路加福音 12 – CCBT & HCB

Chinese Contemporary Bible (Traditional)

路加福音 12:1-59

警戒門徒

1這時,成千上萬的人聚集在一起,甚至互相踐踏。耶穌先對門徒說:「你們要提防法利賽人的酵,就是他們的偽善。 2掩蓋的事終會暴露出來,隱藏的秘密終會被人知道。 3你們在暗處說的,將在明處被人聽見;你們在密室裡的私語,將在屋頂上被人宣揚。

4「朋友們,我告訴你們,不要懼怕那些殺害人的身體後再也無計可施的人。 5我告訴你們應該懼怕誰,要懼怕上帝——祂有權終結人的生命,並把人丟在地獄裡。是的,我告訴你們,要懼怕祂!

6「五隻麻雀不是只賣兩個銅錢嗎?但上帝連一隻麻雀也不會遺忘。 7其實就連你們的頭髮都被數過了。不要害怕,你們比許多麻雀要貴重!

8「我告訴你們,凡在人面前承認我的,人子在上帝的天使面前也必承認他。 9凡在人面前否認我的,人子在上帝的天使面前也要否認他。 10說話得罪人子的,還可以得到赦免,但褻瀆聖靈的,必得不到赦免! 11當人押你們到會堂,或到官員和當權者面前時,不要顧慮如何辯解,或說什麼話, 12因為到時候聖靈必指示你們當說的話。」

無知富翁的比喻

13這時,人群中有人對耶穌說:「老師,請你勸勸我的兄長跟我分家產吧。」

14耶穌答道:「朋友,誰派我作你們的審判官或仲裁,為你們分家產呢?」 15接著,祂對眾人說:「你們要小心防範一切的貪心,因為人的生命並不在於家道富足。」

16耶穌又講了一個比喻,說:「有一個富翁,他的田裡大豐收, 17於是心裡盤算,『我儲藏農產的地方不夠了,怎麼辦呢?』 18於是他說,『不如把原有的倉庫拆掉,建幾座更大的,好儲藏我所有的糧食和財物! 19那時,我就可以對自己說,「你積存這麼多財產,一生享用不盡,現在大可高枕無憂、盡情地吃喝玩樂吧!」』 20但上帝對他說,『無知的人啊!今晚就要取走你的命!你所預備的一切留給誰享用呢?』」

21耶穌說:「這就是那些只顧為自己積財、在上帝面前卻不富足之人的寫照。」

不要為衣食憂慮

22耶穌繼續對門徒說:「所以,我告訴你們,不要為生活憂慮,如吃什麼,也不要為身體憂慮,如穿什麼。 23因為生命比飲食重要,身體比穿著重要。 24你們看,烏鴉不種也不收,沒倉也沒庫,上帝尚且養活牠們,你們比飛鳥不知要貴重多少!

25「你們誰能用憂慮使自己多活片刻呢? 26既然你們連這樣的小事都無能為力,又何必為其餘的事憂慮呢? 27看看百合花如何生長吧,它們既不勞苦,也不紡織,但我告訴你們,就連所羅門王最顯赫時的穿戴還不如一朵百合花!

28「野地的草今天還在,明天就要被丟在爐中,上帝還這樣裝扮它們,何況你們呢?你們的信心太小了! 29你們不要為吃什麼喝什麼憂慮, 30因為這些都是外族人的追求,你們的天父知道你們需要這些。 31你們要尋求祂的國,祂必供給你們的需要。

32「你們這一小群人啊,不要怕!因為你們的天父樂意把祂的國賜給你們。 33要變賣你們的家產去賙濟窮人,要為自己預備永不破損的錢袋,在天上積攢取之不盡的財寶,那裡沒有賊偷,也沒有蟲蛀。 34因為你們的財寶在哪裡,你們的心也在哪裡。

警醒預備

35「你們要束上腰帶,準備服侍,要點亮燈, 36像奴僕們等候主人從婚宴回來。主人回來一叩門,奴僕就可以立即給他開門。 37主人回來,看見奴僕警醒等候,奴僕就有福了!我實在告訴你們,主人必束上腰帶請他們坐席,並親自服侍他們。 38無論主人在深夜或黎明回家,若發現奴僕警醒等候,奴僕就有福了。

39「你們都知道,一家的主人若預先知道賊什麼時候來,一定不會讓賊入屋偷竊。 40同樣,你們也要做好準備,因為在你們意想不到的時候,人子就來了。」

忠僕和惡僕

41彼得問:「主啊!你這比喻是講給我們聽的,還是講給眾人聽的呢?」

42主說:「誰是那個受主人委託管理家中大小僕役、按時分糧食給他們、又忠心又精明的管家呢? 43主人回家時,看見他盡忠職守,他就有福了。 44我實在告訴你們,主人一定會把所有產業都交給他管理。 45但如果他以為主人不會那麼快回來,就毆打僕婢、吃喝醉酒, 46主人會在他想不到的日子、不知道的時辰回來,嚴厲地懲罰12·46 嚴厲地懲罰」或作「腰斬」。他,使他和不忠不信的人同受嚴刑。 47明知主人的意思卻不準備,也不遵行主人吩咐的僕人,必受更重的責打。 48但因不知道而做了該受懲罰之事的僕人,必少受責打。多給誰,就向誰多取;多託付誰,就向誰多要。

家庭分裂

49「我來是要把火丟在地上,我多麼希望這火已經燃燒起來。 50我有要受的『洗禮』,我何等迫切地想完成這『洗禮』啊! 51你們以為我來是要使天下太平嗎?不,我告訴你們,我來是要使地上起紛爭。 52從今以後,一家五口會彼此相爭,三個人反對兩個人,或是兩個人反對三個人, 53父子相爭,母女對立,婆媳反目。」

明辨是非

54然後,祂又對眾人說:「你們看見雲從西方升起,就說,『快下雨了!』果然如此。 55南風一起,你們就說,『天必燥熱』,你們也說對了。 56你們這些偽善的人!既然知道觀察天色、預測天氣,為什麼不知道觀察這個世代呢? 57你們為什麼不自己明辨是非呢? 58如果你和控告你的人要去對簿公堂,要盡量在路上跟對方和解,以免被拉到審判官面前,審判官派差役把你關進監牢。 59我告訴你,除非你付清所欠的每一分錢,否則休想出監牢。」

Hausa Contemporary Bible

Luka 12:1-59

Faɗakarwa da ƙarfafawa

1Ana nan sa’ad da taron dubban mutane suka taru har suna tattaka juna, Yesu fara yin magana, da farko da almajiransa ya ce, “Ku yi hankali da yistin Farisiyawa, wato, munafunci. 2Ba abin da yake rufe da ba za a fallasa ba, ko kuma abin da yake ɓoye da ba za a bayyana ba. 3Abin da kuka faɗa a cikin duhu, za a ji shi a hasken rana. Kuma abin da kuka faɗa a kunne, a cikin ɗakunan ciki-ciki, za a yi shelarsa daga kan rufin ɗakuna.

(Mattiyu 10.28-31)

4“Ina dai gaya muku abokaina, kada ku ji tsoron masu kashe jiki, amma bayan haka, ba sauran abin da za su iya yi. 5Amma zan nuna muku wanda za ku ji tsoronsa. Ku ji tsoron wanda, bayan da ya kashe jikin, yana da iko ya jefa ku cikin jahannama ta wuta. I, ina gaya muku, ku ji tsoronsa. 6Ba ana sayar da kanari biyar a kan kobo biyu ba? Duk da haka, Allah bai manta da ko ɗayansu ba. 7Tabbatacce, gashin kanku ɗin nan ma, an ƙidaya su duka. Kada ku ji tsoro. Darajarku ta fi na kanari masu yawa girma.

(Mattiyu 10.32,33; 12.32; 10.19,20)

8“Ina gaya muku, duk wanda ya shaida ni a gaban mutane, Ɗan Mutum ma zai shaida shi a gaban mala’ikun Allah. 9Amma wanda ya yi mūsun sanina a gaban mutane, shi ma za a yi mūsunsa a gaban mala’ikun Allah. 10Kuma duk wanda ya faɗi kalmar zagi a kan Ɗan Mutum, za a gafarta masa, amma duk wanda ya saɓa wa Ruhu Mai Tsarki, ba za a gafarta masa ba.

11“Sa’ad da an kai ku a gaban majami’u, da gaban masu mulki, da kuma gaban masu iko, kada ku damu da yadda za ku kāre kanku, ko kuma abin da za ku faɗa, 12gama Ruhu Mai Tsarki zai koya muku abin da ya dace ku faɗa a lokacin.”

Misalin wawa mai arziki

13Sai wani mutum daga cikin taron ya ce masa, “Malam, ka ce wa ɗan’uwana ya raba gādon da ni.”

14Yesu ya amsa masa ya ce, “Kai, wa ya naɗa ni alƙali, ko mai sulhu a tsakaninku?” 15Sai ya ce musu, “Ku lura fa! Ku tsare kanku daga dukan kowane irin kwaɗayi. Ran mutum ba ya danganta a kan yawan dukiyarsa ba.”

16Sai ya gaya musu wannan misali ya ce, “Gonar wani mai arziki ta ba da amfani sosai. 17Ya yi tunani a ransa ya ce, ‘Ba ni da inda zan ajiye amfanin gonana. Me zan yi ke nan?’

18“Sai ya ce, ‘Ga abin da zan yi. Zan rushe rumbunana, in gina manya, in zuba dukan hatsina da kayana a ciki. 19Ni kuma zan ce wa raina, “Kana da kaya da yawa masu kyau, da aka yi ajiyarsu domin shekaru da dama masu zuwa. Yi hutunka, ka ci, ka sha, ka yi annashuwa.” ’

20“Amma Allah ya ce masa, ‘Kai wawa! A wannan dare za a nemi ranka. Bayan haka, wa zai gāji abin da ka tara wa kanka?’

21“Haka zai zama ga duk wanda ya tara wa kansa dukiya, amma ba shi da arziki a gaban Allah.”

Kada ku damu

(Mattiyu 6.25-34)

22Sai Yesu ya ce wa almajiransa, “Saboda haka, ina faɗa muku, kada ku damu game da rayuwarku, abin da za ku ci, ko kuma game da jikinku, abin da za ku yafa. 23Rai ya fi abinci, jiki kuma ya fi tufafi. 24Ku dubi hankaki. Ba sa shuki ko girbi, kuma ba su da ɗakin ajiya ko rumbu ba, duk da haka, duk da haka, Allah na ciyar da su. Darajarku ta fi na tsuntsaye sau da yawa! 25Wane ne a cikinku ta wurin damuwarsa, zai iya ƙara ko sa’a ɗaya ga rayuwarsa? 26Tun da ba za ku iya yin wannan ƙanƙanin abu ba, me ya sa kuke damuwa a kan sauran?

27“Ku dubi yadda furanni suke girma. Ba sukan yi aiki, ko saƙa ba, duk da haka, ina faɗa muku cewa, ko Solomon cikin kyakkyawan darajarsa duka, bai yafa kayan ado da ya kai kamar na ko ɗaya a cikinsu ba. 28In haka ne Allah yake yi wa ciyayin jeji sutura, wadda yau suna nan, sa’an nan gobe kuma a jefa cikin wuta, Allah ba zai yi muku sutura fiye da ciyayin jeji ba, ya ku masu ƙarancin bangaskiya! 29Kada ku sa zuciyarku a kan abin da za ku ci, ko abin da za ku sha, kada ku damu a kan su. 30Gama duniya da ba tă san Allah ba, tana faman neman dukan waɗannan abubuwa, Ubanku na sama kuwa, ya san kuna bukatarsu. 31Amma ku nemi mulkinsa, za a kuwa ƙara muku waɗannan abubuwa.

32“Ya ƙaramin garke, kada ku ji tsoro, gama ya gamshi Ubanku ya ba ku mulkin. 33Ku sayar da dukiyarku, ku ba wa matalauta. Ku yi wa kanku jakar kuɗin da ba za su lalace ba. Ku yi wa kanku ajiyar dukiyar da ba za tă kare ba a sama, inda ɓarawo ba zai yi kusa ba, asu kuma ba za su iya su lalatar ba. 34Gama inda dukiyarku take, nan ne zuciyarku ma take.

Zama a faɗake

(Mattiyu 24.45-51)

35“Ku shirya ɗamara don hidima. Ku bar fitilunku suna ci, 36kamar maza da suke jiran maigidansu ya dawo daga bikin aure. Saboda duk lokacin da ya dawo ya ƙwanƙwasa ƙofa, a shirye suke su buɗe masa nan da nan. 37Zai zama da albarka in maigida ya dawo, ya tarar da bayinsa suna zaman tsaro. Gaskiya ni faɗa muku, zai sa kayan hidima da kansa, ya sa bayinsa su zauna kan tebur, sa’an nan ya yi musu hidimar abinci. 38Zai zama da albarka ga bayin da maigidansu ya iske su, suna zaman tsaro, a duk lokacin da ya dawo, ko da ya dawo a sa’a ta biyu, ko ta uku na tsakar dare ne. 39Amma ku fahimci wannan. Da maigida ya san sa’ar da ɓarawo zai zo, ai, da ba zai bari a shiga, a fasa masa gida ba. 40Ku ma, sai ku zauna da shiri, domin Ɗan Mutum zai zo a sa’ar da ba ku yi tsammani ba.”

41Bitrus ya yi tambaya ya ce, “Ya Ubangiji, mu ne kake faɗa wa wannan misali, ko kuwa ga kowa da kowa ne?”

42Ubangiji ya amsa ya ce, “To, wane ne manaja mai aminci da hikima, wanda maigida ya ba shi riƙon bayinsa, domin ya ba su abincinsu a daidai lokaci? 43Zai zama da albarka ga bawan nan wanda maigidan ya dawo, ya same shi yana yin haka. 44Gaskiya nake gaya muku, maigidan zai ba shi riƙon dukan dukiyarsa. 45Amma da a ce bawan ya yi tunani a zuciyarsa ya ce, ‘Ai, maigidana ya yi jinkirin dawowa,’ sa’an nan ya fara dūkan bayin, maza da mata, ya kuma shiga ci, da sha, har da buguwa. 46Maigidan bawan nan zai dawo a ranar da wannan bawan bai yi tsammaninsa ba, kuma a sa’ar da bai sani ba. Maigidan zai yayyanka shi, ya kuma ba shi rabonsa tare da marasa bangaskiya.

47“Bawan da ya san nufin maigidansa, kuma bai yi shiri ba, ko kuma bai yi abin da maigidansa yake so ba, zai sha mummunan duka. 48Amma wanda bai sani ba, ya kuwa yi abin da ya isa horo, za a dūke shi kaɗan. Duk wanda aka ba shi mai yawa, mai yawan ne za a bida daga gare shi. Duk wanda kuma aka ba shi riƙon amana mai yawa, fiye da haka kuma za a bida daga gare shi.

Ba salama ba sai dai rabuwa

(Mattiyu 24.45-51)

49“Na zo ne domin in kawo wuta a duniya. Ina so da ta riga ta ƙunu! 50Amma ina da baftismar da za a yi mini, na kuwa damu sosai, sai na kammala ta! 51Kuna tsammani na zo domin in kawo salama a duniya ne? A’a! Ina gaya muku, rabuwa ne. 52Daga yanzu, za a iske mutum biyar a gida ɗaya sun rabu, suna gāba da juna, uku suna gāba da biyu, biyun suna gāba da ukun. 53Za su rarrabu. Mahaifi yana gāba da ɗan, ɗan kuma yana gāba da mahaifin. Mahaifiya tana gāba da diyar, diyar kuma tana gāba da mahaifiyar. Suruka tana gāba da matar ɗa, matar ɗa kuma tana gāba da suruka.”

Fahimtar lokuta

(Mattiyu 16.2,3; 5.25,26)

54Ya ce wa taron, “Sa’ad da kuka ga hadari ya fito daga yamma, nan da nan kukan ce, ‘Za a yi ruwan sama,’ sai a kuwa yi. 55Sa’ad da kuma iska ta taso daga kudu, kukan ce, ‘Za a yi zafi,’ sai kuwa a yi. 56Munafukai! Kuna san yadda za ku fassara yanayin ƙasa da na sararin sama. Ta yaya ba ku san yadda za ku yi fassarar wannan zamani ba?

57“Don me ba ku iya auna wa kanku, abin da yake daidai ba? 58Yayinda kake kan hanyar zuwa kotu da maƙiyinka, ka yi matuƙar ƙoƙari ku shirya tun kuna kan hanya. In ba haka ba, zai kai ka gaban alƙali, alƙali kuma ya miƙa ka ga ɗan sanda, ɗan sanda kuma ya jefa ka a kurkuku. 59Ina gaya maka, ba za ka fita ba, sai ka biya kobo na ƙarshe.”