bacajući žito u more.

39Kad se razdanilo, mornari nisu prepoznali obalu, ali opazili su neki zaljev ravne obale te odluče pokušati onamo zavesti lađu. 40Odvežu zato sidra i puste da padnu u more. Popuste konopce na kormilima i razviju prednje jedro prema vjetru te se usmjere prema obali. 41Ali nalete na plićak i brod se nasuče. Pramac nasjedne i ostane nepomičan, a krmu su razbijali žestoki valovi.

42Vojnici nakane poubijati zatvorenike da koji ne otpliva i ne pobjegne, 43ali im stotnik, želeći poštedjeti Pavla, ne dopusti da to učine. Zapovjedi da oni koji znaju plivati prvi skoče u more i otplivaju do obale, 44a ostalima reče da doplivaju na daskama i olupinama lađe. Tako su svi živi i zdravi dospjeli na kopno.

Hausa Contemporary Bible

Ayyukan Manzanni 27:1-44

Bulus ya tafi Roma a jirgin ruwa

1Sa’ad da aka yanke shawara cewa za mu tashi a jirgin ruwa zuwa Italiya, sai aka danƙa Bulus da waɗansu ’yan kurkuku a hannun wani jarumin mai suna Juliyos, wanda yake na Bataliyar Babban Sarki. 2Muka shiga jirgin ruwa daga Andiramitiyum wanda yake shirin tashi zuwa tasoshin da suke bakin tekun lardin Asiya, sai muka kama tafiya. Aristarkus, mutumin Makidoniya daga Tessalonika, yana tare da mu.

3Kashegari muka sauka a Sidon; Juliyos kuwa, cikin alheri ga Bulus, ya bar shi yă je wajen abokansa domin su biya masa bukatunsa. 4Daga can kuma muka sāke kama tafiya muka zaga ta bayan tsibirin Saifurus saboda iska tana gāba da mu. 5Sa’ad da muka ƙetare tekun da yake sassan gaɓar Silisiya da Famfiliya sai muka sauka a Mira ta Lisiya. 6A can jarumin ya sami wani jirgin ruwan Alekzandariyan da za shi Italiya sai ya sa mu a ciki. 7Tafiyar ta ɗauki kwanaki da yawa muna yi kaɗan-kaɗan da ƙyar muka iso kusa da gaɓar Kinidus. Da iskar ta hana mu ci gaba, sai muka bi ta bayan tsibirin Kirit ɗaura da Salmone. 8Muka ci gaba a gefen gaɓar da ƙyar har muka iso wani wurin da ake kira Kyakkyawan Mafaka, kusa da garin Laseya.

9An riga an ɓata lokaci da yawa, tafiya kuwa ta riga ta zama da hatsari domin a lokacin Azumi27.9 Wato, da Ibraniyanci Ranar Kafara ke nan (Yom Kippur) ya riga ta wuce. Saboda haka Bulus ya gargaɗe su, 10ya ce, “Mutane, ina gani tafiyarmu za tă zama da masifa ta kuma kawo babbar hasara ga jirgin ruwan da kaya, da kuma ga rayukanmu ma.” 11Amma jarumin, a maimakon ya saurari abin da Bulus ya ce, sai ya bi shawarar matuƙi da kuma mai jirgin ruwan. 12Da yake tashar jirgin ruwan ba tă dace a ci damina a can ba, yawanci suka ba yanke shawara cewa mu ci gaba da tafiya, da bege za mu kai Funis mu ci damina a can. Wannan tashar jirgin ruwa ne a Kirit, tana fuskantar kudu maso yamma da kuma arewa maso yamma.

Hadari

13Da iska ta fara busowa daga kudu a hankali, sai suka yi tsammani sun sami abin da suke nema; saboda haka suka janye ƙugiyar jirgin ruwa suka bi ta gefen tsibirin Kirit. 14Ba a jima ba, sai ga wata guguwar iska mai ƙarfin da ake kira “’Yar arewa maso gabas,” ta buga daga tsibirin. 15Iskar ta ci ƙarfin jirgin ruwan har ya kāsa fuskantar iskar; saboda haka muka sallamar mata tă yi ta tura mu. 16Da muka bi ta bayan wani ɗan tsibirin da ake kira Kauda, da ƙyar muka jawo ɗan ƙaramin jirgin kusa da jirgin. 17Da mutanen suka jawo shi cikin babban jirgin ruwan, sai suka sa igiyoyi ta ƙarƙashin jirgin ruwan kanta don su ɗaɗɗaura shi. Don gudun kada a fyaɗa mu da yashin gaɓar Sirtis, sai suka saukar da ƙugiyar jirgin ruwan, suka bari aka yi ta tura jirgin haka. 18Haka muka yi ta shan bugun guguwar hadarin nan kashegari suka fara jajjefar da kayan da jirgin yake ɗauke da su a cikin teku. 19A rana ta uku, da hannuwansu suka jefar da kayan aikin jirgin ruwan a cikin teku. 20Da dai aka yi kwana da kwanaki ba a ga rana ko taurari ba guguwar iska kuma ta ci gaba da bugowa, a ƙarshe muka fid da zuciya za mu tsira.

21Bayan mutanen sun daɗe ba su ci abinci ba, Bulus ya miƙe tsaye a gabansu ya ce, “Mutane, da kun ji shawarata na kada ku tashi daga Kirit, da ba ku fāɗa wannan masifa da hasara ba. 22Amma yanzu ina ƙarfafa ku ku yi ƙarfin hali, domin ba ɗayanku da zai rasa ransa; jirgin ruwan ne kaɗai zai hallaka. 23Jiya da dare wani mala’ikan Allahn da nake nasa nake kuma bauta wa ya tsaya kusa da ni 24ya ce, ‘Kada ka ji tsoro, Bulus. Lalle za ka tsaya a gaban Kaisar a yi maka shari’a; Allah kuma cikin alherinsa ya ba ka dukan rayukan mutanen da suke tafiya tare da kai.’ 25Saboda haka ku yi ƙarfin hali, ku jama’a, gama gaskata Allah a kan cewa yadda aka faɗa mini ɗin nan, haka zai faru. 26Duk da haka, dole a fyaɗa mu a wani tsibiri.”

Jirgin ruwa ya yi hatsari

27A dare na goma sha huɗu iska dai tana ta korarmu a Tekun Adiriyatik, wajen tsakar dare sai masu tuƙin jirgin suka zaci sun yi kusa da ƙasa. 28Sai suka gwada zurfin ruwan suka ga ya kai ƙafa ɗari da ashirin. Bayan ɗan lokaci kaɗan suka sāke gwadawa suka ga zurfin ya kai ƙafa tasa’in. 29Don gudun kada a fyaɗa mu a kan duwatsu, sai suka saki ƙugiyoyin jirgin guda huɗu daga bayan jirgin suka yi fata gari ya waye. 30Cikin ƙoƙarin tserewa daga jirgin, sai masu tuƙin jirgin suka saukar da ɗan ƙaramin jirgin ruwan cikin tekun, suka yi kamar za su saki waɗansu ƙugiyoyi daga sashen gaba na babban jirgin ne. 31Sai Bulus ya ce wa jarumin da kuma sojojin, “In mutanen nan ba su tsaya a cikin jirgin nan ba, ba za ku tsira ba.” 32Sai sojojin suka yayyanke igiyoyin da suke riƙe da ɗan ƙaramin jirgin, suka bar shi ya bi ruwa.

33Kafin gari ya waye Bulus ya roƙe su duka su ci abinci. Ya ce, “Kwana goma sha huɗu ke nan, kuna zama cikin zulumi kun kuma kasance ba abinci, ba ku ci kome ba. 34Ina roƙonku yanzu ku ci abinci. Kuna bukatarsa don ku rayu. Ba ɗayanku da zai rasa ko gashin kansa guda ɗaya.” 35Bayan da ya faɗi haka, sai ya ɗauki burodi ya yi godiya ga Allah a gabansu duka. Sa’an nan ya gutsuttsura ya fara ci. 36Dukansu kuwa suka sami ƙarfafawa, suka kuma ci abinci. 37Dukanmu a jirgin kuwa mutane 276 ne. 38Sa’ad da suka ci iyakar abin da suke so, sai suka rage nauyin jirgin ta wurin zubar da hatsin a cikin tekun.

39Da gari ya waye, ba su gane ƙasar da suke ba, amma suka ga wani lungu da gaci mai yashi, sai suka yanke shawara su kai jirgin can in za su iya. 40Da suka yanke ƙugiyoyin, sai suka bar su a cikin teku a lokaci guda kuma suka ɓalle maɗaurin abin juya jirgin. Sai suka tā da filafilan gaban jirgin daidai yadda iska za tă tura shi gaba, sa’an nan suka nufi gaci. 41Amma jirgin ruwan ya shiga yashi ya kafe. Kan jirgin ya shiga cikin yashin ya kāsa motsi, sai jirgin ya fara farfashewa ta baya saboda haukan raƙuman ruwa.

42Sojojin suka yi niyya su kakkashe ’yan kurkukun don hana waninsu yă yi iyo yă tsere. 43Amma jarumin ya so yă ceci ran Bulus, sai ya hana su aiwatar da niyyarsu. Ya kuma yi umarni duk waɗanda suka iya ruwa su fara fāɗawa zuwa gaci. 44Sauran kuma su bi katakai zuwa can ko kuma a kan tarkacen jirgin ruwan. Ta haka kowa ya kai bakin teku lafiya.