2 Korinćanima 1 – CRO & HCB

Knijga O Kristu

2 Korinćanima 1:1-24

Pozdravi

1Pišu vam Pavao, apostol Krista Isusa Božjom voljom, i brat Timotej. Pišemo Božjoj crkvi u Korintu i svima svetima u cijeloj Ahaji. 2Neka vam je milost i mir od našega Boga Oca i Gospodina Isusa Krista.

Bog pruža utjehu svima

3Slava Bogu, Ocu našega Gospodina Isusa Krista. On je izvor svakog milosrđa i Bog koji nas tješi. 4On nas tješi u svim nevoljama, da bismo i mi mogli druge tješiti u nevoljama istom utjehom kojom Bog tješi nas. 5Koliko se obilno patnje za Krista izlijevaju na nas, toliko je preobilna i naša utjeha u Kristu. 6Podnosimo li nevolje, to je zaradi vaše utjehe i spasenja. Primamo li utjehu, to je zato da bismo vas mogli hrabriti kako biste strpljivo mogli podnositi iste patnje koje i mi podnosimo. 7Čvrsto vjerujemo da ćete, kao što s nama dijelite patnje, također dijeliti s nama i Božju utjehu.

8Željeli bismo da znate, braćo, kakve su nas nevolje zapale u Aziji. Opteretile su nas preko svake mjere, toliko preko naše snage da smo već bili izgubili nadu da ćemo preživjeti. 9Smatrali smo se već osuđenima na smrt, ali sve se to zbilo zato da se ne bismo uzdali u sebe, već u Boga koji uskrisuje mrtve. 10Od tolike nas je smrtne pogibli izbavio onaj u kojega se uzdamo da će nas i dalje izbavljati! 11I vi pomažete moleći za nas, da bi mnogi mogli zahvaljivati za uslišane molitve mnogih.

Pavlova promjena plana

12Možemo s pouzdanjem i s čistom savješću reći da smo prema svima, a posebice prema vama, postupali sveto i iskreno u svemu što smo činili, ne oslanjajući se na tjelesnu mudrost, već na Božju milost. 13-14Nismo vam pisali ništa što ne biste mogli pročitati ili razumjeti. Nadam se da ćete nas, kao što ste nas djelomice već razumjeli, jednoga dana potpuno razumjeti. Tako ćemo i mi vama, kao i vi nama, biti na ponos u dan našega Gospodina Isusa.

15U tome sam pouzdanju kanio doći tako da primite dvostruki blagoslov: 16svratiti najprije k vama na putu u Makedoniju, a zatim i vraćajući se iz Makedonije, kako biste me mogli otpraviti na put u Judeju.

17Jesam li, dakle, o tome lakomisleno odlučio, ili sam poput ljudi iz svijeta koji kažu “da”, a zapravo misle “ne”? 18Bog mi je svjedok da nisam takav. Moje “da” znači “da” 19jer u Isusa Krista, Božjega Sina o kojemu smo vam Timotej, Silvan i ja propovijedali, nema dvojbe između “da” i “ne”; naprotiv, on je Božje “da”, Božja potvrda. 20U njemu su tako ostvarena sva Božja obećanja; zato možemo reći “Amen” kad proslavljamo Boga kroz Krista. 21Bog je taj koji i vas i nas čini snažnima u Kristu i koji nas je pomazao. 22Obilježio nas je pečatom da smo njegovo vlasništvo i u srca nam stavio zalog: Svetoga Duha.

23Prizivam Boga za svjedoka da vam govorim istinu: nisam ponovno došao u Korint samo zato što vas nisam htio ražalostiti oštrim prijekorom. 24Jer, ne bismo vam htjeli naređivati što i kako da vjerujete, već surađivati s vama da biste bili radosni, jer vi u vjeri čvrsto stojite.

Hausa Contemporary Bible

2 Korintiyawa 1:1-24

1Bulus, manzon Kiristi Yesu ta wurin nufin Allah, da kuma daga Timoti ɗan’uwanmu,

Zuwa ga ikkilisiyar Allah da take a Korint, tare da dukan tsarkaka a ko’ina a Akayya.

2Alheri da salama daga Allah Ubanmu da kuma Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.

Allah na dukan ta’aziyya

3Yabo ya tabbata ga Allah, da Uban Ubangijinmu Yesu Kiristi, Uba mai tausayi, da kuma Allah na dukan ta’aziyya, 4wanda yakan yi mana ta’aziyya a cikin dukan wahalolinmu, domin mu kuma mu iya ta’azantar da waɗanda suke cikin kowace irin wahala, da ta’aziyyar da mu kanmu muka samu daga Allah. 5Gama kamar yadda wahalar Kiristi ta cika har tana zuba a cikin rayuwarmu, haka nan kuma ta wurin Kiristi ta’aziyyarmu ta cika har tana zuba. 6In muna shan wahala, ai, muna shanta domin ta’aziyyarku, da cetonku ne, in mun sami ta’aziyya, ai, mun same ta domin ta’aziyyarku ce, wadda take sa ku jure wa irin wahalan nan, da muke sha. 7Begen da muke da shi dominku kuwa, tabbatacce ne, domin mun san cewa kamar yadda kuke tarayya da mu a cikin wahalolinmu, haka kuma kuke tarayya da mu a cikin ta’aziyyarmu.

8’Yan’uwa, ba ma so ku zama da rashin sani, a kan wahalolin da muka sha a lardin Asiya. Mun sha wahaloli sosai, har abin ya fi ƙarfinmu, ya sa muka fid da tsammanin rayuwa. 9Ba shakka, a zuciyarmu mun ji kamar hukuncin kisa ne aka yi mana. Wannan kuwa ya faru ne domin kada mu dogara da kanmu, sai dai ga Allah, wanda yake tā da matattu. 10Shi ya cece mu daga irin wannan hatsari na mutuwa, zai kuwa cece mu. A kansa muka kafa bege cewa zai ci gaba da cetonmu, 11yayinda kuke taimakonmu ta wurin addu’o’inku. Mutane da yawa kuwa za su yi godiya ta dalilinmu, saboda albarkar da aka yi mana, ta amsa addu’o’i masu yawa.

Canja shirye-shiryen Bulus

12Wannan shi ne taƙamarmu. Lamirinmu yana ba da shaida cewa mun yi zamanmu a duniya, musamman a dangantakarmu da ku cikin tsarki, tsakani da Allah. Mun yi haka ta wurin bishewar alherin Allah, ba bisa ga hikimar duniya ba. 13Gama ba mu rubuta muku abin da ba za ku iya karatu ko ku kāsa fahimta ba. Ina kuma fata cewa, 14kamar yadda kuka ɗan fahimce mu, za ku kai ga cikakkiyar fahimta cewa za ku iya yin taƙama da mu, kamar yadda mu ma za mu yi taƙama da ku a ranar da Ubangiji Yesu zai dawo.

15Saboda na amince da haka, shi ya sa na so zuwa wurinku da fari, domin ku sami albarka riɓi biyu. 16Na yi shiri in ziyarce ku a kan hanyata zuwa Makidoniya, in kuma sāke dawo wurinku a kan hanyata daga Makidoniya, sa’an nan ku yi mini rakiya a hanyata zuwa Yahudiya. 17Kuna gani na yi wannan shirin ba da sanin abin da nake yi ba ne? Ko kuwa, kuna gani na yi shirin nan da halin mutuntaka ne, don in ce, “I” in koma in ce, “A’a”?

18Kamar dai yadda ba shakka Allah yake mai aminci, haka ma maganar da muka yi muku, ba “I” da kuma “A’a” ba ce. 19Gama Ɗan Allah, Yesu Kiristi, wanda ni da Sila da Timoti muka yi muku wa’azinsa, ai, ba “I” da “A’a” ba ne, amma a cikin Kiristi, “I” ne kullum. 20Domin dukan alkawaran Allah cikarsu a gare shi suke, ta wurinsa ne kuma muke faɗar “Amin”, domin a ɗaukaka Allah. 21Allah ne fa yake sa mu da ku mu tsaya daram cikin Kiristi. Shi ne ya shafe mu, 22ya buga mana hatiminsa a kan mu nasa ne, ya kuma sa mana Ruhunsa a cikin zukatanmu, domin yă tabbatar da abin da yake zuwa nan gaba.

23Labudda, Allah shi ne shaidata cewa don kada in ƙara muku wahala ne ya sa ban koma Korint ba. 24Ba nuna muku iko a kan bangaskiyarku muke yi ba, sai dai muna aiki tare da ku ne saboda farin cikinku, domin bisa ga bangaskiya ce kuke tsaye da ƙarfi.