Djela Apostolska 25 – CRO & HCB

Knijga O Kristu

Djela Apostolska 25:1-27

Pavao pred Festom

1Tri dana pošto je preuzeo vlast nad pokrajinom, Fest iz Cezareje ode u Jeruzalem. 2Ondje mu veliki svećenici i drugi židovski uglednici iznesu tužbu protiv Pavla. Preklinjali su ga da se smiluje 3i pošalje Pavla u Jeruzalem jer su spremali zasjedu da ga putem smaknu. 4Ali Fest odgovori da je Pavao u zatvoru u Cezareji te da će i on uskoro onamo. 5“Ovlastite nekolicinu da pođu sa mnom”, reče stoga. “Ako je taj čovjek što skrivio, neka ga optuže.”

6Osam ili deset dana potom vrati se u Cezareju. Sutradan sjedne na sudački stolac i zapovjedi da dovedu Pavla. 7Kad uđe Pavao, židovski vođe iz Jeruzalema okruže ga i iznesu protiv njega mnoge teške optužbe koje nisu mogli dokazati. 8Pavao se branio: “Nisam zgriješio ni protiv židovskoga Zakona, ni protiv Hrama, ni protiv cara.”

9A Festus ga, želeći ugoditi Židovima, upita: “Jesi li voljan poći u Jeruzalem da ti se ondje za to sudi u mojoj nazočnosti?”

10Pavao odgovori: “Ne. Stojim pred carevim sudom, gdje mi se i treba suditi. Dobro znaš da tim Židovima nisam ništa skrivio. 11Ako sam pak zaista skrivio što zaslužuje smrt, ne bježim od toga. Ali ako me ovi ovdje neopravdano tuže, nitko me ne može njima izručiti. Prizivam se na cara!”

12Fest se na to posavjetuje s Vijećem pa odgovori: “Na cara si se prizvao, pred cara ćeš ići!”

13Nakon nekoliko dana dođu kralj Agripa i njegova sestra Berenika u Cezareju pozdraviti Festa. 14Kako su se ondje zadržali nekoliko dana, Fest ispriča kralju o Pavlu. “Tu je neki čovjek što ga je Feliks ostavio u zatvoru”, reče. 15“Dok sam bio u Jeruzalemu, veliki svećenici i starješine optužili su ga i zatražili da ga osudim. 16Odgovorio sam im da Rimljani ne običavaju kazniti čovjeka a da mu ne sude. Prije toga valja optuženika suočiti s tužiteljima i dati mu prigodu da se brani od optužbe.

17Kad su dakle skupa sa mnom doputovali ovamo, odmah sam sutradan, bez odgađanja, sjeo na sudački stolac i zapovjedio da dovedu tog čovjeka. 18Ali tužitelji koji su stajali oko njega nisu ga optužili ni za što od onoga što sam ja pretpostavljao. 19Riječ je bila o nečemu prijepornom glede njihove vjere, o nekakvome Isusu koji je umro, a Pavao tvrdi da je živ. 20Ne snalazeći se u takvoj raspravi, upitao sam ga bi li htio poći u Jeruzalem da mu ondje za to sude. 21Ali prizivom je zatražio da se podloži presudi njegova Veličanstva. Zato sam zapovjedio da ga čuvaju u zatvoru dok ga ne pošaljem caru.”

22“Htio bih i ja čuti tog čovjeka”, reče Agripa.

“Čut ćeš ga sutra”, odgovori Fest.

Pavao pred Agripom

23Sutradan tako Agripa i Berenika uđu u dvoranu s velikim sjajem, praćeni vojnim zapovjednicima i najvećim gradskim uglednicima. Na Festovu zapovijed dovedu Pavla. 24Fest tada reče: “Kralju Agripa i svi nazočni, evo čovjeka zbog kojega me svi ovdašnji i jeruzalemski Židovi salijeću vičući da ga smaknem. 25Ali nisam utvrdio da je učinio išta zbog čega bi zaslužio smrt. Kako se on sam prizvao na cara, odlučio sam ga caru i poslati. 26Ali nemam o njemu što pouzdano napisati caru. Zato sam ga izveo pred vas, posebice pred tebe, kralju Agripa, da bih nakon ove istrage znao što napisati. 27Jer doista je besmisleno poslati zatvorenika caru a ne navesti za što se optužuje!”

Hausa Contemporary Bible

Ayyukan Manzanni 25:1-27

Shari’a a gaban Festus

1Kwana uku bayan isowa a lardin, sai Festus ya haura daga Kaisariya zuwa Urushalima, 2inda manyan firistoci da shugabannin Yahudawa suka bayyana a gabansa suka kuma gabatar da ƙararsu a kan Bulus. 3Suka roƙi Festus a gaggauce a matsayin alfarma gare su, da yă sa a mai da Bulus Urushalima, gama sun ’yan kwanto su kashe shi a hanya. 4Festus ya amsa ya ce, “Bulus yana tsare a Kaisariya, ni da kaina kuma zan je can ba da daɗewa ba. 5Ku sa waɗansu daga cikin shugabanninku su tafi tare da ni su kawo ƙararsu a kan mutumin a can, in ya aikata wani laifi.”

6Bayan ya yi kwanaki takwas ko goma tare da su, sai ya gangara zuwa Kaisariya, kashegari kuma ya kira a yi zaman kotu ya kuma umarta a kawo Bulus a gabansa. 7Da Bulus ya bayyana, sai Yahudawan da suka gangaro daga Urushalima suka tsaya kewaye shi, suna kawo ƙarar masu tsanani da yawa a kansa, waɗanda ba su iya tabbatarwa ba.

8Sa’an nan Bulus ya kāre kansa ya ce, “Ban aikata wani laifi game da dokokin Yahudawa ko game da haikali ko kuma game da Kaisar ba.”

9Festus, da yake yana so yă yi wa Yahudawa alfarma, sai ya ce wa Bulus, “Ka yarda ka je Urushalima a yi maka shari’a a can a gabana a kan waɗannan zarge?”

10Bulus ya amsa ya ce, “Yanzu ina tsaye a gaban kotun Kaisar, inda ya kamata a yi mini shari’a. Ban yi wani laifi ga Yahudawa ba, kai da kanka ma ka san da haka sarai. 11In kuwa ina da wani laifin da ya isa kisa, ban ƙi in mutu ba. Amma in ƙarar da waɗannan Yahudawa suka kawo a kaina ba gaskiya ba ne, ba wanda yake da iko ya ba da ni a gare su. Na ɗaukaka ƙara zuwa gaban Kaisar!”

12Bayan Festus ya yi shawara da majalisarsa sai ya ce, “Ka ɗaukaka ƙara zuwa gaban Kaisar. To, ga Kaisar kuwa za ka tafi!”

Festus ya nemi shawarar Sarki Agiriffa

13Bayan ’yan kwanaki sai Sarki Agiriffa da Bernis suka iso Kaisariya don su yi wa Festus gaisuwar bangirma. 14Da yake za su yi kwanaki da dama a can, sai Festus ya tattauna batun Bulus da sarki. Ya ce, “Akwai mutumin da Felis ya bari a daure. 15Sa’ad da na je Urushalima, manyan firistoci da dattawan Yahudawa suka kawo ƙara game da shi suka kuma nema a hukunta shi.

16“Na gaya musu cewa ba al’adar Romawa ba ce a hukunta mutum kafin ya fuskanci masu ƙararsa ya kuma sami damar kāre kansa game da ƙararsu. 17Da suka zo nan tare da ni, ban yi wani jinkiri ba, na kira zaman kotu kashegari kuma na umarta a kawo mutumin. 18Sa’ad da masu zarginsa suka tashi tsaye don su yi magana, ba su zarge shi da wani laifin da na yi tsammani ba. 19A maimako haka, sai suka kawo waɗansu ’yan maganganu game da addininsu da ba su yarda da shi ba da kuma game da wani Yesu da ya mutu wanda Bulus ya ce yana da rai. 20Na rasa yadda zan bincike irin abubuwan nan; saboda haka na yi tambaya ko zai yarda ya tafi Urushalima a yi masa shari’a a can game da waɗannan zargi. 21Da Bulus ya ɗaukaka ƙara zuwa gaban Babban Sarki sai na umarta a tsare shi har kafin in aika shi zuwa ga Kaisar.”

22Sai Agiriffa ya ce wa Festus, “Ni ma zan so in saurari mutumin da kaina.”

Sai ya amsa ya ce, “Za ka kuwa ji shi gobe.”

Bulus a gaban Agiriffa

23Kashegari Agiriffa da Bernis suka yi shiga irin ta sarauta suka shiga ɗakin jama’a tare da manyan sojoji da manyan mutanen birni. Da umarnin Festus, sai aka shigo da Bulus. 24Sai Festus ya ce, “Sarki Agiriffa, da kuma dukan waɗanda suke tare da mu, kun ga wannan mutum! Dukan jama’ar Yahudawa sun kawo mini kararsa a Urushalima da kuma a nan Kaisariya, suna kururuwa suna cewa bai kamata a bar shi da rai ba. 25Ban same shi da wani laifin da ya isa kisa ba, amma saboda ya ɗaukaka ƙararsa zuwa gaban Babban Sarki sai na yanke shawara in aika da shi Roma. 26Ba ni da wata tabbatacciyar maganar da zan rubuta wa Mai Girma game da shi. Saboda haka na kawo shi a gabanku duka, musamman a gabanka, Sarki Agiriffa, saboda a sakamakon wannan bincike zan iya samun abin da zan rubuta. 27Don a ganina wauta ce a aika da ɗan kurkuku ba tare da an nuna zargin da ake yi a kansa ba.”